HausaTv:
2025-06-24@09:01:05 GMT

Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar

Published: 9th, May 2025 GMT

A wani lokaci a gobe Asabar ne ake sa ran ministan harkokin wajen Iran zai fara wata ziyara a kasashen Saudiyya da kuma Qatar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi zai ziyarci Saudiyya da Qatar a, bayan rahotannin da ke cewa akwai yiwuwar yin wata sabuwar tattaunawa tsakanin Tehran da Washington.

M. Baghai ya bayyana cewa ziyarce ziyarce da Araghchi zai yi na daga cikin manufofin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na ci gaba da karfafa alakarta da makwabtanta.

“Ministan harkokin wajen kasar ta Iran, zai fara tafiya birnin Riyadh don ganawa da manyan jami’an Saudiyya, sannan kuma zai tafi Doha don halartar taron tattaunawa tsakanin Iran da kasashen Larabawa.”

Bayanin hakan ya biyo bayan rahoton da kafar yada labaran Amurka Axios ta bayar cewa, ranar Lahadi ne ake sa ran za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawar tsakanin Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani.

Tun da farko dai an shirya gudanar da taron ne a ranar 3 ga watan Mayu, amma aka dage.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran

Amurka ta sanar da kaddamar da manyan hare-hare kan wasu muhimman cibiyoyin nukiliya a kasar Iran.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce an kai hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliya guda uku na Iran, inda ya yi barazanar kai wasu hare-haren idan har Iran ba ta nemi yi sasanci ba.

Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

A wata sanarwar da Trump ya fitar a jawabin da ya yi a talabijin yana ikirarin sun tarwatsa cibiyar, ya ce “hare-haren na soji babbar nasara ce.”

Trump ya ce Amurka ta kai hare-haren ne a yankunan Natanz and Isfahan na cibiyar nukiliyar Fordo wurin da Iran ke aikin shirin bunkasa makamashinta na Uranium da ke can karkashin kasa.

A cikin jawabinsa Trump ya ce ko dai Iran ta nemi zaman lafiya ko kuma ta fuskanci mummunan bala’in fiye da wanda aka gani a kwanaki takwas da suka gabata.

“Amurka za ta sake kai wa Iran hari idan har ba ta nemi yin sulhu ba,” a cewar Trump.

Gwamnatin Iran ta tabbatar da hare-haren amma ta ce babu wani lahani da suka yi wa cibiyoyin nukiliyarta, sannan kuma ta musanta ikirarin cewa an tarwatsa cibiyoyin.

Hukumar makamashi ta Iran ta ce hare-haren na rashin hankali ne da suka saba wa dokokin duniya, kuma hukumar ta ce hare-haren ba za su hana Iran ci gaba da cimma muradin ta ba na samar da makamin nukiliya.

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya la’anci hare-haren na Amurka yana mai cewa kasarsa za ta yi duk mai yiwuwa domin tana da hakkin kare ’yancinta.

Shi dai Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya taya Trump murna kan hare-haren, yana mai cewa “da karfin gaske da adalci na Amurka zai canza tarihi.”

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah-wadai da hare-haren na Amurka, inda Antonio Guterres ya ce babbar bazarana ce ga zaman lafiyar duniya kuma mataki ne mai hatsari na kara rura wutar yaki, haka ma kasashe aminan Iran irinsu Cuba da Venezuela sun yi Allah-wadai da hare-haren.

Tun a ranar 13 ga watan Yuni ne Isra’ila ta ƙaddamar da hari kan Iran, tana mai cewa ta yi hakan ne domin kawar da shirin Iran na mallakar makamin nukiliya, bayan Firaiminista Benjamin Netanyahu ya yi iƙirarin cewa Iran na dab da mallakar makamin.

A matsayin martani, Iran ta ƙaddamar da hare-haren ɗaruruwan makamai masu linzami da na jirage marasa matuƙa kan Isra’ila, inda ƙasashen biyu suka ci gaba da musayar wuta ta sama, tsawon sama da mako ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’
  • Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya