Natanyahu Ya Bada Umurnin A Dakatar Da Musayar Fursinoni Da Kungiyoyi Masu Gwagwarmaya A Gaza
Published: 30th, January 2025 GMT
Firai ministan HKI Banyamin Natanyahu Ya bada umurnin a dakatar da musayar fursinoni da kungiyoyi masu gwagwarmaya a Gaza. Bayan da Falasdinawa sun Saki mutane 8 ya zuwa yanzu, yahudawa 3 da kuma wasu yan kasar Thailand 5.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labaran yahudawan suna fadar haka.
Kafin haka dai Falasdinawan sun salami wadannan fursinonin yahudawan 8 ne a zagaye uku na musayar fursinoni da kuma janyewar sojojin yahudawan daga yankunan gaza. Majiyar ofishin firay ministan ya bayyana cewa an dakatar da musayar fursinonin ne har sai abinda hali yayi. Da kuma zuwa lokacinda za’a samarwa ma’aikatansa tsaro a gaza.
Kafin haka dai falasdinawa suna son musayar fursinonin yahudawa kimani 100 da suke hannunsu da faladinawa 2000 wadanda suke hannun HKI.
A yau Alhamis dai Falasdinawa sun saki wata fursina guda, ba yahudiya, sannan tana saran a saki falasdunawa 110 30 daga cikinsu yara kanana.
Ya zuwa yanzu dai yahudawan sun janye sojojinsu daga yankunan Falasdinawa da dama a zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Lebanon: Za A Yi Jana’izar FItaccen Mawakin Gwagwarmaya Da Kishin Kasa Ziyad Rahbani A Yau Litinin
A yau Litinin ne za a yi jana’izar sanannen mawakin kasar Lebanon wanda ya yi fice da wakokin gwgawarmaya da kishin kasa wanda zai sami halartar wakilan gwamnatin kasar da kuma al’umma.
Jana’izar za ta kasance ne a majami’ar Raqad Sayyida dake garin Bakfaya.
Asibitin Khuri da Rahbani ya rasu ya cika da mutane tun da safiyar yau domin daukar jana’izarsa zuwa garin Bakfaya.
A ranar Asabar din da ta gabata ne dai Rahbani ya rasu yana dan shekaru 69 bayan da ya yi gajeruwar rashin lafiya.
A lokacin rayuwarsa ya shahara da wakoki na gwgawarmaya da kishin kasa, daga cikin da akwai wakar da ya yi wa Shahid Sayyid Hassan Nasarallah.