Bukatun da shugaban Amurka ya fara gabatarwa shugaban gwamnatin Siriya al-Julani a gamuwarsu ta farko

Fadar shugabanci ta Amurka White House ta bayyana cikakken bayani kan ganawar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi da shugaban gwamnatin rikon kwarya ta Siriya, Ali al-Julani, a birnin Riyadh fadar mulkin kasar Saudiyya a ranar Laraba.

A cikin wata sanarwa da fadar White House ta fitar ta ce: Trump ya karfafa al-Julani da yin abin da ya bayyana a matsayin wani babban aiki ga al’ummar Siriya, wato sanya hannu kan yarjejeniyar kyautata alakar jakadanci da gwamnatin yahudawan sahayoniyya, a karkashin tsarin da kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa, Bahrain da Morocco suka kulla alaka da gwamnatin mamayar Isra’ila a shekara ta 2020.

Trump ya kuma yi kira ga al-Julani da ya kori Falasdinawa daga Siriya, yana nufin manyan shugabannin kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinu.

Trump ya kuma yi kira ga al-Julani da ya yi aiki don hana sake bullowar kungiyar ta’addanci ta Da’ish wato ISIS a Siriya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali

Rahotanni daga sojojin da ke mulki a Mali, sun ce sun kama wasu sojoji kusan 30 da ake zargin suna shirin kifar da gwamnati ƙasar.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa cikin waɗanda aka kama akwai Janar Abass Dembele, tsohon gwamnan yankin Mopti da ke tsakiyar ƙasar.

Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 

Har yanzu gwamnatin ƙasar ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba game da lamarin.

Ita ma gwamnatin da ke mulki yanzu ta karɓi mulki ne ta hanyar juyin mulki a shekarar 2021.

Wannan zargi ya ƙara nuna cewa akwai rashin kwanciyar hankali a tsakanin gwamnatin sojin.

Yanzu haka dai gwamnatin na fuskantar matsalar hare-haren masu iƙirarin jihadi a Arewacin Mali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Lafiyar Tinubu kalau – Soludo
  • PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
  • Giyar mulki Na Jan Trump – Ƴan Democrats
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu
  • Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
  • Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali