HausaTv:
2025-05-13@13:33:34 GMT

Gwamnatin Netanyahu Tana Yi Wa Gwamnatin Trump Leken Asiri

Published: 13th, May 2025 GMT

Jaridar “Telegraph” da ake bugawa a Birtaniya ta buga labarin dake cewa; gwamnatin Benjamine Netanyahu ta bai wa kungiyar leken asiri ta waje, umarnin bin diddigin abubuwan da gwamnatin Amurka take yi a cikin sarari da boye.

Rahoton ya kuma kara da cewa; Netanyahu yana kokarin fahimtar abubuwan da gwamnatin Donald Trump take yi ne a boye, kuma menene manufofinta.

Da ma a baya, tashar talabijin din “Fox News” ta nakalto tsohon jami’in  hukumar leken asirin HKI yana cewa; Donald Trump ya janye taimakon da yake bai wa Tel Aviv.

Har ila yau, jami’in na HKi ya ce; Tel Aviv tana cikin kidima saboda dalilai da dama da su ka hada da kasa sanin yadda za ta yi da Yemen.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Indonesia: Tawagar Iran Tana Halartar Taron Majalisun Kungiyar  Kasashen Musulmi

‘Hudu daga cikin ‘yan majalisar shawarar musulunci ta Iran sun isa birnin Jakarta na kasar Indonesia domin halartar taron majalisun kungiyar kasashen musulmi.

A yau Litinin ne dai aka bude taron majalisun kasashen kungiyar kasashen musulmi a birnin Jakarta na kasar Indonesia wanda shi ne karo na 19.

Taken da aka bai wa taron karo na 19 shi ne: “Kafa Gwamnatoci masu hikima a kuma cibiyoyi masu karfi a matsayin ginshikin jajurcewa.”

 Tawagar ta Iran dai wacce Ruhullah Mutafakkir Azad yake jagoranta, ta kuma kunshi Sara Fallahi, Sayyid Yahya Sulaimani, da Muhammad Mahdi Shahriyari.

Taron zai ci gaba har zuwa ranar 15 ga watan nan na Mayu da ake ciki, kuma tawagar ta Iran za ta gabatar da jawabi a wurin taron, akan batutuwan da su ka shafi siyasa, al’adu, mata da iyali.

A yayin wannan taron za a tabo batun da ya shafi al’ummar Falasdinu da halin da suke ciki,musamman a yankin Gaza.

A gobe Talata kuwa shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran, Muhammad Kalibaf zai isar birnin na Jakarda domin halartar taron.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Batun Zuba Hannun Jari A Amurka Ne Babbar Ajandar Ziyarar Shugaba Donald Trump Zuwa Kasashen Larabawan Yankin Tekun Pasha
  • Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
  • Sabuwar Gwamnatin Siriya Zata Kulla Kyakkyawar Alaka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  •  Indonesia: Tawagar Iran Tana Halartar Taron Majalisun Kungiyar  Kasashen Musulmi
  • Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
  • Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani  
  • Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670
  • Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta