Leadership News Hausa:
2025-08-11@08:34:38 GMT

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Published: 11th, May 2025 GMT

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Sarkin Katsina Muhammadu Dikko Allah ya yi ma shi rasuwa,a shekarar 1944 da ba’a dade da shigarta ba,bayan ya sanu damuwa daga rashin lafiya, wannan shi yasa aka fara fafutukar neman wanda zai gaje shi.Ta bnagare daya akwai gidan Sarautar Dallazawa  a karkashin jagorancin Yarima, wanda shi dan Sarkin Katsina Abubakar ne wanda yake ganin Sarautar Katsina wata dama ce ta shi,sai ta daya bangaren kuma akwai ‘ya’yan marigayi Sarkin Katsina Muhammadu Dikko,wadanda su ma suna da matukar karfi,wadanda daga cikinsu ma da akwai wata ‘yar jayayya kan wanda zai gaji mahaifin nasu.

Watan Maris 1944,sai masu zaben Sarki suka zabi  karami daga cikin ‘ya’yan Dikko da ake kira da suna Usman Nagogo,wanda shi ne Turawan mulkin mallaka na Ingila suke so saboda yana da ilimin Boko,da kuma yadda ya kasance kusa da mahaifinsa.An nadawa Usman Nagogo rawanin Sarautar ranar  19 Mayu 1944 Yayin da shi kuma marigayi Sarkin Katsina Muhammadu Dikko aka rufe shi,a Lambun da ke fadar Sarkin Katsina Dikko

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Sarki Sarkin Katsina Muhammadu Dikko

এছাড়াও পড়ুন:

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

Waɗan nan sune suka keɓe makomar Nijeriya, kuma suka yi garkuwa da ita. Har ila yau, a cewar majalisar dattawa ta 9 da ta yi bincike na sayar da ƙaddarorin gwamnati, wanan ɓarnar dukiyar ƙasa ne a rana tsaka, kuma kamar yadda ɗaya daga cikinsu ya bayyana kafin ya koma cikinsu, ya ce: “PRIƁATIZATION” ba komai ba ce face “PIRATIZATION” — wato sata da rabon ganima ce a fili.

Waɗannan su ne masu kuɗi na yaki haram -yaki halas ,da suka ƙwace jam’iyyu, suka wawure zaɓuka, suka yi watsi da kowa sai nasu, suka kashe baitul-mali, kuma yanzu suna neman dawowa bisa kan Karagar Mulki da sunan dimokuraɗiyya. Wannan cutar dimokuraɗiyyar Nijeriya ce da ke ƙara bazuwa, kuma yaudara ne gadan-gadan da rana tsaka!

Ko wanne cikinsu yana da tabon keta doka. Waɗannan ‘yan wasan kwaikwayo ba ‘yan adawa ba ne ga juna, amma abokai ne wajen wawure dukiyar ƙasa da kuma durƙusar da ƙasa marasa kishin Nijeriya ko ‘yan Nijeriya, wanda suke kama da Judasu da ke neman a dawo da shi cikin sahun Manzanni.

“Izaa Zulzilatil Ardu Zilzaalahaa”

“Idan ƙasa ta girgiza da girgizarta ta ƙarshe…” (Suratul Zilzalah, Aya ta 1)

Amma tambaya biyu?:

Lokacin da waɗannan bayi, ‘yan cartel, masu siyar da Nijeriya , suke rike da gwamnati daga 1999 zuwa 2025:

Me suka yi alkawari ga ‘yan Nijeriya?

Me aka tono game da su bisa kundin tsarin mulkin 1999 da dokar sayar da kamfanonin gwamnati (Priɓatization Act), da rahotannin kwamitin majalisa, da ƙasidan el-rufai da bayanan jaridun gaskiya kamar Premium Times, Guardian, Daily Trust, ThisDay, Ɓanguard, Punch, Sahara Reporters da sauransu?

Alƙawura: (Sakamakon ƙarancin wuri, za a kawo kaɗan daga ciki)

Rashin inganci na kamfanonin gwamnati yasa za a sayar da su

Tsauri da wahalar tafiyar da su

Yawan ma’aikata

Rashin riƙon amana

Cin hanci da rashawa

Nauyi ga gwamnati

Rage kashe kuɗi

Samar da ayyukan yi

Shigo da jarin da ƙasashen waje

Gyaran tattalin arziki

Ci gaban ilimi da lafiya

Bunƙasa noma

Yaki da fatara

Samar da tsaro da walwala da dai sauransu…

Amma Abin Da Suka Aikata: Suna da hannu a:

Sayar da Niger Dock, sun kori ma’aikata 3,600

Sayar da Eleme Petrochemicals -Kafanin da ta saye ta tamayar da kuɗin ta har da riban jarin a cikin watani 14 kacal.

ALSCON – An gina ta akan kuɗi dalar amurka $3.2bn, aka sayar da ita akan dalar amurka $130m.

Sayar da Daily Times, NICON Insurance, Transcorp Hilton, da Ughelli Power

NEPA, NITEL, Nigeria Airways, Delta Steel, da sauran su

Cire tallafin man fetur.

Rashin biyan fansho da hakkokin ma’aikata.

Ka da mu manta da labarin akwatuna 53 a fili tashin jirgin saman a legas ( wato the 53 Suitcases Saga).

Da labarin dalar amurka $40m da aka fitar zuwa Amurka.

Takardun makaranta jamiá da shaidar ƙaryar ta Chicago State Uniɓersity.

Raba kan ‘yan Nijeriya da salon tsarin musulim – musulim ticket.

Zargin cin hanci na Grass-cutting a san sanin ‘yan gudun hijira.

Biyan fensho har ƙarshen rayuwa ga manyan sakatarorin gwamnatin taraya (PERM.SECs) da shugaban ma’aikata(Heads of Serɓice) daga asusun IPPIS ba tare da sun bada gudunmawa ba , da dai sauran su.

Rusa tattalin arziki ta karyar da darajan naira.

Ƙarancin abinci da ilimi

Durkusar da noma da kiwo da kuma tsarin noma da ya tsaya cik

Mayar da asibitocin wajen hanyar samun kuɗin shiga da taɓarɓarewan kiwon lafiya.

Rashin tsaro da garkuwa da jama’a da dai sauransu…

Kada mu manta da wanna ayoyin

“Faman ya’mal mithƙaala tharratin khayran yarah”- (Suratul Zilzalah, Aya ta 7)

“Wa man ya’mal mithƙaala tharratin sharran yarah “-(Suratul Zilzalah, Aya ta 8)

“Zaɓin da ke Gaban ‘Yan Nijeriya”

To ga su kamar haka, ‘yan Nijeriya na cewa:

PDP – Power to the People? To ku dawo da duk ƙadarorin da aka siyar ba bisa ƙa’ida ba kuma a siyar da ƙadarorin Dubai domin a kafa cibiyoyin masana’antu na matasa.

APC – Renewed Hope? Ku dawo da tallafin da aka cire, kuma a mayar da gidan Naira biliyan 21 zuwa Asibitin Ƙasa mai daraja ta ɗaya.

ADA – Justice for All? To ku dawo da duk kuɗaɗen da aka wawure daga sayar da ƙadarori da sauran madaƙala da ya faru a ƙarƙashin zamanin ku.

ADC – Arise & Shine? To ku jabaya kuba Nijeriya da ‘yan Nijeriya damar tashi, da haskakawa da cin nasara.

Tsakanin dukkan su dake cikin PDP, APC, ADA da ADC sun more rayuwa, sunyi komai mai yuwuwa a ƙarƙashin sama ta ɗaya, halartatce da haramtatce, ko ƙarya ne?

To kada mu manta da wanna aya -“Fabi ayyi aala’i Rabbikumaa tukazzibaan?”- (Surah Ar-Rahman: Ayoyi 13 da sauran ayoyi 30)

A Ƙarshe”

Bari mu rufe sharhin da waɗannan kalmomi masu ratsa zuciyar bil adama masu tsoron Ubangiji :

“Inna Allaha ‘ala kulli shai’in shaheed” – Lalle Allah shaida ne a kan komai. (Surah Al-Mujadilah: 6)

“Wallahu khabeerun bima ta’maloon” – Allah yana sane da duk abin da kuke yi. (Surah Al-Hujurat: 18)

“Wa makaroo wa makarallah, wallahu khayrul makireen” – (Surah Al-Imran: 54)

(Su sami malamai su yi masu cikanken bayanin wannan aya)

“Yawma’izinyasdurun naasu ashtaatan liyuraw a’maalahum” – A ranar nan, mutane za su rabu sassa daban-daban domin a nuna musu ayyukansu (munana da kyawawa). (Surah Al-Zalzalah: 6)

Hon. (Alh) Adamu Rabiu (Bakondare)

Ƙwararre a fannin Kula da Ayyuka da Tantance su (M&E) kan Manufofi, Kuɗi, Siyasa da Gudanar da Gwam

nati Mai Kyau, kuma mai fafutukar Ci Gaba Mai Ɗorewa. Ya rubuto daga Kaduna

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi
  • NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
  • Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina
  • Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman
  • Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu