HausaTv:
2025-11-27@22:00:14 GMT

Kungiyar Kurdawan Turkiya Za Ta Ajiye Makamanta Na Yaki

Published: 12th, May 2025 GMT

 Kungiyar Kurdawan Turkiya PKK ta sanar da cewa za ta ajiye makamanta ta kuma rusa kanta.

Kamfanin dillancin labarum “Furat” mai kusanci da kungiyar ta PKK, ya nakalto cewa; Kungiyar ta yanke zartar da wannan matakin ne a yayin taron da ta yi kaso na 12 da ta yi kwanaki kadan da su ka gabata.

Sanarwar ta PKK ta kuma kunshi cewa;Jam’iyyun siyasa na kurdawa za su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansa domin bunkasa tsarin demokradiyya da sake gina al’ummar Kurdawa.

Haka nan kuma PKK ta ce, da akwai alakar a sake Shata salon alakar Kurdawa da Turkiya.

A martanin da jam’iyyar dake Mulki a Turkiya ta fitar, ta bayyana cewa;  Zartar da  matakin da kungiyar ta Kurdawa ta dauka na ajiye makamanta da kuma rusa kanta, da dukkanin rassanta, zai zama bude wani sabon shafi.

Kakakin jam’iyyar, Umar Jalik ya ce; Matakanin yana da matukar muhimmanci ga Turkiya, domin hakan yana nufin kawo karshen ta’addanci,kuma gwamnati za ta sa ido ta ga aiwatar da wannan matakin, kuma za a rika sanar da shugaba Rajab Tayyib Urdugan akan zartar da matakan.

Kungiyar dai ta PKK ta yi taronta ne a arewacin Iraki a ranakun 5 da 7 ga watan Mayu, bisa gayyatar jagoranta Abdullahi Ojlan da yake tsare tsawon shekaru 26 da su ka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano

Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.

Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Wani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.

Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.

Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.

Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Iran ta yi tir da matakin Australiya na alakanta IRGC, da mai tallafawa ta’addanci
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina