Iran Ta Musanta Zargin Kamfanin Dillancin Labaran Reuters Dangane Da Aikawa Rasha Makamai
Published: 11th, May 2025 GMT
Jakadan JMI a MDD ya musanta zargin kamfanin dillancin labaran reuters dangane da rotohonsa na cewa JMI tana aika makamai masu linzami zuwa kasar Rasah don taimakawa kasar Rasha yakin da take fafatwa da kasar Ukraine fiye da shekaru 3 da suka gabata.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto
Ofishin jakadancin JMI dake birnin NewYork ya kara da cewa, abin mamaki da kamfanin dilancin laraban reuters, shi ne ba wannan ne karo na farko yake yada labaran karya a duniya wanda wai yake samu daga wasu wadanda basa son a bayyana sunansu.
Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa bata bayan wani bangare daga cikin bangarori biyu da suke fafatawa a kasar Ukraine.
Don haka bata taba taimakawa kasar Rasha da makamai don yakar kasar Ukraine ba, kuma bata taba taimaka kasar Ukraine.
Ofishin jakadancin ya bayyana cewa ra’ayinta da so samu ne ta zama mai shiga tsakani don warware rikicin kasar ta Ukraine.
Amma reuters ya ci gaba da bada labaran karya wadanda suke cewa tana shirin aikawa kasar Rasha damdamalin cilla makamai masulinzami wadanda Iran ta aikawa kasar Rasa a Bara, kamar yadda Amurka take zargin hakan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bayyana Damuwarsa Da Makaman Nukliyar HKI A Sanda Ake Takura Mata
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana fuska biyu na kasashen yamma, dangane da shirin magakamashin nukliya na kasarsa, da kuma yadda basa magana kan makaman nukliya wanda HKI take da su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya Asabar, a birnin Doha na kasar Qatar a inda yake halattan taron JMI da kasashen larabawa a jiya Asabar.
Ministan ya kara da cewa, wannan rashin adalci ne a fili sannan nuna fuska biyu, Iran wacce babu tabbas kan shirinta na makamashin nukliya na soje ne, an cika duniya da cewa tana son ta mallaki makaman nukliya amma ga HKI wacce aka tabbatar da cewa tana da makaman na nukliya, babu magana a kan nata.
Aragchi ya kammala da cewa shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce, kuma babu wata anniya ta maida shin a kera makaman nukliya.