Ministan harkokin wajen kasar Iran yayi Allah wadai da harin da aka kai kan ginin ofishin jakadancin kasarsa da ke Stockholm na kasar sweden

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da harin da aka kai ofishin jakadancin Iran da ke Stockholm tare da yin kira ga gwamnatin Sweden da ta dauki mataki mai tsanani kan wadanda suka kai harin.

A yayin wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da ministar harkokin wajen Sweden Maria Malmer Stenergård, bangarorin biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma na ofishin jakadancin.

A yayin tattaunawar, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da harin da aka kai ofishin jakadancin Iran da ke Stockholm tare da yin kira ga gwamnatin kasar Sweden da ta dauki mataki mai tsanani kan wadanda suka aikata wannan lamari tare da daukar matakan da suka dace don hana sake aukuwar lamarin.

Araghchi ya kuma bayyana dangantakar dake tsakanin Tehran da Stockholm tare da jaddada bukatar yin zurfafa tuntuba domin warware rashin fahimtar juna da inganta hadin gwiwar kasashen biyu.

A nata bangaren, ministar harkokin wajen kasar Sweden ta jaddada aniyar kasarta na kare cibiyoyin diflomasiyyar Iran, tana mai jaddada cewa Stockholm za ta dauki matakan da suka dace don tabbatar da tsaron ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen kasar Sweden

এছাড়াও পড়ুন:

Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan

Al’ummar Japan na gudanar da bikin tunawa da ranar harin Nagasaki da ya faru shekaru 80 da suka gabata, wani hari da ke zama irinsa na farko kuma mafi muni da duniya ta taba gani.

Tarihi ya nuna cewa Amurka ce ta fara harba makamin Nukiliya a garin na Nagasaki kwanaki uku bayan na garin Hisroshima a wani ɓangare na dakatar da yaƙin duniya na biyu.!

Harin na ranar 9 ga watan!!!!!!!mutane dubu 70 a take bayan mutane 140 da suka mutu kwanaki uku da suka gabata a harin na Hiroshima.

An yi ittifakin cewa wannan shine harin da ya tilastawa Japan miƙa wuya a ranar 15 ga watan Agustan wannan shekarar, matakin da ya kawo ƙarshen yaƙin.

Bayanai sun ce a yau mutane sama da 2,600 daga ƙasashe sama da 90 sun halarci taron tunawa da wannan rana a bikin da aka gudanar da filin taro na garin Nagasaki.

Firai ministan ƙasar Shigeru Ishiba ya fara buɗe taron da jawabi da misalin ƙarfe 11:02 dai-dai lokacin da makamin ya dira a garin, a wani ɓangare na girmama waɗanda suka rasa rayukansu, kafin !bisani kuma aka rika kaɗa ƙarararwa don tunawa da ruhinsu.

An saki gwamman tattabaru da ke alamta zaman lafiya bayan da shugaban ya kammala jawabi, inda ya ce wannan taro ya shiga cikin kundin tarihin ƙasar wanda za’a gajeshi ƴaƴa da kakanni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza
  • Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi
  • Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
  • Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu
  • Araqchi: Hari Kan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyar Kasar Iran Ba Zai Taba Canza Matsayinta Ba
  • Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Wutar Lantarki Ta Kasa
  • Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano