An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Published: 11th, May 2025 GMT
A yau Asabar ne kasashen Sin da Amurka suka fara wani babban taron tattalin arziki da cinikayya na matakin koli a birnin Geneva na kasar Switzerland.
A matsayin shugaban tawagar kasar Sin kan harkokin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Amurka da Sin, He Lifeng, wanda mamba ne a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana mataimakin firaministan kasar, ya halarci taron tare da jagoran tawagar Amurka, babban sakataren baitul-malin kasar, Scott Bessent.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ya Ce Gwagwarmaya Zata Ci Gaba Har Zuwa Nasara
Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kasim, ya bayyana cewa mutanen kasar Lebanon zasu ci gaba da gwagwarmaya da HKI wacce ta ke mamaye da wasu kasashen larabawan yankin har zuwa nasara.
Tashar talabijibn ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sheik Kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar ta kafar bidiyo a taron da aka fara gudanarwa a yau a makarantar Darushafia dake birnin Qom.
Taron na Qom yana Magana dangane da “Makarantun Hauza a Qum, Juyin juya halin musulunci a Iran da kuma Gwagwarmaya’.
Sheik Kasim ya kara da cewa mutanen kasar Lebanon sun fara gwagwarmaya ne bayan gwamnatin HKI ta mamaye kasarsu, sannan bayan sun sami jagoranci da tunanin Imam Khumaini (q) wanda ya kafa JMI. Yace tunanin Imam Khumaini Q ne ya taiamakawa mutanen kasar Lwabanon suka kai inada suka kai. Kuma alkawalin All…Gaskiya ce, nasara tana zuwa ga musulmin yankin da kuma duniya gaba daya.