Gwamnatin Netanyahu Tana Yi Wa Gwamnatin Trump Leken Asiri
Published: 13th, May 2025 GMT
Jaridar “Telegraph” da ake bugawa a Birtaniya ta buga labarin dake cewa; gwamnatin Benjamine Netanyahu ta bai wa kungiyar leken asiri ta waje, umarnin bin diddigin abubuwan da gwamnatin Amurka take yi a cikin sarari da boye.
Rahoton ya kuma kara da cewa; Netanyahu yana kokarin fahimtar abubuwan da gwamnatin Donald Trump take yi ne a boye, kuma menene manufofinta.
Da ma a baya, tashar talabijin din “Fox News” ta nakalto tsohon jami’in hukumar leken asirin HKI yana cewa; Donald Trump ya janye taimakon da yake bai wa Tel Aviv.
Har ila yau, jami’in na HKi ya ce; Tel Aviv tana cikin kidima saboda dalilai da dama da su ka hada da kasa sanin yadda za ta yi da Yemen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Indonesia: Tawagar Iran Tana Halartar Taron Majalisun Kungiyar Kasashen Musulmi
‘Hudu daga cikin ‘yan majalisar shawarar musulunci ta Iran sun isa birnin Jakarta na kasar Indonesia domin halartar taron majalisun kungiyar kasashen musulmi.
A yau Litinin ne dai aka bude taron majalisun kasashen kungiyar kasashen musulmi a birnin Jakarta na kasar Indonesia wanda shi ne karo na 19.
Taken da aka bai wa taron karo na 19 shi ne: “Kafa Gwamnatoci masu hikima a kuma cibiyoyi masu karfi a matsayin ginshikin jajurcewa.”
Tawagar ta Iran dai wacce Ruhullah Mutafakkir Azad yake jagoranta, ta kuma kunshi Sara Fallahi, Sayyid Yahya Sulaimani, da Muhammad Mahdi Shahriyari.
Taron zai ci gaba har zuwa ranar 15 ga watan nan na Mayu da ake ciki, kuma tawagar ta Iran za ta gabatar da jawabi a wurin taron, akan batutuwan da su ka shafi siyasa, al’adu, mata da iyali.
A yayin wannan taron za a tabo batun da ya shafi al’ummar Falasdinu da halin da suke ciki,musamman a yankin Gaza.
A gobe Talata kuwa shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran, Muhammad Kalibaf zai isar birnin na Jakarda domin halartar taron.