Aminiya:
2025-05-22@06:42:28 GMT

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa

Published: 9th, May 2025 GMT

Wasu daliban jami’a da ke shirin tafiyar aikin yi wa kasa hidima NYSC sun rasu a wani harin da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne suka kai musu a yankin Gbarabtoru-Ekpetiama, Karamar Hukumar Yenagoa.

Matasan biyu da suka kammala karatunsu a Jami’ar Niger Delta (NDU), Amassomma, sun rasu ne bayan da gungun wasu mutane da ke wake-waken kungiyar asiri a cikin wata mota suka kai musu hari da adduna.

Kwamandan Kungiyar ‘Yan Banga (VGN) na Jihar Bayelsa,Tolummbofa Akpoebibo Jonathan ya ce, daya daga cikin samarin ya yi kokarin tserewa, amma maharan suka bi shi suka kama shi suka sassare shi.

Ya bayyana cewa da misalin karfe 11:00 na daren ranar Alhamis ne, abin ya faru kuma matasan biyu biyu sun mutu ne sakamakon raunukan da suka samu.

Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare An kama mutum 78 da makamai da kwayoyi a Kano JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa an kama wasu da ake zargi kuma Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) na gudanar da bincike.

An kuma tsare direban motar da ake zargin maharan sun yi amfani da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kugiyar asiri

এছাড়াও পড়ুন:

Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50

Iyalan sarkin Okoloke na jihar Kogi, Oba James Dada Ogunyanda, sun yi kira ga al’umma don taimakawa wajen tara kuɗin fansa Naira miliyan ₦50 da masu garkuwa suka buƙata. An sace Sarkin ne daga fadarsa a Yagba West LGA ranar Alhamis da ta wuce.

Duk da cewa sun tara miliyan ₦25 ta hanyar sayar da kayansu, iyalan sun ce wasu ‘yan siyasa da suke tsammanin za su taimaka sun har yanzu sun ji shiru. “Wasu ma sun toshe wayoyinmu,” in ji wani ɗan gidan, yana nuna damuwarsu game da yawan rashin lafiyar Sarkin da ke hannun masu garkuwa tsawon kwana 5.

Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

Masu garkuwar sun fara buƙatar miliyan ₦100 kafin su rage zuwa miliyan 50. Iyalan sun ƙaryata labarin cewa an ƙara rage kuɗin zuwa miliyan, suna mai cewa har yanzu masu garkuwar sun dage kan miliyan 50.

Sun yi kira ga manyan ‘yan siyasa na Kogi ciki har da Sanata Dino Melaye, Sanata Sunday Karimi, Hon Leke Abejide, Hon Faleke da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da su taimaka wajen cikasa sauran kuɗin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tottenham ta lashe Gasar Europa bayan doke Manchester United
  • Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci
  • Ana Kara Samun Karuwar Sojojin HKI Da Suke Kashe Kansu
  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 
  • Kungiyar Hizbullah Ta ce Marigayi Shahid Ra’isi Ya Kasance Mai Taimakawa Kasar Lebanon Da Kuma Falasdinawa Ne
  • Iran Ta Kira Jakadan Burtaniya A Tehran Saboda Tuhumar Da Akewa Iran Da Leken Asiri A London
  • Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50