Kasar Sin ta zage damtse kan wannan aiki inda ta kuduri aniyar yin ginin tashar da kayan da aka sarrafa da albarkatun duniyar wata, tare da tabbatar da cewa suna da ingancin da za a iya dogaro da su. Wannan zai zama ta harbi tsuntsu biyu da dutse guda, na farko zai saukaka sufurin jigila da kuma kula da gyaran tashar yadda ya kamata.

Babban jagoran tsara aikin binciken duniyar watan, Wu Weiren ya ce kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta kera injin buga tubali ko bulon gini na kasar duniyar wata ta hanyar amfani da kayan aiki da aka sarrafa daga albarkatun duniyar watan. Injin yana aiki ne ta hanyar janyo makamashin hasken rana tare da kaiwa tarin kasar buga tubalin. Daga nan kasar za ta narke idan zafin makamashin ya kai digiri 1,400 zuwa 1,500 a ma’aunin Celsius, inda hakan zai bayar da damar buga bullon cikin sauki a duk yanayin girman da ake bukata.

Tuni dai aka aike da wani samfurin tubalin kasar duniyar wata da aka sarrafa da wasu kayayyaki makamantan na duniyar wata domin nazari a kai a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin don gano irin sinadaran dake ciki da kuma karkon tubalin. Ana sa ran dawo da samfurin tubalin zuwa doron kasa a karshen 2025.

Fatan kasar Sin kamar yadda shugaban tsara wannan aiki Mista Wu ya bayyana shi ne, sauran kasashen duniya su shiga cikin wannan bincike a dama da su wajen samun nasarar gina katafariyar tashar binciken albarkatun duniyar wata ta kasa da kasa, saboda a kullum burin Sin shi ne gina al’umma mai makoma ta bai-daya ga bil’adama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: duniyar wata

এছাড়াও পড়ুন:

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Haka zalika, sun ki bayyana takamaiman wajen da za a daura auren, har sai bayan an kammala, inda suka bayyana yin hakan a matsayin wata hanya ta kawar da cece-kuce daga al’umma.

 

Kazalika a ‘yan watannin da suka gabata kuma, an sake daura auren jaruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau tare da angonta Ibrahim Garba, a wani biki wanda za a iya kira da na sirri da aka gudanar a birnin Kaduna, daura auren shahararriyar jarumar Kannywood din, Rahma Sadau da mijinta Ibrahim Garba, wanda aka gudanar a ranar Asabar, ya yi matukar bai wa mutane mamaki, duba da cewa; kafin daurin auren babu wata alama ko sanarwa da aka fitar daga makusantan mijin ko matar.

 

An yi bikin da safe, a Masallacin Atiku Auwal da ke Unguwar Rimi, inda ‘yan’uwa da abokan arziki suka halarta, Rahma yayin da take magana da manema labarai ta bayyana cewa; ta zabi yin bikin cikin natsuwa ne, domin kauce wa hayaniya, bayan labarin ya bayyana a kafafen sada zumunta, ta tabbatar da daura auren nata.

 

Rahma ta shahara a fina-finan Kannywood da kuma wasu daga cikin fina-finan Nollywood, bayan da aka daura auren, masoyanta da abokan aikinta, suka tura mata sakwannin taya murna daga sassa daban-daban na Nijeriya, wannan aure ya zo ne watanni kadan bayan rasuwar mahaifinta, wanda ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.

 

Haka yasa ake saka alamar tambaya a kan jaruman masana’antar ta Kannywood, a kan cewa; me ya sa suke daura aurensu a sirrance? Yayin da wasu ke ganin yin hakan a matsayin wata hanya ce da jaruman ke bi wajen kauce wa bakin mutane, wasu kuma na ganin wannan a matsayin wata hanya ta nuna girman kai ko isa da jaruman ke bi, domin nuna wa duniya cewa; su ba kamar sauran al’umma ba ne.

 

Koma dai mene ne, akwai bukatar jaruman su tuna cewa; suna da dimbin mutane da ke kiran kansu a matsayin masoyan jaruman, wanda ko babu komai dai, bai dace a ce masoyinka ba shi da labarin wani abin alherin da ya same ka ba, musamman harka ta aure, wadda ka iya zama silar daina fitowa a fina-finai ga jarumai mata da mazajensu, ba su amince su ci gaba da harkar fim ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nishadi Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano October 6, 2025 Nishadi An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana October 4, 2025 Nishadi Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa September 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha
  • Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa
  • Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa