Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar
Published: 9th, May 2025 GMT
A wani lokaci a gobe Asabar ne ake sa ran ministan harkokin wajen Iran zai fara wata ziyara a kasashen Saudiyya da kuma Qatar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi zai ziyarci Saudiyya da Qatar a, bayan rahotannin da ke cewa akwai yiwuwar yin wata sabuwar tattaunawa tsakanin Tehran da Washington.
M. Baghai ya bayyana cewa ziyarce ziyarce da Araghchi zai yi na daga cikin manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na ci gaba da karfafa alakarta da makwabtanta.
“Ministan harkokin wajen kasar ta Iran, zai fara tafiya birnin Riyadh don ganawa da manyan jami’an Saudiyya, sannan kuma zai tafi Doha don halartar taron tattaunawa tsakanin Iran da kasashen Larabawa.”
Bayanin hakan ya biyo bayan rahoton da kafar yada labaran Amurka Axios ta bayar cewa, ranar Lahadi ne ake sa ran za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawar tsakanin Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani.
Tun da farko dai an shirya gudanar da taron ne a ranar 3 ga watan Mayu, amma aka dage.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa tattalin arzikin kasar Iran nan gaba zai ginu ne bisa shirin bayan karewar man fetur ne, inda fasahohi da ilmi da kirkire-kirkire da kuma darussan da za’a dauko daga kasashe kawayen kasar a kungiyoyin BRICS da kuma SCO ne zasu zama abin dogaru.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto shugaban yana fadar haka ne a daren jiya Asabar a wani taro wanda yake magana a kan hanyoyin da Iran zata bi don bunkasa fasaha da ilmin kere-keren kasar da samar da ci gaba masu dorewa a kasar. Pezeshkiya yace sauye-suyen da sauri da ake samu a duniya musamman a yankin tekun fariya sun sanya dabarbarun ci gaba na sauyawa da sauri ga kasar Iran.
Ya ce dole ne Iran ta maida hankali wajen samar da dukiya ta hanyar samar da kamfanoni wadanda suka gina ayyukansu kan bincike da ilmi. Mu dauko ilmomin jami’o’immu mu maida su a aikace a cikin kamfanonimmu.
Sanna ya kara da cewa dole ne mu dauki korewar da kasashe mambobi a kungiyoyin BRICS da SCO mu yi amfani da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Hamas Ta Yi Bukaci A Hukunta HKI Akan Rusa Asibitoci September 21, 2025 IRGC: Duk Wani Sabon Kuskuren Abokan Gaba Zai Fuskanci Mayar Da Martani Mai Tsanani September 21, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Wata Mota A Kudancin Labanon September 21, 2025 Iran Za ta Iya Shawo Kan Duk Wani Takunkumi Da Aka Sanya Mata . September 21, 2025 Pakistan:Yarjejeniyar Tsaro Da Suka Kulla Da Saudiya Kamar Kawancen Tsaro Na Nato Ne. September 21, 2025 Matatar Mai Ta Dangote Ta Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai A Nijeriya September 21, 2025 Isara’ila Ta Kaddamar Da Shirin Iko Da Wasu Yankuna A Yammacin Kogin Jodan. September 21, 2025 Iran za ta katse hulda da IAEA idan aka maida mata takunkuman MDD September 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci