Ɓarayin dabobbi sun shiga hannu, an ƙwato awaki 85 a Gombe
Published: 30th, January 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar dabbobi.
Waɗanda aka kama sun haɗa da Abdulkadir Tukur mai shekara 35 da Ibrahim Saidu mai shekara 20.
KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-RufaiAn same su da tumaki 28 da awaki 57, jimillar dabbobi 85 da ake zargin da sato su.
An kama su ne a ranar 25 ga watan Janairu, 2025, bayan da Dagacin Tulmi a Ƙaramar Hukumar Akko, Abubakar Umar, ya kai wa ‘yan sanda rahoto.
Wani mafarauci mai suna Yayaji Muhammad ne ya tare su a garin Tulmi, inda suka kasa bayar da cikakken bayani kan dabbobin da ke tare da su.
Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce jami’an ofishin Pindiga sun karɓi rahoton tare da fara bincike.
Ya ce waɗanda ake zargi sun amsa laifinsu, kuma har yanzu an mayar masu dabbobin guda 25 daga cikinsu.
Daga cikin mutanen da aka mayar wa dabbobinsu akwai Joseph Ahmadu da aka mayar wa da awaki shida, Bello Sintali da ya samu awaki huɗu, Godwin Iro da aka mayar wa da awaki 10, da Zaraya Jepter da aka dawowa da awaki biyar.
Dukkaninsu sun fito ne daga Jurara yankin Kashere da wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomin Akko da Billiri.
Haka kuma, wasu mutum huɗu da ake zargi da hannu a satar dabbobin sun tsere.
Waɗanda suka tsere sun haɗa da Rabe Saidu, Hamisu Saidu, Bode Saidu, da Wada Saidu, dukkaninsu daga ƙauyen Dawo a Ƙaramar Hukumar Kwami.
’Yan sanda na ci gaba da ƙoƙarin kamo su tare da ƙwato sauran dabbobin da aka sace.
DSP Buhari Abdullahi, ya tabbatar wa jama’a cewa suna ci gaba da bincike, kuma dabbobin da aka sace suna hannun ’yan sanda a matsayin shaida.
Ya ce dukkanin waɗanda ake zargin za a gurfanar da su a kotu.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, ya buƙaci jama’a su kasance masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi domin taimakawa wajen tabbatar da doka da oda a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi da ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
Rahotonni sun tabbatar da cewa: Da tsakar daren jiya Litinin wayewar garin yau Talata, sojojin mamayar Isra’ila dauke da motocin soji guda hudu da wasu sojoji masu tafiyar kafa sun kutsa cikin yankunan kasar Siriya daga titin Al-Hurriya, inda suka wuce titin Al-Kassarat, zuwa Talat Jabata Al-Khashab.
Majiyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Siriya ta bayyana cewa: Sojojin mayar sun kafa shingen binciken ababen hawa inda suka tsaya suna binciken ababan hawa da ke wucewa, sannan suka haska wuta don gano hanyar kafin su fita ta hanyar da suka shiga. Jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma suna shawagi a sararin samaniyar birnin Damascus fadar mulkin kasar ta Siriya.
A jiya Litinin ma, sojojin mamayar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wasu sansanoni na rundunar sojin ta 36 ta musamman da aka fi sani da Ain al-Burj a gabashin kauyen Qala’at Jandal da ke cikin karkarar birnin Damascus, tare da kafa wani sansanin soji a saman dutsen Barbar domin sa ido kan motsin da ake yi a yankin.