Gwamnatin kasar Iran ta yi kakkausar suka ga gwamnatin HKI kan hare-haren da ta kaiwa wani sansanin yan gudun hijira a gaza inda ta kashe ko takai mutanen da dama ga shahada, daga ciki har da mata da yara jarirai.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei yana fadar haka a jiya Litinin, a jawabinda ta saba gabatarwa a ko wace litinin.

Esmaeil Baghaei ya kara da cewa nauyin MDD ce ta dakatar da kissan kiyashin da HKI take yi a Gaza, kuma kasa yin haka wani abin kunya ne ga majalisar.

Ya kuma kara da cewa ya zama wajini kutunan kasa da kasa wadanda suka hada da ICJ ta MDD da kuma ICC mai hukunta manya-manyan laifuka su yiwa shuwagabanin HKI sharia kan laifukan yakin da suke aikatawa a gaza fiye da shekara guda.

Tun ranar 7 gawatan Octoban shekara ta 2023 ne sojojin HKI suka fara kaiwa falasdinawa a Gaza hare-hare, ta sama da kasa, da manufar shafe kungiyar wacce take iko da yankin daga doron kasa da kuma kwace yankin gaza daga hannun Falasdinawa. Kuma ya zuwa yanzun sun kashe falasdinawa fiye da 56,000.

Wasu fiye da dubu 107 suka ji rauni. Banda haka tun kimani watanni biyu da suka gabata suna hana shigar da abinci zuwa cikin yankin wanda ya kai ga miliyoyin Falasdinawa a yankin suna fada cikin yunwa maitsanani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

Lee ya kara da cewa, fifikon musammam da Hong Kong ke da shi karkashin manufar “kasa daya mai tsarin mulki biyu’, ya ba yankin damar jan hankalin masu zuba jari na ketare domin su lalubo damarmakin kasuwanci a yankin da ma kasuwar babban yankin kasar Sin tare da taimakwa kamfanonin babban yankin shiga kasuwannin ketare.

 

Bugu da kari, ya ce kamfanonin waje da dama sun samu damarmakin kasuwanci a Hong Kong, kuma suna ci gaba da fadada harkokinsu. Su ma kamfanonin babban yankin kasar Sin sun aminta da karfin Hong Kong kuma suna hada gwiwa da tawagar dake Hong Kong wajen lalubo damarmakin dake akwai a kasuwanni masu tasowa na ketare. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya
  • Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar
  • Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa
  • Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen