Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Published: 15th, May 2025 GMT
Kasar Sin ta zage damtse kan wannan aiki inda ta kuduri aniyar yin ginin tashar da kayan da aka sarrafa da albarkatun duniyar wata, tare da tabbatar da cewa suna da ingancin da za a iya dogaro da su. Wannan zai zama ta harbi tsuntsu biyu da dutse guda, na farko zai saukaka sufurin jigila da kuma kula da gyaran tashar yadda ya kamata.
Babban jagoran tsara aikin binciken duniyar watan, Wu Weiren ya ce kasar Sin ita ce ta farko a duniya da ta kera injin buga tubali ko bulon gini na kasar duniyar wata ta hanyar amfani da kayan aiki da aka sarrafa daga albarkatun duniyar watan. Injin yana aiki ne ta hanyar janyo makamashin hasken rana tare da kaiwa tarin kasar buga tubalin. Daga nan kasar za ta narke idan zafin makamashin ya kai digiri 1,400 zuwa 1,500 a ma’aunin Celsius, inda hakan zai bayar da damar buga bullon cikin sauki a duk yanayin girman da ake bukata.
Tuni dai aka aike da wani samfurin tubalin kasar duniyar wata da aka sarrafa da wasu kayayyaki makamantan na duniyar wata domin nazari a kai a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin don gano irin sinadaran dake ciki da kuma karkon tubalin. Ana sa ran dawo da samfurin tubalin zuwa doron kasa a karshen 2025.
Fatan kasar Sin kamar yadda shugaban tsara wannan aiki Mista Wu ya bayyana shi ne, sauran kasashen duniya su shiga cikin wannan bincike a dama da su wajen samun nasarar gina katafariyar tashar binciken albarkatun duniyar wata ta kasa da kasa, saboda a kullum burin Sin shi ne gina al’umma mai makoma ta bai-daya ga bil’adama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: duniyar wata
এছাড়াও পড়ুন:
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje
A cikin wata wasika mai kwanan wata 23 ga Mayu, 2025, mai lamba CR/3000/IGP-SEC/MU/ADM/14/ABJ/VOL 118/57, wacce aka aike wa sakataren gwamnatin jihar Kano, na cewa, IGP ya bukaci a mika Bature zuwa gaban wani jami’i, SP Mojirode B. Obisiji a ranar Alhamis 29 ga Mayu, 2025, domin amsa tambayoyi.
In ba a manta ba, IGP a watan Disamba, 2024 ya ba da irin wannan umarni tare da tura jami’an sa ido na IGP domin su kamo mai magana da yawun Gwamnan Kano tare da kai shi hedikwatar rundunar da ke Abuja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp