Kasar Siriya ta rikide daga Jihadi da zaluncin gwamnatin mamayar Isra’ila zuwa ga kulla kyakkyawar alaka da gwamnatin ‘yan mamaya

Gaskiya ta fara bayyana daya bayan daya, sannan makirci da makarkashiyar kungiyoyin masu dauke da makamai bisa da’awar gudanar da jihadi a Siriya suka fara bayyana ga al’umma, masu da’awar jihadi sun kama hanyar fitar da Siriya daga cikin sahun masu fada da makirce-makircen yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya ta hanyar kulla kyakkyawar alaka da su, da janyewa daga duk hakkokin kasar Siriya da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta mamaye na Siriya a baya-bayan nan.

Manufar samar da sabuwar gwamnatin masu da’awar jihadi, kamar yadda aka sani, ita ce tabbatar da tsaron babban sansanin Amurka mafi girma a yanking abas ta tsakiya, wato “haramtacciyar kasar Isra’ila.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya zargi Iran da Isra’ila da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta.

Da yake jawabi kafin tafiyar Babban Taron Ƙungiyar NATO, da zai gudana a birnin Hague, Trump, ya bayyana takaicinsa bisa yadda kasashen biyu game da saɓa yarjejeniyar, sa’o’i kaɗan bayan sun amince da ita.

Tun da farko sai da ya buƙaci Isra’ila ta janye shirinta na kai wa Iran hari.

A safiyar Litinin bayan sanarwar Trump cewa ɓangarorin sun amince su tsagaita wuta ne, Ministan Tsaron Isra’ila ya yi barazanar kai wa Iran hari mai tsanani bayan zargin ta da harbo wa ƙasarsa rokoki.

Iran ta musanta zargin tare da cewa Isra’ila za ta yaba wa aya zaƙi idan kuskura ta kawo mata hari.

Daga bisani Trump ya ce wa Isra’ilar, “Kada ki kai harin bom a Iran, yin kika babban saɓawa ne. Ki umarci matuƙa jiragenkinki su koma gida.”

Buƙatar tasa bayan fara tsagaita wuta da Iran ta yi, na da alaƙa da sabon tayar da jijiyoyin wuts tsakanin Iran da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
  • An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin