Aminiya:
2025-08-09@16:22:05 GMT

Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita

Published: 9th, May 2025 GMT

Wasu kananan yara biyar sun mutu a cikin wata mota da aka yi watsi da ita a harabar wani gida a yankin Agyaragu da ke Karamar Hukumar Obi da ke Jihar Nasarawa.

Yaran sun rasu ne a sakamakon daukewar nunfashinsu a cikin motar, lamarin da ya jefa mazauna yakin yankin, wadanda yawancinsu manoman ne, daga kabilu daban-daban, cikin alhini.

An gano gawarwakinsu ne da misalin karfe 1 na rana a cikin motar bayan mutanen yankin sun shafe tsawon lokaci ana neman su.

Misis Ifeoma Nnaji, wacce ta rasa ’ya’yanta biyu, Nmesoma da Chidima, ta bayyana yadda aka gano gawarwakin ta ce, “Mun duba ko’ina… Daga karshe, wani ya ba da shawarar mu duba motar da aka yi watsi da ita, kuma a can muka same su, babu rai,” in ji ta cikin kuka.

Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci Masana sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas

Ta bayyana cewa motar ta dade da ajiye a gidansu kuma a kullum a kulle take.

Misis Bridget Iormagh, kakar Eunice Shapera mai shekaru biyar, ta bayyana bakin cikinta, ta ce, “A kullum tana kusa da kofar gidana… Amma a wannan ranar, Eunice ta bi sauran yaran suka tafi wasa.” Wani makwabci ne ya gano yaran a cikin motar da aka yi watsi da ita.

Wannan mummunan lamari shi ne irinsa na uku da ya faru a Jihar Nasarawa a ’yan shekarun nan, inad a watan Agustan shekarar 2013, wasu biyu sun mutu a watan Agustan 2019 a Keffi.

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta mika sakon ta’aziyyarta ga iyalan wadanda suka rasa ’ya’yansu. Mataimakin Gwamna Dakta Emmanuel Akabe ya jagoranci tawagar da ta kai ziyarar ta’aziyya ga yankin, inda ya bayyana lamarin a matsayin “mai karya zuciya da kuma bakin ciki.”

Ya kuma yi kira ga iyalan da su dauki wannan babban rashin a matsayin kaddara daga Allah.

Kakakin ’yan sanda na Jihar Nasarawa, SP Ramhan Nansel, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce sun samu rahoton ne da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Lahadi.

Ya kara da cewa an tabbatar da mutuwar yaran a Asibitin Aro sakamakon shakewar numfashi, kuma an fara cikakken bincike don gano yadda yaran suka samu shiga motar.

Hukumomi na kira ga iyaye da masu ababen hawa da su kara kula da ’ya’yansu da kuma tabbatar da cewa yara ba za su iya shiga motocin da aka ajiye ko kuma aka yi watsi da su ba, domin kauce wa irin wannan bala’i a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: aka yi watsi da ita Nasarawa da aka yi watsi da ita Jihar Nasarawa a cikin motar

এছাড়াও পড়ুন:

Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da biyan sama da biliyan ɗaya a matsayin kuɗin garatitu ga iyalan ma’aikatan gwamnati 445 da suka rasu.

Wannan biyan zai shafi tsoffin ma’aikatan jihar, ma’aikatan wucin-gadi, ma’aikatan ƙananan hukumomi, da malaman firamare.

Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara 

Ana sa ran biyan kuɗin zai fara daga kan watan Disamba 2024 zuwa Maris ɗin 2025.

Gwamna Idri, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da walwalar ma’aikata da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen yi wa jihar hidima.

Ya ce biyan haƙƙoƙin ma’aikata ba wasa ba ne, kuma gwamnatinsa za ta yi tsayin daka wajen ganin an biya su a kan lokaci.

Wasu tsoffin ma’aikata sun yaba da wannan mataki, amma sun roƙi gwamnan da ya ci gaba da biyan sauran waɗanda ba su shiga jerin wannan sahun ba.

Sun ce akwai ɗimbin masu jiran haƙƙinsu, kuma idan ana biyan kowa a hankali, cikin lokaci kaɗan za a rage yawan masu jiran kuɗi.

Sun kuma buƙaci gwamnati ta duba tsarin fansho na jihar don inganta shi.

A cewarsu, yawancin masu karɓar fansho a Kebbi na cikin halin ƙunci saboda kuɗin da ake ba su ba ya wadatarwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi
  • Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Tataba