Kwamnadan Dakarun IRGC Yace Sojojinsa A Shiye Suke Su Kare Kasar Daga Makiya
Published: 14th, May 2025 GMT
Babban kwamadn dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran ko (IRGC) Manjo Janar Hussain Salami ya bayyana cewa dakarun kare juyin jya halin musulunci a nan Iran a shirye suke don fuskantar duk wani kuskureb da makiya zasu yin a kawowa kasar Hare-hare.
Janar Salami ya bayyana haka ne a jiya Talata a lokacinda yake wani Jawabi a birnin Mashad na arewa maso gabacin kasar Iran.
Janar Salami yana wannan maganane bayan da shugaban kasar Amurka Dunal Trump wanda yake ziyarar wasu kasashen larabawa a yankin yammacin Asiya, na cewa idan an kasa cimma dai-daito tsakanin Iran da Amurka a tattaunawa kan shirinta na makashin nukliya to Iran ta shiryawa yaki.
Salami ya kara da cewa sun san makiyan JMI a wannan yankin, a duk lokacinda hanyoyin tattaunawa da Diblomasiyya sun kasa kaiwa ga fahintar juna to kuwa sojojin kasar Iran musamman dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar a shirye suke su kare kasar da kuma mutuncinta.
Manjo Janar Salami ya bayyana cewa: Karfin sojoji da kuma dakarun kare juyin juya halin musulunci karuwa yake a ko wace shekara.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin
এছাড়াও পড়ুন:
Burtaniya Ta Gabatar Da Sabbin Tsare-Tsare Na Shige Da Fice Da Kuma Bisar Shiga Kasar
Gwamnatin kasar Burtaniya ta gabatarwa majalisar dokokin kasar sabbin tsare-tsare na shigar kasar ta hanyoyi daban-daban.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto Firai ministan kasar ta Burtania Keir Starmer yana fadar cewa abinda yake gabatarwa Majalisar don neman amincewarta, wani tsari ne wanda zai kawo tsabta a harkokin bada Visar shiga kasar Burtaniya daga kasashen duniya daban-daban.
Starmer ya kara da cewa kafin haka tsarin shige da fice a kasar ta zama a tarwatse yake. A halin yanzu bayan samar da wadannan tsare-tsare masu zuwa kasar Burtania ko wadanda suke son zama a kasar dole ne su zama masu amfanar kasar,. Da farko dole su iya turancin ingishi da wasu abubuwan da zasu taimawa ci gaban kasar.
Kafin haka dai kididdiga ta nuna cewa zuwa cikin watan Yunin shekarar da ta gabata kadai mutane kimani 906, 000 suka kaura zuwa kasar. Wanda ya ninka na shekara ta 2019 har sau 4.
Yan Najeriya dai na daga cikin wadanda suke kaura zuwa kasar Burtaniya, ko don karatu ko aiki.
Mai yuwa wannan sabon tsarin yana iya shafar kasar.