A jawabinsa a wajen tarbar Jirgin Ruwan na na yankin Asia Jim Stewart, ya bayyana jin dadinsa ga Hukumar ta NPA, bisa goyon bayan da ta bayar wajen samar da kyakyawan yanayi a babban wajen da Jiragen Runwan na Tashar Onne suke tsayawa.

“Muna da kyakaywar dangantakar gudanar da ayyuka da Manajan Tashar ta Onne Mista Abdulrahmon Hussain da kuma sauran ‘yan tawagar Hukumar ta NPA, “Inji Stewart.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin shugabancin shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho, wanda kuma kashin bayan duk wata nasara da muka zamu.

“Sake farfado da babban wajen tsayawar Jiragen Ruwan a Tashar Onne, hakan ya kara mana kwarin Guiwa”. A cewar Stewart.

Kazalika, Stewart ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kara samar da wadatattun kudade domin a kara fadada aikin yasar Gulnin da ke a Tashar ta Onne.

Tashar ta Onne, musamman domin a samu karin yawan Jiragen Ruwa masu tsayawa a Tashar, wanda hakan zai kuma kara taimaka wa, wajen bunkasa hada-hadar kasuwanci a Tashar.

“Mun shirya tsaf, domin tarbar Jiragen Ruwa masu yawa da suka, amma domin mu ci gaba da cin gajiyar da ta kamata a Tashar ta Onne, akwai matukar bukatar a mayar da hankali wajen kara fadada yin haka a Gulbin da ke a Tashar, ” Inji Stewart.

“Mun kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kara taimaka wa Hukumar ta NPA da kudaden da suka kamata, musamman domin a kara fadada hakar Gubin na Tashar Onne,” A cewar Stewart.

 

Ya bayyana cewa, biyo bayan isowar da Jirgin Ruwa na Kota Cempaka ya yi a Tashar ta Onne, a shekarar da ta gabata, wannan nasarar ta nuna irin yadda ake ci gaba da samar da dabarun zuba hannun jari a Tashar ta Onne da kuma yadda aka kara mayar da hankali, wajen kara inganta ayyukan na Tashar.

Kazalika, Stewart ya jaddda mahimmancin zamanantar da Tashar ta Onne, ta hanyar gyare-gyaren da ake yi a Tashar, matsayin wata manufa ta rage cunkoson Jiragen Ruwa da ke tsayawa Tashar.

 

Ya yi nuni da cewa, ganin yadda irin wadannan manyan Jiragen Ruwa suka fara isowa Tashar ta Onne, hakan kara taimaka wa, wajen kara bunka tattalin arziki ga Tashoshin Jiragen Ruwan kasar nan,

Ya kara da cewa, hakan zai kuma kara taimaka wa, wajen ragewa ‘yan kasuwar da ke shigoa da kayan zuwa cikin kasar nan da kuma rage cazarsu kudin harajin fitar da kaya zuwa ketare.

 

“Wannan nasarar bai wai kawai ta shafi Tashar ta Onne bane kadai, har da daukacin tattalin arzikin kasar nan, kuma sake farfadowar Tashar ta Onne, za ta kara bayar da wata damar kara shigowar Jiragen Ruwa cikin kasar nan, wanda hakan zai kuma kara samarwa da Nijeriya, da wasu kudaden shiga, “Inji Stewart,

Shi kuwa a na sa jawabin Hukumar ta NPA wani babban Direban Jirgin Ruwa a Tashar ta Onne Yakubu Ezra, ya jaddada cewa, Hukumar ta NPA, a shiraye take wajen karbar duk wasu Jiragen Ruwa da za su sauka a Tashar ta Onne.

“An tanadar da isassun kayan aiki na fasahar zamani Tashoshin Jiragen Ruwan kasar nan, musamman domin a Jiragen Ruwan su rinkaa tsakyawa a cikin sauki, tare da kuma bai wa ma’aikatan horon da ya dace, “ Inji Yakubu.

A cewasa, samun nasarar ta isowar Jirgin Ruwan na Kota Carum alamu ne da nuna irin karfin Tashar ta Onne da kuma irin kwarewar da Tashar take da shi.

Ganin yadda Jiragen Ruwa da dama daga Afrika ta Yamma ke shirin isowa Tashar ta Onne, hakan ya kara nuna irin ingantattun kayan aiki da damarun da aka samar a Tashar, wanda hakan zai kara bayar da dama wajen kara janyo zuwan Jirage da kasa da kasa, zuwa Tashar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a Tashar ta Onne kara taimaka wa Hukumar ta NPA Jiragen Ruwan Jiragen Ruwa Jirgin Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaduwa da rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci kuma jagoran Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Fitaccen malamin ya rasu a Bauchi ranar Alhamis yana da shekaru 101.

Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

A cikin wata sanarwa da Kakakin shugaban, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya bayyana Sheikh Dahiru Bauchi a matsayin jagoran da ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa, wa’azi da jagorantar al’ummar Musulmi.

Tinubu ya ce rasuwar malamin ba wai asara ce ga iyalansa da almajiransa kawai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba ne kuma murya ce ta daidaito da hikima. A matsayinsa na mai wa’azi kuma babban mai fassarar Alƙur’ani mai tsarki, ya kasance mai kira ga zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Ya tuna da albarka da ya samu daga marigayin a lokacin shirye-shiryen zaɓen 2023.

Shugaban Ƙasa ya miƙa ta’aziyya ga almajiran malamin a faɗin Najeriya da wajen ƙasar, yana mai kira da su dawwamar da sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, tsoron Allah da kyautatawa ɗan adam.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana
  • Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
  • Tashar Talabijin ta Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan