Leadership News Hausa:
2025-06-23@22:39:40 GMT

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Published: 9th, May 2025 GMT

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci bukukuwan cika shekaru 80 da cimma nasara a yakin kishin kasa na tsohuwar Tarayyar Soviet.

An gudanar da faretin soja na ranar samun nasara, wanda ke ayyana cika shekaru 80 da samun nasara a yakin kishin kasa na Tarayyar Soviet ne a birnin Moscow.

Shugabanni daga kasashe da hukumomin duniya sama da 20 ne aka gayyata domin halartar bukukuwan.

(Fa’iza Mustapha)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran

Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da Isra’ila ke kai mata.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake magana da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ta wayar tarho.

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Shugaba Pezeshkian ya ce Iran tana da niyyar yin haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don amfani da makamashin nukiliya ta hanyar da ba ta da alaƙa da yaƙi, amma hakan ba yana nufin za su dakatar da inganta shirye-shiryensu na nukiliya gaba ɗaya ba.

Ya ƙara da cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa ƙasarsa ba za su wuce haka nan ba, domin kuwa Iran za ta riƙa mayar da martani mai zafi.

A ranar Asabar, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗi cewa za ta kai wa Isra’ila ta hark ta jiragen ruwa.

A cewar wani kakakin rundunar sojin Iran da ya bayyana a wani bidiyo, duk ƙasar da ta tura makamai zuwa Isra’ila, kamar ta shiga yaƙi da Iran ce kai-tsaye, kuma Iran ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare kanta ba.

A ranar Juma’ar da ta gabata, Iran ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa Isra’ila, lamarin da ya jikkata mutane aƙalla 19 a birnin Haifa da ke Arewacin Isra’ila, kamar yadda wani asibiti a yankin ya tabbatar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya
  • Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran