2025-09-18@07:06:40 GMT
إجمالي نتائج البحث: 267
«kawar da cutar»:
Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025. Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci. Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Shugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696. Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar. Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba. Sai dai an...
Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano. Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman. Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono Ya ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar. “Mun fara wannan shiri fiye da shekara...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Rikicin kwamitin gudanarwa da malaman Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Bida (Bida Poly), ya ƙara ƙamari bayan da makarantar ta dakatar da ayyukan Kungiyar Malamai (ASUP) sannan ta kawo sojoji domin kula da jarrabawa da dalibai ke gudanarwa. Ƙungiyar ASUP reshen kwalejin ta shiga yajin aiki mara wa’adi, domin neman a biya su alawus ɗin ƙarin aiki na watanni 18 da suka wuce. Ƙungiyar ta umarci mambobinsu da kada su gudanar da jarrabawar zangon da ta fara ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025. Wani ma’aikacin makarantar ya shaida wa wakilinmu cewa sojojin an gayyace su ne domin kare ɗalibai da wasu malamai daga shirin da ASUP ke yi na hana gudanar da jarrabawa. ’Yan bindiga sun kai wa sojoji...
Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi. Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka. NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna Rahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar. A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a...
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta. Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa. Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba. Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon...
A yau Lahadi ne wakilan kasashen Sin da na Amurka, sun isa birnin Madrid na kasar Sifaniya, domin gudanar da tattaunawa game da batutuwan tattalin arziki da cinikayya. Cikin kwanaki masu zuwa, sassan biyu za su zanta game da batutuwan da suka hada da matakin Amurka na kakaba haraji, da karya ka’idar kayyade fitar da hajoji, da batun dandalin TikTok, kamar dai yadda kakakin ma’aikatar cinikayyar Sin ya tabbatar a ranar Jumma’a. (Saminu Alhassan) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
An gano gawar Haneefa, yarinya ’yar shekara uku da ruwa ya tafi da ita lokacin da yayarta Fatima, ke goye da ita yayin ambaliyar da ta rutsa da su a Tudun Jukun da ke Zariya, a Jihar Kaduna. An tsinci gawar ne bayan kwanaki shida da aka kwashe ana nemanta, a gangaren ƙasan Kilaco, unguwar Gyallesu, da misalin ƙarfe 11 na safiyar ranar Lahadi. Ambaliya: NEDC ta raba wa mutum 2,200 kayan agaji a Yobe Likitoci sun janye yajin aikin da suka fara bayan kwana biyu Babban jami’in ƙungiyar Red Cross a Zariya, Abdulmumin Adamu ne, ya tabbatar da gano gawar, inda ya ce hakan ya kawo ƙarshen binciken neman mutanen da ruwa ya tafi da su. A ranar 8...
“An ajiye gawar a ɗakin ajiye gawarwaki yayin da bincike ke ci gaba. Za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala binciken.” Da yake magana kan sauran masu laifi da aka kama a faɗin ƙananan hukumomi 18 na jihar, kwamishinan ya ce an cafke su ne bisa zargin aikata laifuka da suka haɗa da: kisan kai, garkuwa da mutane, fashi da makami, shiga ƙungiyoyin asiri, mallakar miyagun ƙwayoyi ba bisa doka ba, da sata, da sauransu. Lawal ya nuna cewa an samu nasarar waɗannan kame ne ta hanyar ƙoƙarin jami’an rundunar da kuma haɗin kan jama’ar jihar, waɗanda suka bayar da sahihan bayanai ga rundunar. A cewarsa: “A cikin makonnin da suka gabata, rundunarmu ta...
Kakakin rundunar ’yansandan Jihar Taraba, ASP Leshen James, ya tabbatar da lamarin, inda ya ce suna neman saurayin tare da sauran mazauna gidan da suka tsere. “Lokacin da jami’anmu suka isa wajen, ba kowa a cikin gidan. Saurayin da sauran mazauna gidan sun riga sun gudu,” in ji shi. Ya ƙara da cewa ’yansanda za su gudanar da bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru da Comfort. Lamarin ya haifar da firgici da damuwa ga ɗalibai da mazauna yankin. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu...
ya kuma isa wurin tare da gano gawar mamacin a cikin wata mota ƙirar ‘Peugeot 406’, ɗauke da lamba kamar haka; BWR-577 BF. “Ba tare da ɓata wani lokaci ba, aka kai gawar zuwa babban asibitin Asokoro, inda likitoci sukatabbatardacewa; hargawar ta fara ruɓewa. “Kwamishinan ƴansanda na babban birnin tarayya Abuja, ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike kan wannan al’amari da ya faru tare da bayar umarnin ƙara ƙaimi wajen gano ko wane ne mamacin.” Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Yayin da aka gano gawar Surajo a ranar Litinin, an gano gawar Fatima washegari, Talata. Sai dai har yanzu ba a gano gawar kanwar Fatima ‘yar shekara uku, Haneefa ba. A lokacin da lamarin ya faru, Fatima tana goye da kanwarta Haneefa mai shekaru uku a duniya. Su biyun suna dawowa ne daga gidan kakarsu da ke Magume zuwa gidan su da ke Tudun Jukun. Malamin Islamiyyar su Fatima, mai suna Malam Daddy ne ya yi musu rakiyar hanya acikin kekensa mai taya Uku (Keke-napep). Shaidun gani da ido sun ce, abin takaicin ya afku ne a mahadar da ke kusa da Cocin Nasara Baptist da ke kan hanyar Gaskiya babban layi a Tudun Jukun. ...
Kasar Sin da Tarayyar Afrika (AU), sun yi alkawarin karfafa goyon bayan juna wajen gina tsarin jagorantar harkokin duniya bisa adalci tare da tabbatar da zaman lafiya a duniya. An yi alkawarin ne a ranar Juma’a yayin wani taron manyan jami’ai a Addis Ababa na Habasha, albarkacin cika shekaru 80 da Sinawa suka yi nasarar turje wa harin Japan da yakin duniya na II. Da yake jawabi ga taron, Jiang Feng, shugaban tawagar kasar Sin a AU, ya nanata bukatar tunawa da tarihi da karfafa hadin gwiwa a duniya domin shawo kan kalubalen tsaro da duniya ke fama da su. Da yake jawabi a madadin kwamishinar kula da harkokin lafiya da jin kai da ci gaban al’umma Amma Twum-Amoah, babban...
Sanarwar ta ce, “E-NEC ta yi Allah-wadai da gazawar Gwamnatin Tarayya wajen cika alkawuranta, tare da nuna bakin ciki cewa babban adadin likitocin kasar ba a biya su ba don Asusun Horon Likitocin Kasar na shekarar 2025. Haka kuma, gwamnati ta ki biyan bashin watanni biyar da suka rage sakamakon sake duba tsarin albashin Likitocin Hadin Gwiwa na kashi 25/35, da sauran tsofaffin bashin albashi.” “E-NEC ta nuna rashin jin dadinta kan dankwafe mutane ba bisa ka’ida ba na takardun membobinsu na Kwalejojin Likitoci da Masu Koyar da Lafiya na Yammacin Afirka (WACP/WACS) da Hukumar Likitocin Hakoran Nijeriya (MDCN) ta yi, da kuma ci gaba da rashin bayar da takardun mambobinsu daga Kwalejin Likitocin Kasa na Bayan Digiri (NPMCN).”...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Gwamnatin Nijeriya ta bayyana goyon bayanta kan shirin mayar da rubuta Jarabawar Kammala Sakandare ta Yammacin Afirka (WAEC) da komfuta wato CBT daga shekarar 2026. Wannan babban sauyin, wanda aka tsara cewa zai fara aiki a shekarar 2026 ya jawo mabambantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin ilimi. An kama wata uwa kan binne jaririyarta a Kebbi Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja Da yake jawabi a gaban Majalisar Dokoki da manyan masu ruwa da tsaki a wani taron wayar da kai a Abuja, Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya ce jarabawa ta tsarin CBT da za a dinga yi a duk faɗin ƙasar, zai ƙarfafa tsarin ilimin ƙasar. Alausa ya ce Gwamnatin Tarayya tana...
Kan batun yiwuwar Obi zai koma PDP, Wike ya yi watsi da shi, ya ce hakan zai jawo wa jam’iyyar matsala. “Obi ya zargi PDP, ya ce jam’iyyar ta lalace. Yanzu kuma jam’iyyar ta gyara kenan a gare shi? Wannan zai kashe jam’iyyar,” in ji shi. Wike ya ce dawo da Obi saboda kawai neman mulki zai rusa ƙa’idoji da mutuncin jam’iyyar. Ya dage cewa hanyar da PDP za ta sake bi domin farfaɗowa ita ce bin tsarin rabon mulki, adalci da gaskiya, ta yadda shugabancin ƙasa zai koma Kudu. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin...
Dakarun Kai Daukin Gaggawa ta kasar Sudan sun kai hare-hare kan sansanin Abu Shouk da ke birnin El Fasher da manyan bindigogi Majiyar sojojin Sudan ta shaidawa gidan talabijin na Al Jazeera cewa, dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces (RSF) sun yi luguden wuta kan sansanin ‘yan gudun hijira na Abu Shouk da ke El Fasher, babban birnin arewacin Darfur a ranar Litinin. Haka zalika majiyoyin ba su bayar da alkaluman hasarar dukiya ko hasarar rayukan mutane da aka yi a sansanin ba, wanda mazauna sansanin ke fama da matsananciyar rayuwa. Ofishin kai daukin gaggawa na sansanin ya tabbatar da cewa: Mazauna yankin na fama da karancin abinci, magunguna, da ruwa, wanda hakan ke shafar lafiyarsu da mayar...
Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyed Abdul Malik al-Houthi ya yi kakkausar suka kan harin wuce gona da iri da Isra’ila ta kai a birnin San’a wanda ya kai ga shahadar firaministan kasar Yemen da wasu jami’an farar hula da dama. A cikin wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin na jinjinawa shahidai, al-Houthi ya bayyana cewa, “laifi na kai hari kan ministoci da ma’aikatan farar hula ya kara tabbatar da laifukan Haramtacciyar Kasar Isra’ila a yankin,” yana mai jaddada cewa dukkan wadanda suka yi shahada suna gudanar da ayyukansu ne a fagagen da ba na soja ba. Da yake mika ta’aziyyarsa ga iyalan shahidai, abokan aikinsu, da al’ummar kasar Yemen, ya tabbatar da cewa wuce gona da...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Sanata Kabiru Garba Marafa tsohon ɗan Majalisar Dattawa da ya wakilci yankin Zamfara ta tsakiya jigo a Jam’iyar APC a jihar ya fice daga jam’iyar. Sanata Marafa ya bayyana ficewarsa a wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook a ranar Jumu’a ya ce bayan tattaunawa da magoya bayansa sun cimma matsayar barin Jam’iyyar APC kan ta zalunce su. An kama wani mutum da laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita Ƙara Kuɗin Fasfo: Gwamnati na jefa ’yan Najeriya cikin matsi — Obi “Bayan mun yi waiwaye a shekara biyu da rabi da suka gabata mun gano cewa, APC a matakin ƙasa da jiha ta zalunce mu, a matakin jiha lalacewar jam’iyar ya kai matuƙa tun bayan kafa kwamitin riƙon...
Ba wai muna yin jayya da sanarar da ofishin Nuhu ya samu a tsakanin wadannan watanni ba ne kuma muna sane da kokarin da yake yi, na ganin cewa, ‘yan Nijeriya na samu su kwanta su yi barcin dare, idanuwansu biyu a rufe ba tare da wata fargabar ko za a kai masu hari ba. Tabbas, muna jinjina masa kan yunkurin da yake ci gaba da yi na rage kalubalen rashin tsaro da Gwamnatin mai ci ta gada. Amma mummunan harin da wasu mahara suka kai a watannin baya a yankin Yelwata, inda suka yi wa wasu al’umomin yankin kisan kiyashi da kuma harin da ‘yan bindiga suka kai kan Masallaci a garin Malumfashi ta Jihar Katsina, ba...
Musiba da auka wa wani gida a Zariya da ke Jihar Kaduna, bayan da katangar wani kango da ke maƙwabtaka da su ta faɗa wa mazauna gidan suna tsaka da barci. Wakilinmu ya ruwaito cewa, ruftawar ginin wadda ta auku a safiyar wannan Larabar ta yi ajalin matar gidan, Habiba Nuhu da ’ya’yanta biyu, Hauwa’u da Aina’u Nuhu. Wani ɗan sanda ya harbe soja a Bauchi A ɗora min laifin hatsarin jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja — Shugaban NRC Sai dai mijinta, wanda shi ma ya samu rauni a sakamakon faruwar lamarin, tuni an sallamo shi bayan duba lafiyarsa a asibiti. Wani maƙwabcinsu, Malam Ahmed, ya shaida wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4 na asubahi,...
An yi kiciɓus da gawar wata budurwa mai shekaru 14 a cikin gidansu da ke unguwar Dandinshe a Ƙaramar Hukumar Dala da ke Jihar Kano. Lamarin dai ya ɗugunzuma mazauna unguwar yayin da Aminiya ta riski iyaye, ’yan uwa da kuma maƙwabta cikin alhini a yayin ziyarar da ta kai har gida. Hisbah ta haramta al’adun gargajiya yayin bukukuwan aure a Bauchi Trump ya yi barazanar korar Gwamnar Babban Bankin Amurka Bayanai sun ce an yi arba da gawar Fatima Sulaiman rataye a jikin wata taga a cikin gidansu, lamarin da ya jefa shakku da ayoyin tambaya kan musabbabin mutuwarta. Aminiya ta zanta da mahaifiyar marigayiyar, Malama Madina Inuwa Makwalla, wadda ta bayyana ganawa ta ƙarshe da ta yi da...
Mataimakin Ministan harkokin wajen Iran da takwarorinsa na Faransa, Jamus, da Birtaniyya za su gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawa a birnin Geneva na kasar Switzerland, a daidai lokacin da kasashen uku ke barazanar aiwatar da abin da ake kira tsarin dawo da takunkumin Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya a kan Iran. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya fada a ranar Litinin cewa, za a koma yin shawarwari tsakanin wakilan Iran da E3 a ranar Talata. Ya ce za a gudanar da taron ne a matakin mataimakan ministocin harkokin waje da daraktocin siyasa. Hakan na zuwa ne bayan wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da babban wakilin kungiyar EU mai...
Wani babban kusa a kungiyar Hamas ya yi Allah wadai da kin amincewar firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu na kin amincewa da sabuwar shawarar da masu shiga tsakani suka yi na tsagaita bude wuta a Gaza. Mamban ofishin siyasa na kungiyar Hamas Bassem Naim, ya fada a ranar Lahadin da ta gabata cewa da gangan Netanyahu ya dakatar da tattaunawar sulhun Gaza don kare kansa da kuma majalisar ministocinsa na masu tsattsauran ra’ayi, da kuma zafafa yakin da ake yi kan al’ummar Gaza. Ya bayar da misali da rahotannin da kafafen yada labarai na baya-bayan nan da ke nuni da cewa gwamnatin kasar ta yi watsi da yarjejeniyar wani bangare da Hamas, yana mai cewa Tel Aviv na son cimma cikakkiyar...
An tsinci gawar wani saurayi mai suna Daniel Ekanen, mai kimanin shekaru 18, a gefen wani kudiddifi da ke unguwar Ikot Effanga a Ƙaramar Hukumar Kalaba, Jihar Kuros Riba. Lamarin ya jefa firgici a zukata da kuma zaman dar-dar a cikin mazauna yankin, inda aka ruwaito cewa an kawo marigayin ne wurin dangin mahaifinsa daga ƙauyen Ikot Offiong da ke ƙaramar hukumar Odukpani a jihar. Sarkin Musulmi ya ayyana Litinin 1 ga watan Rabi’ul Awwal Dangote ya ci gaba da zama attajiri mafi arziƙi a Afirka — Forbes Rahotanni sun nuna cewa ana zargin masu tsafi da sassan jikin ɗan adam ne suka yi kisan, domin kuwa an yanke kansa kafin a jefar da gawarsa a gefen kudiddifin. Wani daga...
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin kasar Armenia ta yi alkawalin cewa babu wani sojojin Amurka da zai shiga yankin kaukas ta kudu kusa da kanika da kasar Iran. Musamman ta san cewa Iran bata son haka hakama kasar Rasha. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Arachi yana fadar haka, bayan tattaunawa da jami’an gwamnatin Armenia a lokacin da shugaban Iran masoud Pezeshkiyan ya kai ziyarar kasar ta Armenia. Kafin haka dai a makon da ya gabata ne shuga Trump a fadar “White House” ya gana da shuwagabannin kasashen Armenia da Azerbaijan inda suka rattaba hannu a kan yarjeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu, tare da amincewar Armenia ta bawa Azerbaijan damar...
An sami gawar wani sojan HKI wanda ya taba yaki a Gaza wanda kuma ake zaton shi ya kashe kansa. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jaridar HKI da yaren Hebru mai suna Yedioth Ahronoth yana fadar cewa an gano gawar sojan dan shekara 28 wanda ba’a bayyana sunansa ba a dajin dajin sweezland kusa da yankin tiberias a yau Alhamis. Labarin ya kara da cewa, idan ya tabbata sojan ya kashe kansa ne to kuwa shi ne 17 da suka kashe kansu tun bayan fara yaki a gaza a shekara ta 2023. Ahronoth ya cewa sojan ya yi aiki da runduna ta 99 a gaza a cikin yan makonnin da suka gabata. Sannan a halin yanzu...
Gwamnatin kasar Afirka ta kudu zata fara tattaunawar kasa dangane da talauci da kuma rashin adalci a rabon arziki a kasar. Gwamnatin kasar ta ware kimani dalar Amurka miliyon 40$ don gudanar da tattaunawar. Inda ake saran dukkan mutanen Afrika ta kudu suna da damar bayyana ra’ayinsu dangane da wadannan matsaloli. Na talauci da rashin adalci a rabon arzikin kasar. Ana fatan masana daga ciki da wajen kasar zasu gabatar da ra’ayinsu ta shafukan sadarwan da za’a samar a cikin taron. A halin yanzu fiye da shekaru 30 kenan da fita karkashin mulkin wariya na launin fata tsiraru a kasar, amma har yanzun kasar tana fama da matsalolin talauci, rashin aikin yi aikata laifuka da sauransu. Mutane da dama suna...
An yi kira ga kwararrun kafafen yada labarai da su tabbatar da madogararsu domin tabbatar da samar da kyakykyawan rahoton abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma. Babban Limamin Masallacin Al-Waheed Central, Imam Mustapha Luqman ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wajen taron hadin gwiwa da kungiyar ‘yan jarida ta NUJ ta shirya domin fara taron makon manema labarai na shekara ta 2025, da kuma bikin cika shekara 45 daka guda a Ilorin jihar Kwara Ya shawarce su da su bi ka’ida wajen gudanar da ayyukansu na yada labarai. Imam Lukman ya bukaci masu aikin yada labarai da su kasance masu adalci da kyautatawa a tsakaninsu . A nasa jawabin, Fasto...
Mahalarta taron masu ruwa da tsaki na yini daya don tabbatar da sakamakon bincike kan al’amuran zamantakewa da suka shafi ilimin ‘ya’ya mata a jihar Zamfara, sun bukaci iyaye, shugabannin al’umma, da gwamnati a dukkan matakai da su magance matsalolin da ke hana yara mata zuwa kammala karatun sakandare. Kungiyar AGILE da ke Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar Media and Publicity Consult ta shirya taron masu ruwa da tsaki na rana daya domin tabbatar da sakamakon binciken da aka yi kan ka’idojin zamantakewa da ke kawo cikas ga ’yan mata matasa da ke hana shiga makarantun gaba da sakandare a jihar Zamfara. Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Abubakar Aliyu Liman na Jami’ar Ahmadu Bello da...
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta aiwatar da shirin bayar da kulawar lafiya kyauta ga tsofaffin ma’aikata masu ƙaramin albashi da ke ƙarƙashin tsarin fansho na haɗin gwiwa (Contributory Pension Scheme – CPS), yana mai bayyana shirin a matsayin muhimmin bangare da zai taimaka wa rayuwarsu. A wata sanarwa da mai ba Shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya kuma bada umarnin a gaggauta aiwatar da karin fansho da aka dade ana jiran shi, tare da kafa mafi ƙarancin adadin fansho domin kyautatawa tsofaffin ma’aikata mafi rauni a tsarin CPS. Wannan umarni ya biyo bayan bayani da Daraktar Janar ta Hukumar Kula da Fansho...
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cikakken goyon bayan rundunar ‘yan sanda ga Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano wajen tabbatar da kiyaye dabi’u da yakar munanan halaye a cikin al’umma. CP Bakori ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar wayar da kai da Sakatare na Hukumar, Abba El-Mustapha, ya kai tare da tawagarsa zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sandan Kano. A yayin ganawar, CP Bakori ya yaba da jagorancin hukumar, musamman kokarin da El-Mustapha ke yi wajen tsara harkokin masana’antar Kannywood da kuma kare tarbiyya ta hanyar sa ido mai tsauri. Ya tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin rundunar da hukumar, musamman wajen dakile cin zarafi da amfani da kafafen sada zumunta...
Wata uwa da ’ya’yanta biyar sun riga mu gidan gaskiya a dalilin ruwan sama kamar da bakin ƙwarya wanda ya janyo ruftawar ginin gidansu a ƙauyen Dankama da ke Karamar Hukumar Kaita a Jihar Katsina. Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na dare a ranar Litinin yayin da waɗanda ajalin ya katsewa hanzari ke tsaka da barci. Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri Bayanai sun ce wasu mutum huɗu waɗanda su ma lamarin ya rutsa da su an gaggauta miƙa su asibiti domin samun kulawa. Magidancin da aka yi wa wannan babban rashi, Muhammad Sani Garba, yayin ganawa...
A nasa tsokaci game da batun, wakilin musamman na kasar Sin a yankin kahon Afirka Xue Bing, ya ce Sin ta dade tana goyon bayan matakan wanzar da zaman lafiya da ci gaba a yankin. Ya kuma jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa ta fuskar shawo kan tarin kalubale dake addabar duniya. (Saminu Alhassan) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
A wani gagarumin ci gaba na inganta walwala da ci gaban yara da matasa wadanda suka isa makaranta, Shugaban Hukumar Kula da Ilimin Farko ta Jihar Nasarawa NSUBEB, Dokta Kasim Mohammed Kasim ya karbi tawagar Kids & Teens Resource Center K&TRC a wani taron bayar da shawarwari da aka mayar da hankali kan shirin Ilimi don Lafiya da walwala, wanda UNESCO ke tallafawa. An gudanar da babban taron ne a hedkwatar Hukumar NSUBEB, inda ya samu halartar kwamishinonin hukumar su uku, da Daraktoci da dama, da kuma tawagar K&TRC karkashin jagorancin wanda ya kafa kuma Shugaba, Mista Martin-Mary Falana. Tattaunawar a yayin zaman ta tabo batutuwan da suka shafi rayuwar yara da matasa a jihar, wadanda suka hada...
An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa. A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa. Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025. Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya...
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zargin yin katsalandan a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa’i, ya musanta zargin katsalandan din Iran a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza. A yayin da yake amsa tambaya game da ikirarin da shugaban kasar Amurka ya yi na cewa Iran na tsoma baki a shawarwarin tsagaita bude wuta a zirin Gaza, ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da dukkan kasashen duniya tana yin kakkausar suka kan kisan gillar da ake yi a Gaza tare da goyon bayan duk wani tsari da zai kai ga dakatar da aikata laifuka da kuma rage radadin wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki. Baqa’i ya jaddada cewa; Masu yin shawarwarin...
Yau Litinin, an gudanar da taron dandalin tattaunawar neman sabon tunani na asali na 2025 a birnin Hangzhou dake lardin Zhejiang. Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, Li Shulei, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi. Mahalarta taron sun bayyana cewa, ya kamata mu ci gaba da sa kaimi ga yin gyare-gyare da kirkire-kirkire yayin bunkasa al’adun gargajiya na kasar Sin, da kuma nuna kimar kasar Sin da karfin wayewar kai da al’adu. A sa’i daya kuma, kamata ya yi a horar da manyan kwararru na al’adu, da kyautata tsarin ba da kariyar tarihi da al’adu, don kare albarkatun al’adun kasar Sin.(Safiyah Ma) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu...
Ministan Harkokin Tsaron Ƙasa, Dakta Bello Mohammed Matawalle, ya baiwa iyalan marigayi Sarkin Gusau, Alhaji Ibrahim Bello, gudummawar naira miliyan biyar da kuma kayan abinci, bayan rasuwarsa a ranar Alhamis da ta gabata a birnin Abuja sakamakon gajeruwar rashin lafiya. Dakta Matawalle, ya bayyana alhininsa bisa wannan rashi na Mai Martaba. Baya ga gudummawar kuɗi, ministan ya kuma bada buhunan shinkafa 20, gero 10, masara 10 da kuma dawa 10 ga iyalan mamacin. Wata tawaga mai ƙarƙashin jagorancin Sanata Hassan Muhammad Nasiha, tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara a zamanin mulkin Matawalle ne suka miƙa gudummawar a madadin ministan. Dakta Matawalle ya bayyana marigayi Sarkin Gusau a matsayin shugaba mai ɗabi’a ta gari, wanda ya kasance...
A yau Litinin ne za a yi jana’izar sanannen mawakin kasar Lebanon wanda ya yi fice da wakokin gwgawarmaya da kishin kasa wanda zai sami halartar wakilan gwamnatin kasar da kuma al’umma. Jana’izar za ta kasance ne a majami’ar Raqad Sayyida dake garin Bakfaya. Asibitin Khuri da Rahbani ya rasu ya cika da mutane tun da safiyar yau domin daukar jana’izarsa zuwa garin Bakfaya. A ranar Asabar din da ta gabata ne dai Rahbani ya rasu yana dan shekaru 69 bayan da ya yi gajeruwar rashin lafiya. A lokacin rayuwarsa ya shahara da wakoki na gwgawarmaya da kishin kasa, daga cikin da akwai wakar da ya yi wa Shahid Sayyid Hassan Nasarallah.
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tattaunawar makamashin nukiliya wani zaɓi ne mai mahimmanci wanda ya ƙarfafa matsayin Iran a duniya Ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa; Kasarsa ta shiga shawarwarin makamashin nukiliya ba na kai tsaye ba da Amurka bisa wata cikakkiyar shawarar kasa. Ya kara da cewa; Wannan mataki na diflomasiyya ya karfafa kimar Iran a duniya, bayan da ta samu goyon bayan kasashe fiye da 120 wadanda suka yi Allah wadai da cin zarafin da yahudawan sahayoniyya suka yi wa Iran a baya-bayan nan. Hakan dai ya zo ne a yayin wata ganawa da aka yi da Araghchi, inda ya yi nazari kan batutuwan da suka shafi makamashin nukiliyar...

Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi
Babban jami’in kungiyar Hamas a Zirin Gaza ya bayyana cewa: Makiya yahudawan sahayoniya suna rufe gazawar sojojinsu da kisan kare dangi Khalil al-Hayya babban jami’in kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas a zirin Gaza ya jaddada cewa: Makiya yahudawan sahayoniyya suna rufe gazawar sojojinsu ta hanyar kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen hula. A cikin wani jawabi kai tsaye ta gidan talabijin, Al-Hayya ya bayyana cewa: “Ya ku ‘ya’yan Dakarun Qassam, da na Quds Brigade, da kuma sauran kungiyoyin gwagwarmaya, abin da kuke yi ya kawo cikas ga farmakin da motoci masu sulke na makiya suke yi. Khalil ya jaddada cewa: Babban hafsan hafsoshin sojin makiya yana rufe gazawar sojojinsa da kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen...
An gano gwawar mutum 15 a yayin da ake ci gaba neman wasu uku bayan hastarin kwalekwale da ya auku a yankin Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja. Kwalekwalen ya kife ne a yayin da yake ɗauke da mutum 43 da buhuna 60 na shansherar shinkafa da shanu uku da tumaki biyu a ranar Asabar. Kifewar kwalekwalen ta auku ne a sakamakon karonsa da wani kututture bayan ya ɗauki fasinjojin daga yankin Guni zai kai su kasuwar mako-mako da ke yankin Zumba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro. Manajan Hukumar Albarkatun Koguna ta Ƙasa (NIWA), mai kula da yankin, Akapo Adeboye, ya ce an gano gwawar mutum 15, amma ana ci gaba neman wasu mutum uku, ko da yake cewa...
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya zanta ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Afganistan Amir Khan Muttaki a yau Lahadi inda bangarorin biyu suka tattauna dangantaka tsakanin kasashen biyu da kuma al-amuran yankin wadanda suka hada da batun gaza da kuma halin da take ciki. Kamfanin dillancin labaran Tasnima na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana cewa kasar Iran ta kira taron gaggabawa na kungiyar OIC ta kasashen musulmi don tattauna wannan batun. A nashi bangaren muttaki ya bukaci gwamnatin kasar Iran ta maida yan kasar Afganistan wadanda suke zauna a kasar zuwa gida tare da mutuntasu. Kafin haka dai a lokacin yakin kwanaki 12 tsakanin HKI da Iran jami’an tsaro a kasar...
Don haka nema tayi kira da jama’a kada suyi amfani da shi labarin daya zaman a kanzon kurege da ake ta yadawa,idan wani bayani suke bukata su tuntubi kafa da suka san ba zata yi zuki ta malle ba,ko kuma jami’an ma’aikatar ilimi ta kafar sadarwarsu ko kuma na, WAEC, da NECO. “An ja hankalin ma’aikatar ilimi ta tarayya akan wani labara ko rahoton da ya karade kafafen sadarwa na zamani,inda aka yi maganar cewar ban soke jarabawar WAEC ta shekarar 2025 da aka yi saboda an samu laifin aikata magudi lokacin da ake yin ta. “Ma’aikatar tace don haka tana sanar da jama’a cewa ta yi nesa da kanta,dangane da ita sanarwar ko labarin saboda kuwa ai na kanzon...
An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje. Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin. Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar. A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu. Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato A ranar 19...
An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje. Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin. Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar. A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu. Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato A ranar 19...
Ya zargi gwamnatin da cewa ba ta dauki kwararan matakai na kawo babban gyara a fannin wutar lantarki ba, sannan ta gaza wajen nuna wani hobbasa game da lamarin ballantana har kuma ta dauki matakin gaggawa a cikin shekaru biyu da ta kwashe tana mulki. “Mun wuce rabin lokacin wannan gwamnatin, kuma miliyoyin ‘yan Nijeriya na ci gaba da caji wayoyinsu a tashoshin caji na hannu, suna kashe dubban naira wajen sayen man fetur na janareta domin samun wutar lantarki. “Ina hasken wutan lantarkin da aka yi wa ‘yan Nijeriya al’kawari? Me ya faru da alkawarinku? Kuma har yaushe ‘yan Nijeriya za su ci gaba da zama cikin duhu?” Ya sake dawo wa da alkawarin Tinubu a lokacin yakin neman...
Shugaban kasar Ukraine ya nuna sha’awar ganawa da shugaban Rasha kan neman hanyar warware rikicin da kasashen biyu ke fama da shi Ana ci gaba da yakin Ukraine musamman ta hanyar kai hare-hare da jiragen sama marasa matuka coiki. Ma’aikatar tsaron Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuka ciki guda 105 na Ukraine da aka harba zuwa yankuna tara, a tekun Azov, da kuma cikin kasar Rasha a daren jiya. Shugaban kasar Ukraine Zelenskyy ya ce: Kasarsa tana da kudade don sarrafa tsarin makamai masu linzami na Patriot guda uku kuma yana neman samar da karin kudade don sarrafa wasu bakwai na daban, gami da taimakon abokan huldarsa na kasashen Turai. A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya...
Jami’an diblomasiyya na kasashen Iran da kuma na tarayyar Turai 3 wato Faransa da Jamus da kuma burtaniya sun fara tattaunawa gaba da gaba bayan yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka kai mata. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta kara da cewa wannan tattaunawar yana da matukar muhimmanci don zasu tattauna kan shirin makamashin nukliyar kasar Iran da kuma dauke mata takunkuman tattalin arzikin da su dora mata saboda shirinta na makamshin nukliya. Har’ila yau ana ganin tattaunawar ta Istambul shi zai fayyace makomar dangantaka tsakanin Iran da tarayyar Turai gaba daya nan gaba. Labarin ya kara da cewa tarunn yana gudana ne a cikin ofishin jakadancin kasar Iran dake birnin Istambul kuma Majid Takht-ravanci da...
Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna. Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana. Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Tattaunawa na baya-bayan nan tsakakin HKI da Hamas ya tashi ba tare da wani ci gaba ba a birnin Doha na kasar Qatar. Idan an cimma wannan yarjeniyar dai ana saran musayan fursinoni 10 na HKI sannan za’a saki wasu da dama dake hannun HKI, Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa rashin nasarar wannan taron ya sanya makomar yaki a Gaza cikin rudu don yanzun kuma ba’a san abinda zai faru ba. Kuma bamu san manufar HKI ba a wannan yakin. Wani jami’in Falasdinawa ya fadawa tashar talabijin ta Al-Sharq kan cewa da alamun tawagar yahudawan sunzo ba taren da niyyar cimma wani Abu ba, tunda duk abunda aka tambayesu sai suce sai sun tambayi tel-Aviv,...
Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya reshen jihar Kano, ta bayyana cewa Fursunoni 58 suna rubuta Jarrabawar Kammala Sakandare ta Kasa NECO ta shekarar 2025. Wannan ci gaba ya samu ne bayan biyan kudin rajista da gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi. Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Musbahu Kofar-Nasarawa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Kano. Ya ce wannan karamci na gwamnatin jihar Kano shaida ce ta jajircewarta wajen kula da walwalar fursunoni, gyaran dabi’unsu da kuma dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata. “Biyan kudin rajistar jarrabawa da gwamnatin Kano ta yi alama ce ta jajircewarta wajen samar da dama ga fursunoni domin su...
Rashford dai ya fi son komawa kungiyar kwallon kafa ta Barcelona domin yana ganin zai iya buga abin a zo a gani a kakar wasa mai zuwa sai dai ita kuma Barcelona ta fi son dan wasa Nico Williams na kungiyar Athletico Bilbao ta kasar Spaniya, wanda shima yake son komawa Bardelona da buga wasa idan har Barcelonan za ta iya biyan kudin da aka yi masa farashi. Kungiya ta kwana-kwanan nan da ta nemi Rashford ita ce kungiyar Bayern Munchen ta Jamus, bayan da Liberpool ta ce ba za ta sayar mata da Luiz Diaz ba, ana ganin yanzu kungiyar za ta karkata akalarta zuwa neman Rashford. Kungiyoyi irinsu Newcastle United da Tottenham da kungiyoyi daga Saudiyya duka sun...
Majalisar riƙon ƙwarya ta Gwamnatin Mali ta bai wa Shugaban Mulkin Sojin ƙasar, Janar Assimi Goita, wa’adin mulki na shekara biyar, wanda za a iya sabunta shi fiye da sau daya ba tare da zaɓe ba. A bara ne Janar Goita ya yi alƙawarin maido da mulkin dimokuradiyya a ƙasar, sai dai hakan ba ta samu ba. Tsohon golan Super Eagles, Peter Rufai ya mutu Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad Wannan matakin ya bude hanya ga Janar Goita ya ci gaba da jagorantar kasar ta yammacin Afirka har zuwa aƙalla shekarar 2030, duk da alƙawarin da gwamnatin sojan ta yi na komawa mulkin farar hula a watan Maris na shekarar 2024. Sai dai sabon ƙudirin dokar...
Uwargidan shugaban ƙasa, Remi Tinubu ta bayar da gudummawar Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin ya rutsa da su a wasu yankunan Jihar Filato. Uwargidan shugaban ƙasar wacce ta bayyana bayar da tallafin a yayin ziyarar jaje da ta kai jihar a ranar Alhamis, ta ce kuɗaɗen da ta bayar ba na gwamnati ba ne, kuɗin ta ne da ta tara don taimakawa wasu. Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC “A yau na zo da gudunmawar Naira biliyan 1 don shirin sabuwar Najeriya (Renewed Hope Initiative), ba ni da maƙudan kuɗaɗe, amma abin da nake da shi shi ne in taimaki rayuwar wasu, ba wai in zuba...
Jakadan Pakistan a kasar Sin, Khalil Rahman Hashimi ya ce, “sabuwar dokar ta bayar da karin kariya har ma da wani sauki na musamman ga kamfanoni masu zaman kansu a kasar Sin. Akwai tanade-tanade da dama a kasar Sin wadanda suke bayar da kwarin gwiwa ga kamfanoni masu zaman kansu don su iya bunkasa harkokinsu da kuma ba da gagarumar gudummawa ga tattalin arzikin kasar Sin. Akwai samun moriya da dama da kuma goyon bayan gwamnati har ma da ba da kariya ta fuskar shari’a ga kamfanoni masu zaman kansu.” Shi ma jakadan Nepal a kasar Sin, Krishma Prasad Oli ya ce, “dokar ta sahale wa kamfanoni su gudanar da ayyukansu ba tare da wani matsi ba. Akwai babbar dama...
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ba za a iya kawar da fasahar nukiliya ta hanyar harin bam ba Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ya jaddada cewa: Ba za a iya kawar da fasaha da kimiyyar da ake bukata don inganta sinadarin Uranium ta hanyar kai hare-haren bama-bamai ba. A wata hira da ya yi da tashar talabijin ta CBS, Araqchi ya yi tsokaci kan ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na cewa ana iya komawa tattaunawa da Iran a cikin wannan mako: Araqchi yana mai mayar da martini da cewa: “Ba ya jin za a dawo da tattaunawar cikin gaggawa.” Ya kara da cewa: “Kafin yanke shawarar komawa kan tattaunawar, dole ne Iran ta fara tabbatar da...
Magajin garin birnin Tehran ya bayyana cewa: Karyar ‘yan sahayoniyya ya tonu na cewa ba su kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran ba Magajin garin birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ali-Ridha Zakani ya tabbatar da cewa: Karairayi da ‘yan sahayoniyya suke yadawa dangane da rashin kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran a fili yake karara. Yana mai nuni da cewa akwai kwarararn dalilai da ake da su wadanda suke fallasa karyar wadannan ikirari. A cikin bayanansa, Zakani ya ce: Dalilai kan wadannan karairayi su ne kaburbura gawawwaki da suka hada da fili mai lamba ta 42 a makabartar Al-Jannar – Zahra da ke babban birnin Tehran. Ya...
Dakatar da ayyukan wuce gona da iri kan Iran wani sharadi ne na ci gaba da tattaunawar makamashin nukiliya Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi ya bayyana cewa: Sharadin ci gaba da gudanar da zaman shawarwarin makamashin nukiliyar Iran shi ne dakatar da duk wani matakin wuce gona da iri kan Iran, kuma har yanzu Amurka ba ta dauki wani mataki ba kan wannan batu. A wata hira da tashar BBC game da batun tattaunawar makamashin nukiliyar Iran da Amurka: Takht-e Ravanchi ya ce: “Sun ji daga Amurka cewa a shirye take ta ci gaba da tattaunawar, amma har yanzu ba a tsayar da ranar ba, kuma Iran ba ta amince da...
Dalibai 29 ne suka rasa rayukansu sakamakon turmutsitsin a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya yayin tserewa fashewar taransifoma Akalla dalibai 29 ne suka mutu a birnin Bangui na kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a wani turmutsutsu sakamakon fashewar tiranfomar lantarki a lokacin jarrabawar sakandare, a cewar ma’aikatar lafiya ta Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya. Wata takarda daga ma’aikatar lafiya ta ce: “Mutane 29 ne suka rasa rayukansu bayan an kai su asibitocin birnin Bangui.” Ba a samu ingantattun bayanan yawan wadanda suka mutu ba har zuwa yammacin ranar Larabar da ta gabata, a lokacin da fashewar ta faru, sama da dalibai 5,300 ne ke zana jarrabawar kwana na biyu na jarabawar sakandare.
Wannan ne ma dalilin da yasa wasu ke ganin hadakar za ta iya yin karfi kwarai da gaske, kasancewar ta samu wakilci a sassa daban-daban na wannan kasa. Dalili kuwa shi ne, ‘yansiyasa ne da a baya suka samu damar rike manya-mnyan mukamai, sannan kuma har zuwa yanzu yana da tasiri a fagen siyasar kasar yadda ya kamata. Manya-manyan jiga-jigan da ake gani a cikin wannan sabuwar tafiya ta hadakar jam’iyyar sun hada da: Jagoran adawa a kasar, wanda a baya ya sha yin takarar shugabancin kasa, sannan kuma ko a shekarar 2023 shi ne ya zo na biyu bayan da ya samu kuri’a kusan miliyan bakwai. Alhaji Atiku Abubakar, wanda a yanzu dan jam’iyyar PDP ne; ya kasance guda...
Ana neman tono gawar tsohon Gwamnan Jihar Oyo, marigayi Otunba Christopher Adebayo Alao-Akala, domin yin gwajin jini (DNA) da nufin tantance halastattun ’ya’yansa da za su ci gadon dukiyar da ya bari. Batun tono gawar ta kunno kai ne bayan taƙaddama ta yi tsami a tsakanin ’ya’yan tsohon gwamnan a kan rabon gadonsa. Babbar ’yar marigayin mai suna Uwargida Oluwatoyin Alao-Aderinto ce ta shigar da ƙara a gaban Mai Shari’a Taiwo na Babbar Kotun Jihar Oyo ta hannun lauyanta, Oladipo Olasope (SAN), inda ta roƙi kotun ta bayar da umarnin tono gawar mahaifin nasu daga kabarinsa domin yin gwajin ƙwayar halittarsa ga wasu mutane bakwai da ke iƙirarin cewa su ne halastattun ’ya’yan marigayin. Uwargida Aderinto ta shigar da ƙarar...

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Tawagogin tattauna batutuwan cinikayya da tattalin arziki na Sin da Amurka, sun kara tabbatar da bayanan tsarin aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin tattaunawar da suka yi ta wayar tarho a ranar 5 ga watan nan na Yuni, da karfafa sakamakon da aka cimma a tattaunawar cinikayya da tattalin arziki da aka yi a Geneva. Kakakin ma’aikatar kula da cinikayya na Sin ne ya bayyana haka yau, inda ya ce an tabbatar da bayanan ne bayan bangarorin biyu sun ci gaba da tuntubar juna bayan tattaunawa mai ruwa da tsaki da suka yi a birnin London a ranekun 9 da 10 ga wata. Ya ce Sin za ta bi tsarin doka wajen sake nazari da...
Wasu gungun ƙudan zuma sun kai hari tare da tarwatsa ɗaliban da ke rubuta jarrabawar Hukumar da ke shirya jarrabawar kammala sakandare ta ƙasa ta Najeriya (NECO) a makarantar sakandaren kimiyya ta Mairi da ke Maiduguri a Jihar Borno. Wannan hari na ba-zata da gungun ƙudan zumar suka kai ya tilastawa ɗalibai da malaman makarantar tserewa daga harabar makarantar domin neman tsira. Shugaban APC na ƙasa Ganduje ya yi murabus NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe Shaidun gani da ido sun ce, sun ga ɗalibai na barin litattafai da takalma da jakunkuna, har ma da kekunansu yayin da suke gudu daga makarantar. A cewar wani ɗalibin da ke jarabawar da ya nemi a sakaya sunansa ya...
Duk da haka, a cikin ‘yan shekarun da suka wuce, rashin daidaituwa na jiki ya bayyana. Jami’ai sun fara fitar da takardun tambayoyi domin samun kudi a wasu kwanaki kafin a fara jarabawar, inda ‘yan kasuwa marasa kishi, dillalai, da malalata dalibai suka lalata shirin. Wannan ya gurgunta kyawawan manufofin WAEC da ta bada fatawa da kuma kawo cikas ga ingancin takaddun shaida. Abubuwan da suka faru na baya-bayan nan sun kara jaddada lalacewar tsarin ilimin kasar. Kusan wata guda da fitowar WASSCE, matsalar tsara JAMB ta tilasta wa dubban daliban UTME a jihohi shida da wasu sassan Legas yin jarrabawar bayan an basu maki kadan. Wannan abin takaici ya sa wata daliba da abin ya shafa ta kashe kanta...
Albarkacin cika shekaru 55 da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Italiya, an shirya bikin kaddamar da shirin talibijin mai taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” da CMG ya gabatar, a jiya Laraba a birnin Rome, hedkwatar kasar Italiya. Za a fara watsa wannan shiri a kafofin yada labarai na kasar fiye da 30. An dauki da kuma tsara wannan shiri ne a garin Zhengding na lardin Hebei da Xiamen na lardin Fujian da Hangzhou na lardin Zhejiang da kuma Dunhuang na lardin Gansu da sauran wuraren da Xi Jinping ya taba kai rangadi ko aiki a can, don yin karin haske kan kokarin da Sin take yi wajen zakulo mafarin al’adun Sinawa, da kiyaye kayayyakin al’adu da sauran...
Yanzu sun sake nuna sha’awarsu, suna fatan ɗaukar ɗan wasan mai shekaru 28. Manchester United ma ta nuna sha’awar ɗaukar Ndidi idan har ta sayar da Casemiro, wanda ake raɗe-raɗin zai koma Saudiyya. A watan Janairu, Monaco da ke gasar Ligue 1 ta yi ƙoƙarin ɗaukar Ndidi, amma Leicester ta ƙi amincewa. Hakazalika, akwai ƙungiyoyi daga Saudiyya da ke son ɗaukarsa kuma suna shirin ba shi albashi mai tsoka, amma Ndidi yafi son ci gaba da buga wasa a Turai. Ndidi ya koma Leicester City a watan Janairun 2017 daga kulob ɗin Genk na Belgium. Ya lashe kofin FA Cup da Leicester a 2020, kuma ya zura ƙwallaye 11 a cikin wasanni 252 da ya buga wa ƙungiyar cikin shekaru...
Iyalan mafarauta 16 ’yan Jihar Kano da aka yi wa kisan gilla a garin Uromi da ke Jihar Edo sun yi zargin cewa gwamnati ta yi watsi da su. Wasu daga cikin waɗanda suka tsallake rijiya da baya a harin da kuma iyalan waɗanda aka kashe, sun bayyana cewa alƙawarin kuɗin magani da tallafi da kuma diyya fa gwamnatocin jihohin Edo da Kano suka yi musu bai wuce fatar baki ba. Ayarin farautan sun baro garin Fatakwal na Nijar Ribas ne, a hanyarsu ta komawa gida domin bikin Ƙaramar Sallah, amma wasu ’yan banga a Uromi suka tare su, suka yi musu kisan gilla. Akasarin mafarautan sun fito ne daga yankin Toronkawa da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure ta Jihar Kano,...

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28
Daga ranar 18 zuwa 21 ga watan nan bisa agogon Rasha, an gudanar da dandalin tattaunawa tattalin arziki na kasa da kasa na St. Petersburg karo na 28 a kasar ta Rasha. Yayin taron, an sake gayyatar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG don halartar dandalin a matsayin abokin huldar yada labarai. CMG, ya gina wani wurin baje koli mai zaman kansa a cikin wurin taron, da kafa dakin nuna shirye-shirye, da yin hira da manyan baki, kuma ya ba da rahotanni game da dandalin a cikin harsuna da yawa. Ban da wannan kuma, a yankin baje kolin, an nuna sabon sakamakon aikace-aikacen fasahohin zamani na AI, wanda CMG ya yi nazari da kansa, da...
Manyan kungiyoyin kwallon kafa a Turai Tottenham Hotspur da West Ham United na fafatawa wajen ganin sun dauki tauraron dan wasan Nijeriya dake buga kwallo a Club Brugge, Raphael Onyedika, ana alakanta Onyedika da barin kungiyar Club Brugge sakamakon rawar gani da ya taka a bana. Dan wasan na Nijeriya ya samu dimbin masu sha’awar raba shi da Brugge saboda bajintar da ya nuna a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta bara, a cewar Transferfeed, kungiyoyin biyu na son siyan dan wasan tsakiyar a wannan bazarar, West Ham na son ya maye gurbin Tomas Soucek dan kasar Czech, wanda ke kan hanyarsa ta barin kungiyar. Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6 Diaz Ba Na...
“An yi hasashen matsakaicin hadarin ambaliya ga al’ummomi 445 a cikin kananan hukumomi 116 daga Afrilu zuwa Yuni, 1,458 a kananan hukumomi 271 daga Yuli zuwa Satumba, da kuma 1,473 a kananan hukumomi 171 tsakanin Oktoba da Nuwamba,” in ji Ministan. Matakan aiki Da yake magana da wannan dan jarida, Shugaban Tsangayar Kimiyyar Muhalli na Jami’ar Jihar Nasarawa dake Keffi, Dokta Kante Pkantisawa, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su mai da hankali sosai kan hasashen yanayi da hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NiMET) da NHSA suka yi. Ya ce, “Ambaliyan da aka yi a Mokwa babbar tunatarwa ce game da tasirin sauyin yanayi da kuma bukatar daukar matakan da suka dace, babu wata fa’ida da ya wuce a ce...
Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya buƙaci Donald Trump kada ya ɗauki matakin soji kan Iran, yana mai kiran da a biyo wa lamarin ta hanyar lalama. Mista Starmer ya ce akwai “mummunan hatsarin bazuwar” yaƙin, inda ya yi kira ga duka ɓangarorin sun rungumi sulhu. Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe Ya ƙara da cewa a baya an samu “jerin tattauna masu yawa da Amurka, kuma ina ganin wannan ita ce hanyar warware matsalar.” Kalaman nasa na zuwa ne yayin da sakataren harkokin wajensa, David Lammy ke shirin ganawa da takwaransa na Amurka, Marco Rubio kan yadda za a taƙaita bazuwar yaƙin....
Ta hanyar inganta manufar yafe harajin kwastam a kai a kai, kasar Sin ta samar da yanayin kasuwanci mai karko a kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin tana kallon manufofinta na rangwame a matsayin matakan tabbatar da burin samun ci gaba, inda take kokarin kyautata tsarin cinikayyar waje na kasashen Afirka, da kuma ba da goyon baya wajen raya masana’antu, da habaka tsare-tsaren tattalin arziki a Afirka. Dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tabbatar da ci gabanta da kasashen Afirka na bai daya, shi ne domin ra’ayinta game da dangantakar dake tsakaninta da Afirka, wato al’ummar Sin da Afirka suna da makomar bai daya a nan gaba. A ganin kasar Sin, ita da Afirka suna da tarihi...
Ga cibiyoyin CBT, Oloyede ya ce dole ne a gargadi wadanda ke da hannu sannan a nemi su sanya hannu kan takardar yarjejeniya. Kuma bayan yarjejeniyar, za a kuma buƙaci su ba da shaidar horar da masu rajistar daliban. Da yake karin haske kan shawarwarin, Oloyede ya ce hukumar ba za ta yi la’akari da duk wani uzuri ba daga cibiyoyin da abin ya shafa a nan gaba ba, duk da ikirarin da suke yi na rashin sani, don haka akwai bukatar su samu horon da ya dace a jami’o’in gwamnatin tarayya da ke kusa da su kafin JAMB ta kara amincewa da su. Cibiyoyin CBT da abin ya shafa da aka gayyata taron sun hada da Misau...

Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun yi bayani kan sabon salon mayar da martani kan Isra’ila a harin ‘Alkawarin Gaskiya na 3″ Ma’aikatar hulda da jama’a ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin jiya Asabar ta sanar da cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage masu saukar ungulu a matsayin mayar da martani ga sabon farmakin da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan Iran. A cikin wata sanarwa da ma’aikatar hulda da jama’a ta IRGC ta fitar ta bayyana cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC...
Ministan harkokin wajen Omani Badr Albusaidi ya sanar da cewa, ba za a gudanar da zagaye na shida na tattaunawar nukiliya tsakanin Iran da Amurka ba. Yau Lahadi ne aka shirya gudanar da zagaye na gaba na shawarwari a Muscat babban birnin kasar Oman. A cikin wani sakon da ya wallafa a kan X (tsohon Twitter), Albusaidi ya tabbatar da sokewar, yayin da ya jaddada cewa “diflomasiyya da tattaunawa sun kasance hanya daya tilo ta samun zaman lafiya mai dorewa.” “Tattaunawar Iran da Amurka, wadda aka shirya gudanar da ita a birnin Muscat ranar Lahadin nan, ba za ta gudana a yanzu ba. Tattaunawar diflomasiyyar da aka faro kan shirin nukiliyar Iran, a watan Afrilu a shiga tsakanin masarautar Oman,...
Da yake nasa jawabin, Sangare ya ce, Nijar na bin manufar Sin daya tak a duniya, kuma tana ba da fifiko ga hadin gwiwarta da kasar Sin, da mayar da hankali sosai kan harkokin tsaro, kana tana son kara amincewa da juna, da ci gaba da yin shawarwari bisa mutunta juna a tsakaninsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Mataimakin firaministan Sin He Lifeng, ya gana da babbar ministar kudin Birtaniya Rachel Reeves jiya Lahadi a birnin Landan, inda suka zurfafa musaya game da batutuwan da suka shafi tattalin arziki da hadin gwiwa a fannin hada-hadar kudade, da sauran batutuwan dake janyo hankulan kasashensu. He, wanda kuma shi ne ya jagoranci tawagar kasar Sin a tattaunawar tattalin arziki da harkokin cinikayya tsakanin Sin da Birtaniya, ya ce kamata ya yi kasashen biyu su yi aiki tare, wajen aiwatar da muhimman kudurori da shugabannin kasashen suka cimma, su kuma ingiza nasarar dandalin tattalin arziki da cinikayya na Sin da Birtaniya, da zurfafa musaya da hadin gwiwa a dukkanin sassan tattalin arziki da cinikayyarsu, da ingiza cimma moriya tare, da wanzar...

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
A ‘yan kwanakin da suka gabata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da masu masana’antu da ‘yan kasuwa na kasa da kasa, inda ya karfafa musu gwiwar kara gudanar da harkokinsu da zuba jari a kasar Sin. Roland Busch, shugaban kwamitin darektoci na kamfanin Siemens yana daya daga cikin baki mahalarta ganawar. A yayin da yake zantawa da wakiliyar CMG, ya bayyana cewa, shugaba Xi da kansa ya halarci ganawar, wanda ya isar da sakon cewa, kasar Sin za ta kara bude kasuwarta, da maraba da kamfanonin kasashen waje da su gudanar da kasuwanci da zuba jari a kasar, lamarin da ya burge kowa da kowa kwarai da gaske. Roland Busch ya jaddada cewa, kamfaninsa bai taba yin...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Gidauniyar ta kuma kai ziyara fadar Hakimin Mokwa, Alhaji Muhammed Aliyu Shaaba, inda wakilan fadar suka yi maraba da tawagar wakilan gidauniyar tare da jinjina taimako da goyon bayan da aka nuna musu a wannan hali da suke ciki na ibtila’i. Kamar yadda Babban daraktan yankin, Musa Aliyu ya bayyana, gidauniyar Dr. Abubakar Bukola Saraki ta kai taimakon kuɗi domin tallafawa waɗanda suka tsira da masu taimaka musu. Sannan ya yi kira ga ƙungiyoyi masu zaman kansu da ɗaiɗaikun mutane da su taimakawa al’ummar garin Mokwa. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a...
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta shirya tsare-tsaren tsaro domin ganin an yi Sallar Idi cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya. Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa za a tura ’yan sanda da sauran jami’an tsaro zuwa filayen Idi, Masallatai, da wuraren taro domin kula da tsaro da zirga-zirgar jama’a. Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano Za a sanya ido sosai a manyan hanyoyi musamman waɗanda ke kai wa zuwa wuraren sallah, domin rage cunkoso da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a. An ware ƙofofin shiga da fita a filayen Sallah domin a riƙa duba mutane da kayan da suke ɗauke da...
An gano gawar yara bakwai a yankin Mokwa, da ke Jihar Neja, bayan ambaliyar ruwa da ta afka wa garin mako guda da ya wuce. Yawan adadin waɗanda suka rasu kawo yanzu ya kai mutum 160, amma wasu jami’ai sun ce za a iya gano gawar sama da mutum 200. Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda Ambaliyar ta kuma tafi da motar haya mai kujeru 18 ɗauke da fasinjoji. Kawo yanzu, bayan kwana shida da faruwar ambaliyar, ba a ga motar ko wani daga cikin fasinjojin ba. Wani mazaunin garin, Baba Abu, ya ce: “Direban bai nemi ƙetare ruwan ba. Ya...
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, a gidansa da ke Legas. Wannan ganawar na cikin ƙoƙarin warware rikicin siyasa da ya addabi jihar. Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano Fubara, ya samu saɓani da ubangidansa na siyasa, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bayan hauwansa mulki. Saɓani kan ikon mallakar kuɗin jihar da naɗin muƙamai ya janyo rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin jihar da kuma majalisar dokokin jihar. A watan Maris 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa, da kuma ‘yan majalisar dokokin jihar baki ɗaya. Ya naɗa...
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, a yau Talata ya yi watsi da ikirarin da Amurka ta yi na cewa kasar ta Sin na karya yarjejeniyar da aka cimma a tsakanin kasashen biyu a tattaunawar tattalin arziki da kasuwanci da aka yi a Geneva, inda ya bukaci Amurka da ta daina yada labarun kanzon kurege. A yayin taron manema labarai na yau da kullum, Lin ya bayyana cewa, kasar Sin ta dauki matakin da ya dace, tare da daukar yarjejeniyar da aka cimma a shawarwarin Geneva da muhimmanci, tare da aiwatarwa yadda ya kamata. Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan...
Ofishin shugaban kasar Turkiya, ya bayyana fatan cewa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya a birnin Istanbul, za ta kai ga tsayar da tsagaita budewa juna wuta wanda kuma zai ga, kawo karshen yakin baki daya. Ofishin shugaban kasar Turkiya ya bayyana haka a yau Talata, ta kuma kara da cewa,; Tattaunawar da aka gudanar a jiya Litinin a tsakanin Rasha da Ukiraniya a kuma fadar shugaban kasar Turkiyya dake birnin Istanbul tana cike da fata na tsayar da yakin. Kamfanin dilalncin labarun “Sputnik” na kasar rasha ya ambato majiyar fadar shugaban kasar ta Turkiya tana cewa; Shakka babu duk wata tattaunawa da bangarori za su zauna akan teburi, tana tattare da kyakkyawan fata, a dalilin haka,...

Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Tsibiran guda uku na Tunb Babba da Tunb Karami da Abu Musa yankuna ne Iran Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da ikirari da kungiyar hadin kan kasashen Larabawan yankin tekun Fasha (PGCC) ta yi dangane da tsibiran Iran guda uku, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta dauki dukkan matakan da suka dace don tabbatar da tsaro da muradun kasar a cikin tsibiran guda uku. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da yin watsi da ikirarin da ke kunshe a cikin bayanin karshe na taron ministocin harkokin wajen kasashen yankin tekun Fasha karo na...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Darakta-Janar Na Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya
Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da Grossi kan sabbin abubuwan da suka shafi tattaunawar nukiliyar Iran Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi da Darakta Janar na Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya Rafael Grossi sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da suka shafi tattaunawar nukiliya da kuma dage takunkumin da aka kakabawa Iran a wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho. A yayin tattaunawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan sabon ci gaban da aka samu a shawarwarin nukiliyar da kuma dage takunkumin. Sun kuma tattauna rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar kan Iran. Haka nan kuma yayin da yake ishara da yadda Iran ke ci gaba da ba da hadin kai ga hukumar ta IAEA, da aiwatar da...
Iran ta tabbatar da cewa ta samu shawarar da Amurka ta gabatar mata daga hannun kasar Oman game da shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya da ake tattaunawa a kai. Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa Iran ta samu wani bangare na shawarwarin daga Amurka daga Oman mai shiga tsakani kan batun a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X. Ya karbi sakon ne daga hannun takwaransa na Oman Badr Albusaidi, wanda ya gudanar da wata gajeriyar ziyara a Tehran. Saidai ministan harkokin wajen Iran din bai bayyana abinda shawarwarin ke kunshe da ba, amma ya jaddada cewa za a duba su a kuma mayar da amsa wacce ta yi daidai da muradin...
“Gane amfanin lamarin da ya shafi ilimi shi yasa, Gwamna Lawal ya kaddamar da dokar ta baci a bangaren ilimi a watan Nuwamba 2023,matakin da aka dauka an yi sa’a ya haifar da da mai ido a bangaren ilimi a Jihar Zamfara. “Fiye da makarantu 500 aka y masu kwaskwarima da samar masu abubuwan da suka kamata tun lokacin da aka kaddamar da dokar ta bacin.An horar da Malaman makarantun gwamnati,ana kuma ci gaba dayin hakan. “Saurin biyan kudaden bashi da Hukumomin WAEC da NECO ya kawo kwanciyar hankali ga daliban da suka kammala makaranta da rubiuta jarabawa, sai dai basu samu ci gaba da karatu ba saboda Hukumomin jarabawar sun rike masu sakamakon jarabawar da suka yi. Daga...
An gano gawar wani direban da yake tuƙi ƙarƙashin kamfanin sufuri da har yanzu ba a tantance shi ba a yankin Samphino na Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa. Daily Trust ta ruwaito cewa, an gano gawar direban matashin mai matsakaicin shekaru da sanyin safiyar Juma’a a cikin motarsa a mahaɗar Samphino da ke unguwar Kpansia a unguwar Yenagoa. Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA Faransa ta haramta shan sigari a cikin jama’a Wasu shaidun gani da ido da mazauna wurin da suka gano mutumin a wurin, an bayyana cewa, sun sanarwa da jami’an tsaro lamarin inda suka yi gaggawar ɗaukar mataki a wajen tare da killace wurin. Mazauna yankin sun ce mai yiwuwa wasu...
Daga baya, hukumar WAEC ta fitar da sanarwa tana mai bada hakuri, inda ta ce wasu ƙalubale ne suka hana isar da kayayyakin jarrabawa akan lokaci. Wannan lamari ba sabon abu ba ne, domin a watan Afrilu, LEADERSHIP ta ruwaito cewa wasu masu rubuta jarrabawar UTME sun bar gida da asuba domin isa cibiyoyin jarrabawa kafin ƙarfe 6:30 na safe, ba tare da wadataccen tsaro ko sufuri ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp