HausaTv:
2025-05-10@01:20:19 GMT

Nijar da Iran sun cimma yarjejeniyar fahimtar juna a tsakaninsu

Published: 9th, May 2025 GMT

Kasashen NIjar da Iran sun cimma yarjejeniyar fahimtar juna a tsakaninsu a bangarori da dama.

Bangarorin sun sanya hannu a yarjejeniyar ne a yayin ganawar data wakana tsakanin ministan harkokin cikin gida da tsaron jama’a da wata tawagar Iran karkashin jagorancin babban kwamandan rundunar tsaron kasa Birgediya Janar Ahmad Rezaei RADAN.

A yayin wannan zama Nijar da Iran sun amince da kafa kwamitin kwararru domin yin musayar ra’ayi lokaci-lokaci da karfafa hadin gwiwa.

Nijar da Iran, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, musamman a fagen yaki da ta’addanci, da manyan laifuffukan kasa da kasa, tsaron iyakoki, da kuma shige da fice ba bisa ka’ida ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna

Wata kotun majistare da ke titin Ibrahim Taiwo a Kaduna ta gurfanar da wasu mutane 10 da suka haɗa da kaka, bisa laifin yi wa wata yarinya ’yar shekara 16 fyaɗe a ƙauyen Likoro da ke ƙaramar hukumar Kudan ta jihar.

An ruwaito cewa wanda ake zargi mutum na 11 na hannu a lokacin da shari’ar ta taso, ranar Alhamis.

An zaɓi Robert Prevost sabon fafaroma Ficewar ’Yan Majalisa 3 a PDP: Raɗɗa ya halarci zauren Majalisar Wakilai

Waɗanda ake zargin, a cewar rahoton farko da aka samu, sun ce wacce aka yi wa fyaɗen an yi ta aikat fyaɗen a lokuta daban-daban ta hanyar yaudara da kuma lallashinta ta zuwa wurarensu daban-daban inda suke da masaniya game da ita.

Lamarin ya haifar da samun ciki kuma wadda aka yi fyaɗen ta haifi ɗa namiji watanni huɗu da suka wuce.

Ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Insfekta Yakubu I. Lemu, ya ce matakin ya saɓawa sashe na 257 na kundin laifuffuka na Jihar Kaduna.

Ya ce, “A cewar rahoton farko da aka samu a ranar 27 ga watan Oktoba, 2024 da ƙarfe 6:30 na yamma, wani Usman Yusuf ya ruwaito cewa ya gano cewa ƙanwarsa Fatima Maikanti na ɗauke da juna biyu na wata shida, ya ce a lokacin da aka tambaye ta, ta bayyana cewa a wurare daban-daban, a lokuta daban-daban waɗanda ake zargin sun yi ta lalata da ita ne, sun kai ta wurare daban-daban a ƙauyen inda ta samu juna biyu, hakan ya sa ta haifi yaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar
  • An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna
  • Aragchi: Muna Bukatar Rage Zaman Daradar Da Kuma Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Pakisatan Da Indiya
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Rasha 
  • Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
  • Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje  
  • Kasashen duniya sun damu da rikici tsakanin Indiya da Pakistan
  • Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
  • Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa