AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa
Published: 9th, May 2025 GMT
A wani bangare na manufofinsu na kara yawan masu kada kuri’a, Alhaji Gamawa ya bayyana cewa, kungiyar mai zaman kanta za ta taimaka wa ‘yan kasa wajen karbar katin zabe, “Lokacin da INEC ta bude dandalin rajistar katin zabe, za mu taimaka musu wajen karbar katin zabe domin su bada gudunmawa a zabe da kuma amfani da ’yancinsu.
Gamawa ya kuma yi magana kan muhimmancin samun katin shaidar zama dan kasa, inda ya ce, yayin da tsaro ya yi karanci, abu ne mai sauki a laka wa dan Nijeriyar ba shi da katin dan kasa sharrin zama bako ko dan mamaya ko kuma sanya shi cikin masu garkuwa da mutane.
“Rashin katin shaidar zama dan kasa babbar matsala ce ga ’yan Nijeriya musamman wadanda ke zuwa yankin Kudancin kasar nan.
“Amotekun ko wasu kungiyoyin al’adu ne za su tare su, za a tattara su a ce su bayyana kansu da kuma inda suka fito, wasu ma suna zargin su ba ’yan Nijeriya ba ne.
“Wasu za su ce ‘yan Kaduna ne amma ina katin shaida? Babu wata shaida ko da ta lasisin tuki ce.”
Ya kuma bayyana cewa, kungiyarsa na shirin gudanar da wani taro na kwana daya domin karbar bakuncin Malamai akalla 200 a karamar hukumar Gamawa wadanda za su zo a wayar da kan jama’a game da gina kasa da hakkokin ‘yan kasa da ayyukansu sannan kuma su wayar da kan dalibai da ke karkashinsu.
A nasa jawabin, shugaban AIRLIN na Jihar Kaduna Alhaji Musa Muhammed ya ce, kungiyar ta dukufa wajen ganin ta kawo sauyi mai kyau da zai dawo da martaba da mutunta ‘yan Nijeriya.
Ya kara da cewa, AIRLIN gida ce ga kowa da kowa musamman wadanda suka yi imanin cewa akwai bukatar a sake farfado al’amuran da suka rushe a Nijeriya.
Taron dai ya samu halartar dukkan shugabannin kungiyar na jiha da na kananan hukumomin jihar, tare da ‘yan rakiyar shugaban na kasa da suka taho
daga Abuja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Ya ci gaba da cewa, rungumar wannan tsari; zai kuma taimaka wajen yakar yunwa a kasar nan, inda ya yi nuni da cewa; ana aiwatar da wannan dabarar yakar sauyin yanayi ne ta hanyar yin amfani da dabarun noman gargajiya, wato yin amfani da takin gargajiya da sauyawa daga gonar da aka yi noma zuwa wata gonar daban.
Sauran dabarun ya bayyana cewa, sun hada da yin shuka da ingantaccen Irin noma da kuma yin noman rani.
Kazalika, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sanya wannan tsari ya zama na kasa baki-daya da za a rika yin amfani da shi.
Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, Shugaban Jami’ar Farfesa Suleiman Bala-Mohammed ya ce; kasidar da aka gabatar a wajen taron ta zo a kan gaba, musamman duba da cewa; ana magana ne a kan yadda za a samar da wadataccen abinci a kasar da kuma wanda za a fitar zuwa ketare.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA