Aminiya:
2025-06-27@10:10:40 GMT

Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna ya rasu

Published: 13th, May 2025 GMT

Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna, Mukhtar Ramalan Yero ya riga mu gidan gaskiya kamar yadda Masarautar Zazzau ta tabbatar.

Alhaji Ramalan Yero, wanda ɗaya ne daga cikin dattawa kuma mai riƙe rawanin Turakin Dawakin Zazzau ya rasu ne da yammacin wannan Litinin ɗin bayan fama da doguwar jinya.

Marigayi Alhaji Ramalan Yero mahaifi ne ga tsohon Gwamnan Kaduna kuma Dallatun Zazzau, Dokta Muktar Ramalan Yero.

Wata sanarwa da Sarkin Fadar Zazzau, Alhaji Abbas Ahmed Fatika, ya fitar ta ce an yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 8:30 na daren yau bayan sallar Isha’i a Unguwar Ƙaura da ke cikin birnin Zariya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: masarautar zazzau Mukhtar Ramalan Yero Ramalan Yero

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici

Gwamnatin Jihar Neja, ta rufe Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU) da ke Lapai saboda matsalolin tsaro da suka janyo mutuwar wasu ɗalibai.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Abubakar Usman, ya ce an ɗauki wannan matakin ne saboda rashin tabbacin tsaro da ke barazana ga rayuwar ɗalibai da ma’aikata.

Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum 1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Gwamna Umaru Bago ya amince da rufe jami’ar nan take, kuma za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu sauyi.

“Lafiyar kowa, musamman ɗalibai da malamai, na da matuƙar muhimmanci ga gwamnatin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da abin da ya faru, kuma muna ɗaukar matakan gaggawa don magance lamarin.”

Gwamnatin ta roƙi ɗalibai, malamai da ma’aikatan jami’ar su kwantar da hankalinsu, kuma su kasance masu lura, su kuma yi aiki tare da jami’an tsaro a wannan lokaci.

Haka kuma gwamnatin ta tabbatar da cewa tana ɗaukar matakai domin wanzar da zaman lafiya.

Ta ce duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

“Za mu ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da kuma tabbatar da doka da oda a faɗin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn