Aminiya:
2025-06-24@13:16:22 GMT

Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita

Published: 9th, May 2025 GMT

Wasu kananan yara biyar sun mutu a cikin wata mota da aka yi watsi da ita a harabar wani gida a yankin Agyaragu da ke Karamar Hukumar Obi da ke Jihar Nasarawa.

Yaran sun rasu ne a sakamakon daukewar nunfashinsu a cikin motar, lamarin da ya jefa mazauna yakin yankin, wadanda yawancinsu manoman ne, daga kabilu daban-daban, cikin alhini.

An gano gawarwakinsu ne da misalin karfe 1 na rana a cikin motar bayan mutanen yankin sun shafe tsawon lokaci ana neman su.

Misis Ifeoma Nnaji, wacce ta rasa ’ya’yanta biyu, Nmesoma da Chidima, ta bayyana yadda aka gano gawarwakin ta ce, “Mun duba ko’ina… Daga karshe, wani ya ba da shawarar mu duba motar da aka yi watsi da ita, kuma a can muka same su, babu rai,” in ji ta cikin kuka.

Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci Masana sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas

Ta bayyana cewa motar ta dade da ajiye a gidansu kuma a kullum a kulle take.

Misis Bridget Iormagh, kakar Eunice Shapera mai shekaru biyar, ta bayyana bakin cikinta, ta ce, “A kullum tana kusa da kofar gidana… Amma a wannan ranar, Eunice ta bi sauran yaran suka tafi wasa.” Wani makwabci ne ya gano yaran a cikin motar da aka yi watsi da ita.

Wannan mummunan lamari shi ne irinsa na uku da ya faru a Jihar Nasarawa a ’yan shekarun nan, inad a watan Agustan shekarar 2013, wasu biyu sun mutu a watan Agustan 2019 a Keffi.

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta mika sakon ta’aziyyarta ga iyalan wadanda suka rasa ’ya’yansu. Mataimakin Gwamna Dakta Emmanuel Akabe ya jagoranci tawagar da ta kai ziyarar ta’aziyya ga yankin, inda ya bayyana lamarin a matsayin “mai karya zuciya da kuma bakin ciki.”

Ya kuma yi kira ga iyalan da su dauki wannan babban rashin a matsayin kaddara daga Allah.

Kakakin ’yan sanda na Jihar Nasarawa, SP Ramhan Nansel, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce sun samu rahoton ne da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Lahadi.

Ya kara da cewa an tabbatar da mutuwar yaran a Asibitin Aro sakamakon shakewar numfashi, kuma an fara cikakken bincike don gano yadda yaran suka samu shiga motar.

Hukumomi na kira ga iyaye da masu ababen hawa da su kara kula da ’ya’yansu da kuma tabbatar da cewa yara ba za su iya shiga motocin da aka ajiye ko kuma aka yi watsi da su ba, domin kauce wa irin wannan bala’i a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: aka yi watsi da ita Nasarawa da aka yi watsi da ita Jihar Nasarawa a cikin motar

এছাড়াও পড়ুন:

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Shugaban kwamitin hana kwacen waya da yaki da miyagun kwayoyi da fadace-fadacen daba da gwamnati Kano ta kafa a watanni 21 da suka wuce, Janaral Gambo Ahmed mai Addau mai ritaya, ya bayyana ce wa yanzu haka wannan kwamiti ya gano cibiyoyi 52 da ake aikata laifuka a daukacin Jihar Kano.

Ya kara da cewa yanzu haka bisa umarni da amincewar gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, wannan kwamiti ya dauki matasa 1,050 aiki, wanda kwamishinan harkokin tsaron cikin gida na Kano, Ibrahim Umar ya kaddamar a madadin gwamnan, domin hada hannu da jami’an ‘yansanda da na NDLEA da cibil defence, da na leken asiri da na farin kaya (DSS), da ‘yan bijilanti da sauransu, domin murkushe wannan mummuna aiki na fadan daba da kwacen waya da harkar miyagun kwayoyi a Kano.

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

Janar Mai Addau ya bayyana cewa yanzu haka gwamnatin Kano ta samar da motoci da ababan hawa don wannan aiki kimanin 100 da kuma alwashin bayar da duk abun da wadannan zaratan matasa ke bukata don yin wannan aiki na tsare lafiyar al’ummar Kano.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su
  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato