Ministan harkokin wajen kasar Iran yayi Allah wadai da harin da aka kai kan ginin ofishin jakadancin kasarsa da ke Stockholm na kasar sweden

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da harin da aka kai ofishin jakadancin Iran da ke Stockholm tare da yin kira ga gwamnatin Sweden da ta dauki mataki mai tsanani kan wadanda suka kai harin.

A yayin wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da ministar harkokin wajen Sweden Maria Malmer Stenergård, bangarorin biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma na ofishin jakadancin.

A yayin tattaunawar, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da harin da aka kai ofishin jakadancin Iran da ke Stockholm tare da yin kira ga gwamnatin kasar Sweden da ta dauki mataki mai tsanani kan wadanda suka aikata wannan lamari tare da daukar matakan da suka dace don hana sake aukuwar lamarin.

Araghchi ya kuma bayyana dangantakar dake tsakanin Tehran da Stockholm tare da jaddada bukatar yin zurfafa tuntuba domin warware rashin fahimtar juna da inganta hadin gwiwar kasashen biyu.

A nata bangaren, ministar harkokin wajen kasar Sweden ta jaddada aniyar kasarta na kare cibiyoyin diflomasiyyar Iran, tana mai jaddada cewa Stockholm za ta dauki matakan da suka dace don tabbatar da tsaron ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen kasar Sweden

এছাড়াও পড়ুন:

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A yau Alhamis, kwamitin fasahar lantarki na kasa da kasa wato IEC, ya gabatar da ka’idar kasa da kasa ta fasahar sadarwar 5G, wadda za ta ingiza harkokin masana’antu, wato ka’idar amfani da fasahar sadarwa ta 5G a intanet na masana’antu.

Kasashen Sin da Jamus ne suka fitar da wannan ka’ida ta hadin gwiwa, kuma masana daga kasashen Amurka, da Faransa, da Japan da dai sauransu, sun yi nazari, da gabatar da ka’idar cikin hadin gwiwa, wadda ta cike gurbin kasa da kasa a fannin ka’idar da za su bi, wajen amfani da fasahar sadarwar ta 5G a harkokin masana’antu.

Wannan ka’ida ta mayar da hankali kan yadda za a daidaita tsarin intanet na 5G, da kiyaye intanet na 5G a lokacin da ake gudanar da ayyukan masana’antu, tare da samar da samfurori da dama, game da yadda za a hada fasahar sadarwar 5G da harkokin masana’antu. Haka kuma, ka’idar ta dace da dukkanin ayyukan dake shafar tsari, da ginawa, da kuma kyautata tsarin sadarwar 5G a ayyukan masana’antu.

Gabatar da wannan ka’ida ta nuna cewa, kasar Sin ta samu gagarumin ci gaba, da sakamako a fannin daidaita ayyukan masana’antu da fasahar 5G, tare da gabatar da dabarar kasar Sin ga sassan kasa da kasa, a fannin aiwatar da kwaskwarima a harkokin masana’antu na dijital. (Mai Fassara: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki November 5, 2025 Daga Birnin Sin Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka November 5, 2025 Daga Birnin Sin Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • Tarayyar Afirka Ta Yi Kiran Da A Girmama ‘Yancin Kai Na Najeriya Da Rashin Tsoma Baki A Harkokin Gidanta
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro