Kasafin kudi na birnin tarayya Abuja (FCT) na shekarar 2025, kimanin naira tiriliyan 1.78 da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisa, ya tsallake karatu na biyu. Shugaba Tinubu ya gabatar da kudirin kasafin FCT na 2025 ta wata wasika da ya aike zuwa ga shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, inda ya bukaci ‘yan majalisar su gaggauta amincewa da kudirin domin saukaka aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa a babban birnin kasar.

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte Da yake karanta wasikar a zauren majalisar a ranar Laraba a Abuja, Akpabio ya bayyana cewa, gabatar da takardar ya yi daidai da sashe na 299 na kundin tsarin mulkin kasar, wanda ya bai wa shugaban kasa ikon mika kudirin kasafin kudin FCT ga majalisar dokokin kasar domin tantancewa da kuma amincewa. Tinubu ya bayyana cewa, an tsara kasafin ne domin bunkasa muhimman sassa da suka hada da kiwon lafiya, jin dadin al’umma, noma, da kuma samar da ayyukan yi. Shugaban ya bayyana cewa, kashi 85 cikin 100 na kasafin za a kashe su ne wajen kammala ayyukan more rayuwa da ayyukan raya kasa, inda aka ware kashi 15 cikin 100 domin aiwatar da sabbin tsare-tsare.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Nasarawa Ta Bukaci Gwamnati Ta Kai Dauki Ga Wadanda Iftila’in Guguwa Ya Shafa

Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta bukaci Gwamnatin Jiha da kananan hukumomin jihar goma sha uku da su gaggauta bayar da kayayyakin tallafi ga wadanda guguwar iska ta shafa a fadin jihar.

Majalisar ta bayyana cewa hakan na da muhimmanci domin inganta rayuwar wadanda abin ya shafa da rage musu radadin halin da suke ciki.

Shugaban Majalisar, Dr. Danladi Jatau, ne ya bayyana hakan bayan Hon. Hudu A Hudu ya gabatar da batun a matsayin lamari mai muhimmanci ga jama’a, yayin zaman majalisar da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Shugaban majalisar ya ce abin jimami ne kwarai yadda guguwar iska ta lalata gidaje, makarantu, gine-gine da wasu muhimman kayayyaki da suka kai daruruwan miliyoyin Naira tare da jikkata mutane da dama.

“Ina godiya da wannan kuduri da Hon. Hudu A Hudu ya gabatar domin wannan iftila’in ya shafi mazabata kai tsaye, inda guguwar ruwan ta rushe dakin jarrabawa na GSS Bassa. Har ila yau, kusan dukkan mazabu a fadin jihar sun fuskanci wannan matsala kamar yadda yawancin ‘yan majalisa suka bayyana.

“Shawarar mu ita ce, dukkan shugabannin kananan hukumomi 13 na jihar su tattara bayanan gine-gine da mutanen da abin ya shafa tare da nemo hanyoyin da za a tallafa musu.

“Muna kira ga Mai Girma Gwamna da ya umurci hukumar bada agajin gaggawa ta jihar NASEMA da ta gaggauta daukar mataki ta hanyar raba kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa,” in ji shi.

Har ila yau, majalisar ta bayyana cewa guguwar ta bar iyalai da dama cikin kunci yayin da wasu ke kwance a asibitoci.

Tunda farko, Honarabul Hudu A Hudu, dan majalisa mai wakiltar Mazabar Awe Arewa, yayin da yake gabatar da batun, ya ce al’ummar Mahanga da ke mazabarsa da wasu yankuna sun rasa matsugunansu sakamakon guguwar.

“Wannan lamari ya shafi rayuwarsu ta yau da kullum matuka, inda gidaje fiye da 30 da mutane 500 suka samu matsala.

“Ina kira gare ku da ku goyi bayan wannan kuduri domin gwamnati ta zo ta taimaka wa mutanena.” Inji shi

 

Daga Aliyu Muraki

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci Gwamnati Ta Kai Dauki Ga Wadanda Iftila’in Guguwa Ya Shafa
  • Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
  • Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Amince Da Wasu Dokokin Ci Gaban Kasa
  • Dole Ne Kansiloli Su Shiga Cikin Dukkan Ayyukan Kananan Hukumomin Su – Gwamna Yusuf
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
  • Majalisa ta yi watsi da kudurin dokar mulkin karba-karba
  • Majalisar Kaduna Za Ta Sanya Mutane 700 Cikin Tsarin Kiwon Lafiya Na Jiha
  • NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
  • ’Yan ta’adda sun ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa