Aminiya:
2025-06-15@14:48:37 GMT

Ɓarayin dabobbi sun shiga hannu, an ƙwato awaki 85 a Gombe

Published: 30th, January 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar dabbobi.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Abdulkadir Tukur mai shekara 35 da Ibrahim Saidu mai shekara 20.

KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

An same su da tumaki 28 da awaki 57, jimillar dabbobi 85 da ake zargin da sato su.

An kama su ne a ranar 25 ga watan Janairu, 2025, bayan da Dagacin Tulmi a Ƙaramar Hukumar Akko, Abubakar Umar, ya kai wa ‘yan sanda rahoto.

Wani mafarauci mai suna Yayaji Muhammad ne ya tare su a garin Tulmi, inda suka kasa bayar da cikakken bayani kan dabbobin da ke tare da su.

Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce jami’an ofishin Pindiga sun karɓi rahoton tare da fara bincike.

Ya ce waɗanda ake zargi sun amsa laifinsu, kuma har yanzu an mayar masu dabbobin guda 25 daga cikinsu.

Daga cikin mutanen da aka mayar wa dabbobinsu akwai Joseph Ahmadu da aka mayar wa da awaki shida, Bello Sintali da ya samu awaki huɗu, Godwin Iro da aka mayar wa da awaki 10, da Zaraya Jepter da aka dawowa da awaki biyar.

Dukkaninsu sun fito ne daga Jurara yankin Kashere da wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomin Akko da Billiri.

Haka kuma, wasu mutum huɗu da ake zargi da hannu a satar dabbobin sun tsere.

Waɗanda suka tsere sun haɗa da Rabe Saidu, Hamisu Saidu, Bode Saidu, da Wada Saidu, dukkaninsu daga ƙauyen Dawo a Ƙaramar Hukumar Kwami.

’Yan sanda na ci gaba da ƙoƙarin kamo su tare da ƙwato sauran dabbobin da aka sace.

DSP Buhari Abdullahi, ya tabbatar wa jama’a cewa suna ci gaba da bincike, kuma dabbobin da aka sace suna hannun ’yan sanda a matsayin shaida.

Ya ce dukkanin waɗanda ake zargin za a gurfanar da su a kotu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, ya buƙaci jama’a su kasance masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi domin taimakawa wajen tabbatar da doka da oda a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi da ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

A wannan lokaci da wasu sassa ke kafa shingaye, GCI na gina gadoji. Manufar na kuma karfafa gwiwar tattaunawa, da gudanar da shawarwari tsakanin sassan duniya masu bambance-bambance, ta yadda za a kafa managarcin tsarin hadin kan bil’adama mai dorewa. GCI da ranar tattaunawa tsakanin wayewar kan kasa da kasa ta MDD, za su kara zamewa duniya muhimman manufofi na “tafiya tare a tsira tare”!(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha