Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Jigawa ta naɗa Kwamared Sani Muhammad Gumel da Kwamared Usman Mohammed Usman a matsayin mambobin majalisar kungiyar na musamman (Ex-Officio).

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakatariyar ta kungiyar, Kwamared Aisha Abba Ahmed, ta sanya wa hannu kuma ta rabawa manema labarai a Dutse.

Ta bayyana cewa, an yi waɗannan naɗe-naɗen ne a matsayin girmamawa da yabo ga jajircewarsu, ƙwarewa, da kuma gudummawar da suke bayarwa wajen haɓaka aikin jarida a Jihar Jigawa da ma ƙasa baki ɗaya.

Aisha Abba Ahmed ta ƙara da cewa, duka waɗannan mutane biyu sun dade suna nuna ƙwazo da biyayya ga manufofi da burin ƙungiyar.

Ta ce, ana sa ran waɗannan mambobin na musamman za su yi aiki kafada da kafada da majalisar, domin tallafa wa shirye-shiryenta, da bayar da shawarwari, da kuma ƙarfafa hulɗa da burin ƙungiyar a fadin jihar.

Ta ce, kungiyar ta buƙaci dukkan mambobi da su ba su haɗin kai da goyon baya wajen sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sakatariyar ta ƙara da cewa, naɗin ya fara aiki nan take.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Wasan farko da Leicester za ta buga a gasar Championship zai kasance a gida, inda za ta kara da Sheffield Wednesday ranar Laraba, 10 ga watan Agusta mai zuwa.

A baya, Van Nistelrooy ya taɓa riƙe matsayin kocin riƙon ƙwarya na Manchester United, bayan da suka sallami Eric Ten Hag kafin su ɗauki Ruben Amorim daga Sporting CP ta ƙasar Portugal.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Mika Wuya Ga ‘Yan Kama Karya
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  • Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
  • Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum