Aminiya:
2025-07-06@14:02:07 GMT

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa

Published: 9th, May 2025 GMT

Wasu daliban jami’a da ke shirin tafiyar aikin yi wa kasa hidima NYSC sun rasu a wani harin da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne suka kai musu a yankin Gbarabtoru-Ekpetiama, Karamar Hukumar Yenagoa.

Matasan biyu da suka kammala karatunsu a Jami’ar Niger Delta (NDU), Amassomma, sun rasu ne bayan da gungun wasu mutane da ke wake-waken kungiyar asiri a cikin wata mota suka kai musu hari da adduna.

Kwamandan Kungiyar ‘Yan Banga (VGN) na Jihar Bayelsa,Tolummbofa Akpoebibo Jonathan ya ce, daya daga cikin samarin ya yi kokarin tserewa, amma maharan suka bi shi suka kama shi suka sassare shi.

Ya bayyana cewa da misalin karfe 11:00 na daren ranar Alhamis ne, abin ya faru kuma matasan biyu biyu sun mutu ne sakamakon raunukan da suka samu.

Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare An kama mutum 78 da makamai da kwayoyi a Kano JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa an kama wasu da ake zargi kuma Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) na gudanar da bincike.

An kuma tsare direban motar da ake zargin maharan sun yi amfani da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kugiyar asiri

এছাড়াও পড়ুন:

Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da labarin da ministan harkokin wajen kasar Jamus ya watsa dangane da shirin Nukliyar kasarsa ya kuma kara da cewa labarin jabu ne.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X . Ya kuma yi watsi da zancen ministan harkokin wajen kasar Jamus wanda yake cewa, jinginar da aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya wato IAEA wanda JMI ta yi,  ya na nuna cewa ba wanda zai bincika ayyukanta na makamashin nukliya ba, kuma ta rufe kofar tattaunawa Kenan.

Aragchi ya bayyana cewa wannan ba haka bane, saboda shirin nukliyar kasar Iran a halin yanzu ya na karkashin majalisar koli ta tsaron kasar Iran ne, don haka ita ce zata fayyece yadda huldar shirin zai kasance tare da hukumar IAEA. Sannan Iran bata fice daga yarjeniyar NPT ba.

Kasar Jamus dai tana goyon bayan hare=hare da HKI da AMurka suka kaiwa JMI a yakin kwanaki 12, dagan  cikin harda hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar. Ya ce aiki ne da bai dace ba wacce JKI ta yi madadin kasashen yamma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  • Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur
  • Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato