NUJ Jigawa Ta Nada Wakilin Rediyon Tarayya A Matsayin Mamba Na Musamman
Published: 14th, May 2025 GMT
Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Jigawa ta naɗa Kwamared Sani Muhammad Gumel da Kwamared Usman Mohammed Usman a matsayin mambobin majalisar kungiyar na musamman (Ex-Officio).
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakatariyar ta kungiyar, Kwamared Aisha Abba Ahmed, ta sanya wa hannu kuma ta rabawa manema labarai a Dutse.
Ta bayyana cewa, an yi waɗannan naɗe-naɗen ne a matsayin girmamawa da yabo ga jajircewarsu, ƙwarewa, da kuma gudummawar da suke bayarwa wajen haɓaka aikin jarida a Jihar Jigawa da ma ƙasa baki ɗaya.
Aisha Abba Ahmed ta ƙara da cewa, duka waɗannan mutane biyu sun dade suna nuna ƙwazo da biyayya ga manufofi da burin ƙungiyar.
Ta ce, ana sa ran waɗannan mambobin na musamman za su yi aiki kafada da kafada da majalisar, domin tallafa wa shirye-shiryenta, da bayar da shawarwari, da kuma ƙarfafa hulɗa da burin ƙungiyar a fadin jihar.
Ta ce, kungiyar ta buƙaci dukkan mambobi da su ba su haɗin kai da goyon baya wajen sauke nauyin da aka ɗora musu.
Sakatariyar ta ƙara da cewa, naɗin ya fara aiki nan take.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.
A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.
Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.
Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.
Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.
Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar
A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.
Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu
Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA