HausaTv:
2025-08-11@23:48:55 GMT

Fafaroma Leon na 14 : Ina matukar bakin cikin abinda  ke faruwa a Gaza

Published: 11th, May 2025 GMT

Sabon shugaban darikar ‘yan katolika na duniya Fafaroma Leo na 14 ya ce yana matukar bakin ciki da abin da ke faruwa a zirin Gaza, inda ya bukaci a tsagaita wuta nan da nan, a ba da agajin jin kai ga fararen hula da suka gaji, kuma a sako duk wadanda aka yi garkuwa da su.”

Fafaroman ya kuma yi kira ga “manyan kasashen duniya” da su dakatar da yaki, ya kuma yi kira da a samar da zaman lafiya “adalci” mai “dorewa” a Ukraine a wani jawabi da ya gabatar yau Lahadi a sallarsa ta farko bayan zama fafaroma.

Shugaban ‘yan katolika na duniya ya kuma yi maraba da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma tsakanin Indiya da Pakistan, amma ya yi kira da a samar da maslaha mai dorewa tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon shugaban jam’iyyar PDP kuma tsohon ministan noma daga 2015 zuwa 2019, Audu Ogbeh, ya rasu a ranar Asabar, 9 ga Agusta, yana da shekaru 78 a duniya, kamar yadda iyalinsa suka tabbatar.

A cikin wata sanarwa, iyalan sun ce: “Ya rasu cikin kwanciyar hankali, ya bar mana gado na gaskiya, hidima da jajircewa ga kasa da al’umma. Mun sami kwanciyar hankali daga yadda ya shafi rayuka da kuma yadda ya kafa misali.”

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

Iyalan sun bayyana cewa za a sanar da yadda za a gudanar da jana’izarsa a nan gaba, tare da godewa abokai, da abokan aiki. Sun kuma roƙi a basu dama domin yin jimamin rasuwar baban nasu.

Rahoton LEADERSHIP ya nuna cewa Ogbeh, wanda ya shahara a siyasa, rubuce-rubuce da aikin gona, ya shugabanci PDP daga 2001 zuwa 2005 kafin ya zama minista a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
  • Ana Zanga-Zanga A Isra’ila Kan Shirin Netanyahu Na Mamaye Gaza
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza