Aminiya:
2025-06-15@13:26:24 GMT

An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden

Published: 30th, January 2025 GMT

An harbe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani, Salwan Momika, ɗan asalin ƙasar Iraƙi mai shekaru 38, a gidansa da ke Södertälje, kusa da birnin Stockholm a Sweden.

A harbe shi lokacin da yake ƙoƙarin wallafa bidiyo a kafar TikTok.

Sarkin yaƙin Zazzau ya rasu ana tsaka da taro  Hisbah ta kama masoya kan yin aure ba tare da amincewar iyayensu ba

Salwan Momika, ya ƙone Al-Ƙur’ani a 2023 a wajen Babban Masallacin Birnin Stockholm, lamarin da ya jawo cece-ku-ce da zanga-zanga a ƙasashen Musulmi.

Lamarin ya haifar da rikicin diflomasiyya, ciki har da kai hari ofishin jakadancin Sweden da ke Bagdad, da kuma korar jakadan Sweden da ke Iraƙi.

A halin yanzu, ’yan sanda sun kama mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan, kuma suna ci gaba da bincike don gano musabbabin harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Salwan Momika

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara

Dakarun sojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu ’yan ta’adda yayin wani samame da suka kai garin Kunchin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.

A sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis, ta ce a ranar 10 ga watan Yuni ne rundunar FANSAN YAMMA ta kashe ƙasurguman ‘yan ta’addan da suka haɗa da Auta da Abdul Jamilu da kuma Salisu.

Leroy Sane ya koma Galatasaray Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu

“Waɗannan ’yan ta’adda suna da alaƙa da ayyukan tashin hankali da ta’addanci da ake yawan samu a yankin gaba ɗaya.

“Wannan farmakin dai na nuni da wani gagarumin koma baya ga masu aikata laifuka, wanda ke dagula zaman lafiya da tsaro a yankin,” in ji sanarwar.

Bayanan sirri na farko-farko sun nuna cewa an kashe ƙarin wasu shugabannin ’yan ta’adda, ciki har da wani da aka fi sani da Babaye a lokacin harin.

Kazalika, a wani lamarin daban, rahotanni sun ce an kashe Sale Ado Madele da aka fi sani da Sarki, babban ɗan shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru.

A wani lamarin mai kama da haka, sojojin sun kuma kashe wasu ’yan ta’adda goma da suka taru a kusa da wata tashar mai da ke garin Danjibga.

Ana kyautata zaton ‘yan ta’addan na cikin wani gungun hadin-gwiwa da Dogo Sule ya haɗa domin kai hari.

Rundunar sojojin Nijeriya ta ce tana ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da kuma maido da dauwamammen zaman lafiya a fadin Jihar Zamfara da yankin Arewa maso Yamma.

“Wannan aiki yana ƙara jaddada ƙudurinmu na wargaza hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda tare da gurfanar da masu aikata laifuka a gaban ƙuliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara