Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Published: 9th, May 2025 GMT
Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bukukuwan cika shekaru 80 da cimma nasara a yakin kishin kasa na tsohuwar Tarayyar Soviet.
An gudanar da faretin soja na ranar samun nasara, wanda ke ayyana cika shekaru 80 da samun nasara a yakin kishin kasa na Tarayyar Soviet ne a birnin Moscow.
Shugabanni daga kasashe da hukumomin duniya sama da 20 ne aka gayyata domin halartar bukukuwan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce gwamnati ce ke da alhakin samar da tsaro da haɗin kai a Jihar Filato da kuma Najeriya baki ɗaya.
Ya ce babu wata ƙasa da za ta shigo don kawo zaman lafiya na dindindin a Najeriya, face ’yan ƙasa sun haɗa kai.
’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — MuftwangAkpabio, ya yi wannan magana ne a filin Polo na Jos a ranar Asabar yayin taron tarbar sabbin mambobin da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a Jihar Filato.
Ya kira jama’a da su goyi bayan ƙoƙarin samar da zaman lafiya tare da yin aiki don ƙarshen rikice-rikece.
Ya ce Shugaba Bola Tinubu yana ƙoƙarin kawo ƙarshen kashe-kashe da tabbatar da zaman lafiya a Filato da sauran sassan ƙasar nan.
“Muna roƙon Allah Ya taimaka mana mu samu zaman lafiya a Filato. Duk wanda zai mulki Filato dole ne ya zama mutum mai kishin zaman lafiya. Wannan ita ce jam’iyyar da ta ke kula da ku,” in ji shi.
Akpabio, ya ƙara da cewa: “Na zo a madadin Shugaban Ƙasa domin tabbatar muku cewa za mu yi duk abin da ya kamata domin ku samu zaman lafiya.
“Babu wasu mutane daga waje da za su zo su kawo muku zaman lafiya. Dole mu ne za mu samar da shi. Dole mu zauna lafiya da juna. Najeriya na buƙatar zaman lafiya domin samun ci gaba.”
Ya tabbatar wa al’ummar Jihar Filato cewa gwamnati za ta magance matsalolin da suke fuskanta.
“Ina kuka a duk lokacin da na ji an kashe wani mutum; yaro ko babba. Matsalar da muke fuskanta ba yau ta samo asali ba.
“Mutane da dama sun mutu a Filato. An zubar da jini mai yawa, kuma ba mu farin ciki da haka. Shugaban Ƙasa ma ba ya farin ciki,” in ji shi.
Akpabio ya amince cewa da cewar ana kashe-kashe, tashe-tashen hankula a ƙasar nan, amma ya yi alƙawarin cewa nan da wani lokaci lamarin zai zama tarihi.
Ya roƙi al’ummar Filato da su goyi bayan Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewar za su samar da ci gaba.