Aminiya:
2025-07-31@10:04:37 GMT

Ɓarayin dabobbi sun shiga hannu, an ƙwato awaki 85 a Gombe

Published: 30th, January 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar dabbobi.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Abdulkadir Tukur mai shekara 35 da Ibrahim Saidu mai shekara 20.

KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

An same su da tumaki 28 da awaki 57, jimillar dabbobi 85 da ake zargin da sato su.

An kama su ne a ranar 25 ga watan Janairu, 2025, bayan da Dagacin Tulmi a Ƙaramar Hukumar Akko, Abubakar Umar, ya kai wa ‘yan sanda rahoto.

Wani mafarauci mai suna Yayaji Muhammad ne ya tare su a garin Tulmi, inda suka kasa bayar da cikakken bayani kan dabbobin da ke tare da su.

Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce jami’an ofishin Pindiga sun karɓi rahoton tare da fara bincike.

Ya ce waɗanda ake zargi sun amsa laifinsu, kuma har yanzu an mayar masu dabbobin guda 25 daga cikinsu.

Daga cikin mutanen da aka mayar wa dabbobinsu akwai Joseph Ahmadu da aka mayar wa da awaki shida, Bello Sintali da ya samu awaki huɗu, Godwin Iro da aka mayar wa da awaki 10, da Zaraya Jepter da aka dawowa da awaki biyar.

Dukkaninsu sun fito ne daga Jurara yankin Kashere da wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomin Akko da Billiri.

Haka kuma, wasu mutum huɗu da ake zargi da hannu a satar dabbobin sun tsere.

Waɗanda suka tsere sun haɗa da Rabe Saidu, Hamisu Saidu, Bode Saidu, da Wada Saidu, dukkaninsu daga ƙauyen Dawo a Ƙaramar Hukumar Kwami.

’Yan sanda na ci gaba da ƙoƙarin kamo su tare da ƙwato sauran dabbobin da aka sace.

DSP Buhari Abdullahi, ya tabbatar wa jama’a cewa suna ci gaba da bincike, kuma dabbobin da aka sace suna hannun ’yan sanda a matsayin shaida.

Ya ce dukkanin waɗanda ake zargin za a gurfanar da su a kotu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, ya buƙaci jama’a su kasance masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi domin taimakawa wajen tabbatar da doka da oda a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi da ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga

Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya.

Yayin wata hira da Trust Radio, Onanuga ya ce maganar cewa ana yi wa Arewacin Najeriya wariya ba gaskiya ba ce, face tsantsar siyasa kawai.

Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Ya ce ƙorafin da Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta yi na cewa an yi watsi da Arewa wajen naɗe-naɗen muƙaman gwamnati da ayyukan ci gaba, wata dabara ce kawai don rage ƙimar shugabancin wanda ya fito daga Kudu.

Ya shawarci ’yan siyasar Arewa da su yi haƙuri, kamar yadda ɓangare Kudu ya yi lokacin mulkin marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya shugabanci ƙasar har na tsawon shekaru takwas.

“Shugaba Tinubu ɗan Najeriya ne kamar kowa. Ya cancanci yin shekaru takwas a kan mulki kamar yadda Buhari ya yi. Ka da mu lalata ƙasa saboda son zuciya,” in ji Onanuga.

Dangane da zargin cewa an fi bai wa ’yan Kudu muƙamai, Onanuga ya ce masu sukar Tinubu su kawo hujjoji da ƙididdiga maimakon su ci gaba da yin zargin da ba shi da tushe.

Ya ƙara da cewa babu wani yanki da ba shi da matsalar hanyoyi ko ayyukan da ba a kammala gama ba, amma ya ce gwamnatin yanzu na ƙoƙarin gyara abubuwan da ta gada.

“Kafin ku zargi gwamnati, sai ku binciki gaskiyar lamarin. Wannan duk siyasa ce kawai don a raina Shugaban Ƙasa,” in ji shi.

Onanuga, ya kuma kare matakin da Tinubu ke ɗauka wajen inganta tsaro.

Ya ce an samu ci gaba sosai, inda ya kafa misalin cewar dukkanin shugabannin tsaro daga yankin Arewa suka fito.

Ya ce yanzu yana iya yin tafiya daga Kaduna zuwa Abuja cikin kwanciyar hankali, tafiyar da a da ta ke da hatsari sosai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine