Aminiya:
2025-08-12@17:51:34 GMT

An kama matashi da kawunan mutanen a Legas

Published: 11th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ta cafke wani mutum mai suna Samson Oghenebreme a unguwar Odomola ɗauke da kawunan mutane.

Sanarwar da kakakin ’yan sandan Legas, Benjamin Hundeyin ya fitar, ta ce an kai kawunan da aka gano asibiti a Epe, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama

An kama matashin ne ɗan shekara 25 bayan da jami’an bijilanti da ke sintiri a yankin suka sanar da jami’an tsaro cewa ba su yadda da take-takensa ba.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa ’yan sandan sun yi zargin cewa matashin yana kai kawunan Jihar Edo wajen wani boka — wanda yake amfani da su don yin kuɗi.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Olohundare Jimoh ya yaba wa jami’an ’yan sanda da na bijilanti kan ɗaukar matakin da ya dace da sauri.

Ya kuma buƙaci duk mazauna jihar da su riƙa sa ido da kai rahoton abin da ba su yarda da shi ba zuwa ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Legas Kawunan mutane

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa

Hukumar tsaro ta sibil difens (NSCDC) ta sanar da cafke wani mutum, Salisu Muhammad, mai shekaru 45, bisa zargin kashe jami’inta, Bashir Adamu Jibrin, a kasuwar Shuwarin da ke Karamar Hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.

A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Muhammed Badarudeen ya fitar a Dutse, babban birnin jihar, lamarin ya faru ne a ranar kasuwa lokacin da marigayin yake gudanar da aikinsa.

Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya

Rahotanni sun nuna cewa, ana zargin Salisu ya buga wa jami’in dutse a kai, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.

Hukumar ta ce ta kama wanda ake zargin ne a gidansa da ke Shuwarin a ranar 7 ga watan Agusta, 2025.

Sai dai bayanai sun ce Salisu wanda bai cimma nasara ba yayi ƙoƙarin tserewa a yayin da ake jigilar sa zuwa hedikwatar NSCDC da ke Dutse a cikin motar jami’an tsaron.

Sanarwar ta ƙara da cewa, Salisu ya samu raunuka ne yayin da yake ƙoƙarin tserewa, kuma daga bisani aka kai shi babban asibitin Dutse, inda aka tabbatar da rasuwarsa sakamakon raunikan da ya samu.

Sai dai ’yan uwansa sun buƙaci cikakken bayani dangane da raunikan da ya samu har da dalilin rasuwarsa a asibitin Sambo Limited wanda aka garzaya da shi bayan ya yi yunƙrin tserewa daga mota da ke tafe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Kwastam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
  • Hukumar Kwatsam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas