Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Published: 15th, May 2025 GMT
Kasar Sin ta zage damtse kan wannan aiki inda ta kuduri aniyar yin ginin tashar da kayan da aka sarrafa da albarkatun duniyar wata, tare da tabbatar da cewa suna da ingancin da za a iya dogaro da su. Wannan zai zama ta harbi tsuntsu biyu da dutse guda, na farko zai saukaka sufurin jigila da kuma kula da gyaran tashar yadda ya kamata.
Babban jagoran tsara aikin binciken duniyar watan, Wu Weiren ya ce kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta kera injin buga tubali ko bulon gini na kasar duniyar wata ta hanyar amfani da kayan aiki da aka sarrafa daga albarkatun duniyar watan. Injin yana aiki ne ta hanyar janyo makamashin hasken rana tare da kaiwa tarin kasar buga tubalin. Daga nan kasar za ta narke idan zafin makamashin ya kai digiri 1,400 zuwa 1,500 a ma’aunin Celsius, inda hakan zai bayar da damar buga bullon cikin sauki a duk yanayin girman da ake bukata.
Tuni dai aka aike da wani samfurin tubalin kasar duniyar wata da aka sarrafa da wasu kayayyaki makamantan na duniyar wata domin nazari a kai a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin don gano irin sinadaran dake ciki da kuma karkon tubalin. Ana sa ran dawo da samfurin tubalin zuwa doron kasa a karshen 2025.
Fatan kasar Sin kamar yadda shugaban tsara wannan aiki Mista Wu ya bayyana shi ne, sauran kasashen duniya su shiga cikin wannan bincike a dama da su wajen samun nasarar gina katafariyar tashar binciken albarkatun duniyar wata ta kasa da kasa, saboda a kullum burin Sin shi ne gina al’umma mai makoma ta bai-daya ga bil’adama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: duniyar wata
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ’yan bindiga suka kashe jarirai, suka bai wa karnuka namansu a Zamfara
Ɗan Majalisa mai wakiltar yankin Kaura Namoda da Birnin Magaji a jih6ar Zamfara, Hon. Aminu Sani Jaji, ya bayyana yadda ’yan bindiga suka bai wa karnuka wasu jairirai tagwaye da aka haifa a daji su ci.
Jaji, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba.
Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi Zaɓen 1993: IBB ya wallafa ba daidai ba a littafinsa — Sule LamiɗoYa ce maharan sun sace wata mata mai ciki a wani ƙauye da ke Zamfara, kuma bayan ta haihu, ’yan bindigar suka jefa wa karnuka domin ci su.
Ya kuma ruwaito yadda wani yaro mai fama da cutar farfaɗiya ya mutu bayan da ya faɗi a dajin.
Ya ce ’yan bindigar sun nemi mahaifin yaron da ya miƙa musu shi, gudun ka da ya rasa sauran yaransa ya umarci yaron ya je wajensu.
Yaron ya yarda ya tafi, kuma nan take suka harbe shi har lahira.
Ɗan majalisar ya ce irin waɗannan abubuwa na nuna cewa gwamnati ta kasa kare mutane a Zamfara.
Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa.
Ya bayyana yadda ya yi alƙawari kafin zaɓen 2023, inda ya faɗa wa jama’a cewa sabuwar gwamnati za ta bai wa tsaro muhimmanci, amma yanzu al’amura sun ƙara lalacewa.
“Mun cuci mutanenmu. Ba sa iya zuwa gonakinsu. Tattalin arziƙinsu ya rushe. Mutane da dama sun rasa matsuguninsu, kuma babu wani taimako daga gwamnati,” in ji shi.
Ya ce ya gana da wasu shugabannin tsaro har da Ministan Tsaro, amma babu wani canji da aka samu.
“Zamfara tana cikin aminci. Yanzu kuwa, tana daga cikin wuraren da rikici ya fi ƙamari. Kundin tsarin mulki ya ce gwamnati na da alhakin kare rayuka da dukiyoyi, amma hakan ba ya faruwa a yanzu.”
Da aka tambaye shi game da bai wa jama’a dama su kare kansu, sai ya ce doka ta fi komai.
“Mu ’yan majalisa ne, ba ma’aikatan tsaro ba. Ba za ce mutane su ɗauki makami ba. Amma gaskiya ne, mutane suna ganin yadda aka bar su,” in ji Jaji.