Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna ya rasu
Published: 13th, May 2025 GMT
Mahaifin tsohon Gwamnan Kaduna, Mukhtar Ramalan Yero ya riga mu gidan gaskiya kamar yadda Masarautar Zazzau ta tabbatar.
Alhaji Ramalan Yero, wanda ɗaya ne daga cikin dattawa kuma mai riƙe rawanin Turakin Dawakin Zazzau ya rasu ne da yammacin wannan Litinin ɗin bayan fama da doguwar jinya.
Marigayi Alhaji Ramalan Yero mahaifi ne ga tsohon Gwamnan Kaduna kuma Dallatun Zazzau, Dokta Muktar Ramalan Yero.
Wata sanarwa da Sarkin Fadar Zazzau, Alhaji Abbas Ahmed Fatika, ya fitar ta ce an yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 8:30 na daren yau bayan sallar Isha’i a Unguwar Ƙaura da ke cikin birnin Zariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: masarautar zazzau Mukhtar Ramalan Yero Ramalan Yero
এছাড়াও পড়ুন:
Borrell : Rabin bama-baman da aka jefa a Gaza sun fito ne daga Turai
Tsohon jami’in harkokin wajen kungiyar tarayyar turai Josep Borrell ya yi kakkausar suka ga kungiyar kan rashin daukar mataki game da kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila ke yi a zirin Gaza yana mai cewa “rabin bama-baman da aka jefa a zirin Gaza ne muke kawowa.”
Da yake jawabi bayan karbar lambar yabo ta Carlos V ta Turai da ke Spain, Josep Borrell ya ce nahiyar Turai na shaida kawar da wata kabila tun bayan karshen yakin duniya na biyu, domin gina wurin yawon bude ido bayan korar da Falasdinawa.
Ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan kiyashi, ya kuma ce kungiyar EU, duk da cewa tana da hanyoyin nunna adawa da kuma kawo karshen ayyukan Isra’ila, amma ba ta sauke nauyin da ke kanta kan wannan batu ba.
Borrell ya ce: “kungiyar Tarayyar Turai ba ta yin abin da za ta iya.
Mista Borrell ya soki Isra’ila da keta dokokin yaki da kuma amfani da yunwa ga farar hular Gaza inda ya kara da cewa: ” bama-baman da aka jefa a Gaza sun ninka na bam din da aka jefa Hiroshima sau uku.”
“Kuma tsawon watanni, babu wani abu da ya shiga Gaza, babu ruwa, ba abinci, ba wutar lantarki, ba man fetur, ba kiwon lafiya.
Borrell ya ce: “Dukkanmu mun san abin da ke faruwa a can, kuma mun sami labarin manufofin da ministocin Netanyahu suka bayyana.
A ranar 18 ga watan Maris ne sojojin Isra’ila suka sake kai hare-hare a zirin Gaza, inda suka kashe dubban Falasdinawa tare da raunata wasu da dama, bayan karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni biyu da kungiyar Hamas da kuma yarjejeniyar musayar fursunonin Isra’ila da Falasdinawa.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza, ta ce akalla Falasdinawa 52,810 aka kashe, akasari mata da yara, yayin da wasu 119,473 suka jikkata tun bayan barkewar mummunan yakin da Isra’ila ta yi da yankin Falasdinu bayan harin ranar 7 ga Oktoba, 2023.