2025-12-09@16:19:17 GMT
إجمالي نتائج البحث: 12298
«Shari a»:
Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia, Mohammed Haliru Arabo, na tsawon wata uku, kan rikicin shugabanci. Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ne ya sanar da hakan a ranar Talata a Lafia, bayan Shugaban Kwamitin Majalisar kan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, Musa Ibrahim Abubakar, ya gabatar da korafi kan rikicin mulki...
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ayyana dokar ta-baci a yankin, kwana biyu bayan yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Jamhuriyar Benin. Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar tsaro ta hukumar karo na 55 a Abua. Touray ya ce daukar...
Shugaban kasar Amurka Donal Trump yayi watis da kasashen turai a tattaunawar dawo da zaman lafiya a Ukraine, wanda hakain ya sa kasashen rauni a cikin al-amuran kasar ta Ukraine. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a wani taro mai muhimmanci wanda Volodimir Zelesky shugaban kasar Ukraine ya yi da Firai...
Ana taro kan yadda manzon Allah mohammad dan Abdullahi (a) ya zauna da wadanda ba musulmi ba a rayuwarsa a Madina. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto hukuma mai kula da al-adu da kuma al-amuran addinin Musulunci a nan Iran tana cewa ana gudanar da wannan taron ne a dai dai lokacinda...
Kakakin rundunar sama ta tarayyar Najeriya, wato ‘Nagerian Air Force’ Ehiment Ejodame ya bayyana cewa jirgin wani jirgin saman rundunar dauke da mutane 11 ya yi saukan gaggawa a kasar Burkina Faso a ranr litinin da ya gabata. Jiridar Daily Trust ta Najeriya ta nakalto Ejodame yana fadar haka a yau Talata ya kuma kara...
Kasashen saudiya da Qatar ta rattaba hannu kan yarjeniyar gida layin dogo mai sauri wanda zai hada birnin Doha na Riyad mai sauri. Shafin yanar gizo na labarai ArabNews ya nakalto cewa kasashen biyu sun cimma wannan yarjeniyar ne a jiya litinin bayan ganarwar yarima mai jiragn gadon sarautar saudiya Mohammad bin salman kuma Firai...
Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya...
Gwamantin Nigeria ta aike da jiragen yaki zuwa kasar Benin domin taimaka wa gwamnatin farar hula domin dakile yunkurin juyin mulkin da aka yi a kasar. Aikin da jiragen yakin su ka fara yi, shi ne shimfida ikonsu a sararin samaniyar kasar Benin a ranar Lahadin da ta gabata,adaidai lokacin da sojoji da suke biyayya...
Kwamandan sojan kasar Pakitsan Asim Munir ya ce; Dole ne Taliban ta zabi wanda za ta yi mu’amala da hulda da su, ko dai gwamnatin Pakistan din, ko kuma ‘yan ta’adda. Asim Munir wanda a makon da ya shude aka sake tabbatar da shi akan mukaminsa na shugaban sojojin kasar, ya kara da cewa sun...
Ministan ilimi da kere-kere na Iran Husain Simayi, wanda ya gana da jakadan kasar Turkiya anan Iran Hijabi Kalanjik ya bayyana azamar kasashen biyu domin yin aiki a wannan fagen. Ministan ilimin da kuma fasahar kere-kere na Iran ya kuma ya kuma ce; Iran tana bayar da muhimmanci ga jami’o’in Turkiya wadanda a bisa ma’aunin...
A wani rahoton da jaridar Jerissalam Post” ta buga ta ambaci cewa; Tun bayan farmakin 7 ga watan Oktoba 2023, ana kara samun matalauta da talauci. Rahoton ya yi nuni da cewa karuwar talaucin yana da alaka ne da yadda farmakin 7 ga watan Oktoba ya yi tasiri a cikin tattalin arziki “Isra’ila”. Haka nan...
Daga Aliyu Muraki Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce gwamnonin Arewa sun amince su sayi na’urorin zamani na tsaro da kuma daukar matasa aiki don tallafawa ayyukan tsaro domin magance matsalolin rashin tsaro a yankin. Gwamnan ya bayyana hakan ne a zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar a Lafia, babban birnin...
Daga Nasir Malali An kashe ’yan bindiga guda goma sha takwas a wani samame da Rundunar Hadin Gwiwa ta Operation Fansan Yamma ta kai a kauyen Kurawa da ke Karamar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sokoto. A wata hira ta wayar tarho, wani shaida daga yankin, Malam Aminu Muhammad, ya shaida wa Rediyon Najeriya a...
Daga Isma’il Adamu Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwar lashe karin mukaman siyasa a zaben shekarar 2027, ciki har da na shugaba kasa da gwamnan Jihar Katsina. Sabon shugaban jam’iyyar da aka rantsar a Jihar Katsina, Alhaji Armaya’u AbdulKadir ne ya bayyana haka a zaben shugabannin jam’iyyar da aka gudanar a Katsina....
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya. A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed...
Kungiyar Tarayyar Afrika ta AU ta yi tir da harin RSF kan wata makarantar kananan yara a kudancin Sudan da ya kashe dimbin fararen hula tare da jikkata da dama, mafi muni a baya-bayan nan da kungiyar ta kai a kokarin da ta ke yi na ci gaba da kwatar yankuna a sassan Kasar. Akalla...
Wakiliyar musamman ta majalisar dinkin duniya kan yankin falasdinu da aka mamaye Francesca Albanese ya bayyana irin halin da ake ciki a yankunan falasdinu da isra’ila ta mamaye a matsayin babban bala’I, ta ce kuma shi ne kisan kare dangi na farko da ya tada hankali duniya sosai. Da take bayani wajen rufe taron da...
Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi da kuma shugaban kasar Azarbaijan Ilham Aleyev a birnin Baku sun tattauna kan dangantakar dake tsakaninsu da kuma hanyoyin da zaa bi wajen warware kalubalen da ake fuskanta. Kasashen iran da Azarbaijan suna da alakar aladu da tarihi mai zurfi a tsakaninsu, kuma dukkan bangarorin biyu, sun jaddada...
A cikin wani taron hadin guiwa da aka yi takanin iran da sauran jakadun kasashen afrika guda 19 da sauran jami’an kasar iran, sun jadadda game da muhimmancin yin aiki tare a bangaren ilimi, bincike da kuma kiwon lafiya, da kuma yadda zaa kara karfafa alaka tsakanin Iran da kuma nahiyar Afrika. Taron ya nuna...
Kungiyar Habbaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka – Ecowas – ta sanar da tura rundunar ko-ta-kwana domin taimaka wa sojojin Jamhuriyar Benin wajen kakkabe sojojin da suka yi yunkurin juyin mulki. A wata sanarwa da kungiyar ta fitar da yammacin jiya Lahadi, ta ce “Shugaban Ecowas, bisa ga amincewar shugabannin kasashen kungiyar ya amince da...
Daga Bello Wakili Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnonin jihohi shidda daga sassan ƙasar a ci gaba da tattaunawar da ake yi domin ƙarfafa batun tsaro a ƙasa. Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo, Umar...
Dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ya bayyana cewa makamai masu linzamu na dakarun sun fada kan matatar man fetur na Haifa a HKI har sau biyu a yakin kwanaki 12 da ta fafata da Iran a cikin watan Yunin wannan shekara. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgediya...
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan kubutar da yan makaranta 100 daga cikin wadanda ‘yan ta’adda suka sace a wata makaranta a jihar Naija a cikin watan Nuwamban da ya gabatata. Tashar talabijan ta almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto kamfanin dillancin labaran reuters na cewa jami’an tsaron kasar sun sami nasarar kubutar da yan...
Firai ministan kasar Iraki Mohammad Shia Assudani ya bayyana cewa gwamnatinsa bata tushe asusun kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon da kuma Ansarallah ta kasar Yemewn ba. Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran IP ya nakalto sudanina cewa gwamnatinsa tana kokarin hana tasowar wani riki a yankin sannan da kuma kaucewa duk wani rikicin siyasa...
Daga Bello Wakili Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya isa Abidjan na kasar Côte d’Ivoire, domin wakiltar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a wajen rantsar da Shugaban Alassane Ouattara a wa’adinsa na hudu. Za a rantsar da Shugaban ne a yau Litinin, 8 ga watan Disamban 2025, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abidjan, wanda...
Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma dan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce Gwamnatin Tarayya ta gaza wajen shawo kan matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara a faɗin kasar nan, lamarin da ya ce yana barazana ga haɗin kan ƙasa da zaman lafiya. Kwankwaso, wanda ya taɓa zama Ministan Tsaro,...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Batun samar da ‘yansandan jihohi na ƙara ɗaukar hankalin ‘yan Najeriya, musamman a dai-dai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a sassa daban-daban na ƙasar nan. Sai dai, samar da ‘yansandan jihohi ba abu ne mai sauƙi Kamar yadda wasu ke tunani ba. Gwamnatocin jihohi na...
Jami’an Rundunar Leƙen Asiri ta musamman a Jihar Kwara sun cafke wani tsohon ɗan gidan yari mai suna Godday Agaadi da bindiga ƙirar AK-47. An kama Emmanuel Okah ne bayan an same shi da bindigar AK-47 da harsashi guda 25 a jikinsa, a lokacin da yake sanye da kayan ’yan sanda. Dubunsa ta cika ne...
Sojojin kasar Thailand sun sanar a yau Litinin cewa, son kai wani sabon hari akan iyakar da take da sabani da makawabciyarta Cambodia. Wannan sanarwar ta sojojin Thailand ya biyo bayan da kasashen biyu suka rika zargin juna da cewa sun keta dakatar da wutar yaki, da shugaban Amurka Donald Trump ya shiga tsakani. Sojojin...
Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran Dr. Isma’ila Baghaie ya yi tir da kashe fararen hula a garin Kalogi dake Jahar Kurdufan na Sudan. Bugu da kari kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su kawo karshen abinda yake faruwa a wannan kasar. Kusan mutane...
Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi wa kasar Najeriya alkawalin taimaka ma ta domin ta fuskanci matsalolin tsaro, musamman ma dai ta’addanci a arewacin kasar. Shugaban kasar Faransan ya ce, takwaransa na Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya bukaci taimako domin fuskantar matsalar tsaro a arewacin kasar. Macron ya rubuta a shafinsa na X cewa;...
Mai Magana da yawun fadar mulkin Rasha Dmitry Viskov ya ce; Fadar mulkin kasar tana maraba da matakin da shugaban kasar Amurka ya dauka na bitar siyasar tsaron kasar, da ta kunshi cire kasar Rasha a matsayin barazanar da Amurkan take fuskanta. Viskov ya fada wa kamfanin dillancin labarun “Tass” cewa; a cikin sabon tsarin...
Fitacce mai shirya fina-finai dan kasar Iran Majid Majidi ya sami kyauta ta musamman a wurin bikin fina-finai na Eurasia, saboda gagarumar rawar da yake takawa a fagen shiryafina-finai da su ka shahada a duniya. A ranar Alhamis din da ta gabata ne aka bude bikin a birnin Moscow wanda ya sami halartar ministan al’adu...
Masana harkokin siyasa, jakadu da ƙungiyoyin fararen hula sun bayyana cewa rashin shugabanci nagari da son mulki na dogon lokaci su ne manyan dalilan da ke haddasa yawaitar juyin mulki a yankin Afirka ta Yamma. Wannan na zuwa ne bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Benin a ranar Lahadi, wanda ya jefa...
Aƙalla sojoji 13 aka cafke a ƙasar Benin bayan yunƙurin da juyin mulki da suka yi bai yi nasara ba. Majiyoyin tsaro da na soja sun bayyana cewa dukkan waɗanda aka kama sojoji ne masu aiki a halin yanzu, sai mutum ɗaya da ya taɓa yin aiki a rundunar amma ya yi ritaya. Kama su...
Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF), ta ce ta taka muhimmiyar rawa wajen daƙile yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin, bayan wasu sojoji sun bayyana hamɓarar da Gwamnatin Shugaba Patrice Talon. Gungun sojojin, sun bayyana cewa ta rushe gwamnati tare da dakatar da kundin tsarin mulki, da rufe iyakokin ƙasar. An gano gawar malamin Islamiyya da...
An gano gawar wani malamin makarantar Islamiyya kuma mahaifin ’ya’ya bakwai, Malam Awwal Yakubu, a cikin wani kango da ke rukunin gidaje na Talba a birnin Minna, na Jihar Neja. Malam Awwal, yana da makarantar Islamiyya a unguwar Barikin-Saleh, an neme shi sama ko ƙasa tun ranar Alhamis ɗin da ta gabata. ’Yan bindiga sun...
Rahotanni daga Jamhuriyar Benin na cewa am kama wasu 12 bayan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba da jijjibin safiyar Lahadin nan. Tun da farko dama fadar shugaban kasar ta ce har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin. Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Benin ya bayyana a gidan talabijin din...
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa har yanzu Amurka ba ta nuna sha’awarta ta shiga “tattaunawa mai ma’ana ba,” yana mai sake nanata cewa dole ne Washington ta fara amincewa da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya na zaman lafiya a karkashin Yarjejeniyar hana yaduwar Makaman Nukiliya ta (NPT). A...
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa Hamas ta bayyana cewa za ta mika makamanta ne kawai ” idan Isra’ila ta kawo karshen mamaya, tana mai jaddada cewa ba za a iya kwance damarar makamai ba a cikin yanayin da ake ciki na zaluncin soja da siyasa. Babban jami’i a ofishin siyasa na Hamas kuma babban mai shiga tsakani...
Jamhuriya Musulinci ta Iran, ta bayyana sabbin dabarun tsaron Amurka na cimma maradun gwamnatin Isra’ila ne. Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya ce sabbin dabarun tsaron Kasa na Amurka (NSS) da ke bayyana ka’idojin Washington da muhimman manufofin harkokin waje a zahiri cimma maradun tsaro ne ga gwamnatin Isra’ila ne. Esmaeil Baghaei ya yi wannan...
Kasar Masar ta sake jaddada cewa ba za ta bari a yi amfani da hanyar shiga iyakar Rafah don korar Falasdinawa daga gidajensu ba, tana mai jaddada bukatar sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza. Ministan harkokin wajen Masar Badr Abdelatty ya yi wannan furucin ne a wata hira da ya yi da Al...
’Yan bindiga sun kai sabon hari wasu yankuna na Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutane huɗu tare da yin awon gaba da mata huɗu. Wani mazaunin Gatawa, ya shaida wa Aminiya ce harin ya faru ne a daren ranar Asabar, lokacin da ’yan bindiga sama da goma suka shiga garin a kan babura. Mutum 5...
’Yan bindiga sun kai sabon hari wasu yankuna na Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutane huɗu tare da yin awon gaba da mata huɗu. Wani mazaunin Gatawa, ya shaida wa Aminiya ce harin ya faru ne a daren ranar Asabar, lokacin da ’yan bindiga sama da goma suka shiga garin a kan babura. Mutum 5...
Majalisar Dokokin Amurka ya iso Abuja yayin da ƙasashen biyu ke ƙara matsa ƙaimi wajen tattaunawar diflomasiyya kan haɗin gwiwar tsaro da kuma zargin tauye haƙƙin addini. Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu, ya ce ya gana da wakilan kuma zuwan tawagar na cikin abubuwan da suka amince da shi a...
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu mutum biyar sakamakon haɗura uku da suka auku a jihar. Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce hatsrin farko ya faru ne da safiyar ranar Alhamis a unguwar Badawa Layin Day by Day ca Ƙaramar Hukumar Nassarawa. Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a...
Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta bayyana cewa ta dakile wani yunkurin juyin mulki, bayan da wasu sojojin ƙasar suka sanar da cewa sun hambarar da shugaba Patrice Talon a gidan talabijin na kasar. Talon, mai shekaru 67, tsohon dan kasuwa ne wanda aka yiwa lakabi da “Sarkin Auduga na Cotonou”, zai mika mulki a watan Afrilun...
Wani jirgin Sojin saman Najeriya ya yi haɗari jim kaɗan bayan tashi daga sansanin Sojin ƙasar da ke Kainji a jihar Neja, sakamakon tangarɗar inji. Kakakin rundunar sojin saman na Najeriya Ehimen Ejodame lokacin da yake tabbatar da faruwar haɗarin ya ce babu ko mutum guda da ya rasa ransa sanadiyyar wannan haɗari, sai dai...
Gwamnatin kasar Rwanda ta rattaba hannu a kan yarjeniya na dalar Amurka miliyon $228 a karkashin sabon tsarin taimako na gwamnatin kasar Amurka. Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa tallafin zai taimakawa kasar Rwanda ta kyautata harkokin kiwon lafiya a kasar ta Rwanda a yayinda tallafin kudaden zai ci gaba a...
Tom Barrack jakadan Amurka na musamman a kasar Siriya ya bayyana cewa gwamnatin kasar Amurka ta yi kokarinkifar da gwamnatin JMI a baya har sau biyu amma ta kasa yin haka. Tashar talabijin ta Presstva a nan Tehran ta nakalto Barrack yana fadawa wani kamfanin dillancin labaran UAE a ranar jumma’an da ta gabata, ya...
