A wani bangare na manufofinsu na kara yawan masu kada kuri’a, Alhaji Gamawa ya bayyana cewa, kungiyar mai zaman kanta za ta taimaka wa ‘yan kasa wajen karbar katin zabe, “Lokacin da INEC ta bude dandalin rajistar katin zabe, za mu taimaka musu wajen karbar katin zabe domin su bada gudunmawa a zabe da kuma amfani da ’yancinsu.

Gamawa ya kuma yi magana kan muhimmancin samun katin shaidar zama dan kasa, inda ya ce, yayin da tsaro ya yi karanci, abu ne mai sauki a laka wa dan Nijeriyar ba shi da katin dan kasa sharrin zama bako ko dan mamaya ko kuma sanya shi cikin masu garkuwa da mutane.

“Rashin katin shaidar zama dan kasa babbar matsala ce ga ’yan Nijeriya musamman wadanda ke zuwa yankin Kudancin kasar nan.

“Amotekun ko wasu kungiyoyin al’adu ne za su tare su, za a tattara su a ce su bayyana kansu da kuma inda suka fito, wasu ma suna zargin su ba ’yan Nijeriya ba ne.

“Wasu za su ce ‘yan Kaduna ne amma ina katin shaida? Babu wata shaida ko da ta lasisin tuki ce.”

Ya kuma bayyana cewa, kungiyarsa na shirin gudanar da wani taro na kwana daya domin karbar bakuncin Malamai akalla 200 a karamar hukumar Gamawa wadanda za su zo a wayar da kan jama’a game da gina kasa da hakkokin ‘yan kasa da ayyukansu sannan kuma su wayar da kan dalibai da ke karkashinsu.

A nasa jawabin, shugaban AIRLIN na Jihar Kaduna Alhaji Musa Muhammed ya ce, kungiyar ta dukufa wajen ganin ta kawo sauyi mai kyau da zai dawo da martaba da mutunta ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa, AIRLIN gida ce ga kowa da kowa musamman wadanda suka yi imanin cewa akwai bukatar a sake farfado al’amuran da suka rushe a Nijeriya.

Taron dai ya samu halartar dukkan shugabannin kungiyar na jiha da na kananan hukumomin jihar, tare da ‘yan rakiyar shugaban na kasa da suka taho

daga Abuja.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru

Kotun tsarin mulkin Kamaru ta haramta wa jagoran adawar ƙasar, Maurice Kamto tsayawa takarar shugaban ƙasa, a babban zaɓe mai zuwa na watan Oktoba, kan abin da ta bayyana rashin cika ka’idojin tsayawa takara.

Lauyansa, Hippolyte Meli Tiakouang ne ya tabbatar wa manema labarai hukuncin kotun wanda ba za a iya ƙalubalanta ba, bayan kammala zamanta na wannan Talata.

A cewarsa, kotun ta yi watsi da ƙarar da suka shigar kan matakin hukumar zaɓen ƙasar na cire shi daga cikin jerin ’yan takarar da za su fafata a zaɓen ranar 12 ga watan Oktoban bana.

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu

Mista Kamto mai shekaru 71, ya yi ƙaurin suna wajen sukar gwamnatin shugaba Paul Biya, kuma shi ne ya yi na biyu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2018, bayan tsayawa takara a jam’iyyar MRC.

A wannan karo kuma ya nemi tsayawa takarar a jam’iyyar MANIDEM, inda ya bayyana muradin tsayawar watanni biyar da suka gabata.

Hukumar zaɓen ƙasar ta yanke hukuncin cire Kamto saboda “’yan takara masu yawa,” bayan wani ɗan takara daga wani tsagin jam’iyyar ya miƙa buƙatar makamanciyar wannan, wanda ya sa ake nuna damuwa kan halascin shugabancin jam’iyyar.

Bayan gabatar da hukuncin, Kamto wanda da alama bai ji daɗin hakan ba, ya fice daga harabar kotun ba tare da magana da ’yan jarida ba.

Hukuncin da aka yanke a ranar Talata ya ƙara tayar da fargabar hargitsi.

An jibge jami’an tsaro a kusa da cibiyar taro da ke babban birnin ƙasar, Yaoundé, inda Kwamitin Kundin Tsarin Mulki ya bayyana hukuncin, da kuma manyan titunan birnin.

A ranar da ta gabata, ’yan sanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye tare da kama mutane da dama da suka fito zanga-zangar goyon bayan Kamto.

Lauyoyinsa waɗanda ba su yi ƙarin bayani kan mataki da za su ɗauka ba, sun ce Kamto ne zai bayyana matakin da zai ɗauka.

Masu suka na ganin cewa akwai wata maƙarƙashiya ne na kawar da ɗan siyasar daga zaɓen.

Duk da raɗe-raɗin rashin lafiya, yanzu haka shugaba Paul Biya mai shekaru 92, wanda ya shafe tsawon shekaru 43 yana mulkin Kamaru, zai sake neman wa’adi na takwas a kan karagar mulki ba tare da wata ƙwaƙƙwarar adawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
  • Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe?
  • NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin minista ba — Sarki Sanusi II
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
  • Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru