Dole Ne Kansiloli Su Shiga Cikin Dukkan Ayyukan Kananan Hukumomin Su – Gwamna Yusuf
Published: 14th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umurci shugabannin kananan hukumomin jihar 44 da su tabbatar da cewa Kansilolinsu sun shiga dukkan ayyukan da aka gudanar a kananan hukumominsu .
Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da kansilolin kananan hukumomi 484 daga kananan hukumomi 44 na jihar.
Taron wanda ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, da nufin karfafa alaka tsakanin gwamnatin jihar da majalisun kananan hukumomi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa tana da hankali kuma ba ta da almundahana, kuma ba za a amince da duk wani nau’i na almundahana ba.
Ya kuma bukaci kansilolin da su yi aiki tukuru don ganin sun rike amanar da aka ba su.
Gwamnan ya shawarce su da su yi aiki tare da shugabannin su don inganta ilimi, kiwon lafiya, noma, da kuma ci gaban bil’adama.
Gwamna Yusuf ya umurci kansilolin da su fito da ayyukan da za su amfanar da unguwanninsu, wadanda za a aiwatar da su ne domin amfanin kowa da kowa.
Kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu Muhammad Tajuddeen ya yabawa kokarin kansilolin kananan hukumomin wajen gudanar da harkokin kananan hukumominsu.
Ya bukace su da su ci gaba da marawa manufofin gwamnati baya tare da tabbatar da sun sanar da masu zabe wadannan manufofin.
Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Falgore, ya shawarci shugabannin kananan hukumomin da su yi aiki tare da shugabanninsu domin cimma manufofinsu.
Ya kuma yi kira ga gwamnan da ya duba albashi da alawus-alawus na kansilolin kananan hukumomin domin kara musu kwarin gwiwa.
Shugabar Kungiyar Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON) reshen Jihar Kano, Hajiya Saadatu Yusha’u, ta yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na taba rayuwar ‘yan Kano ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
Shugaban kungiyar kansilan Arewa maso Yamma, Bashir Shehu Achika, ya yaba da kokarin gwamnati mai ci na samar da ababen more rayuwa ga talakawa.
Ya yi nuni da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna jajircewarsa na tallafawa kananan hukumomi ta hanyar ware kudade don gudanar da ayyuka don jin dadin jama’a.
Achika ya roki gwamnatin jihar da ta shirya wani taron karawa juna sani domin bunkasa kwarjinin kansilolin kananan hukumomi domin gudanar da ayyuka masu inganci.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Kabir Yusuf
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Ta wadanne hanyoyi cutar Kansa ke farawa?
Kowace kwayar halitta ta jikin mutum akwai aikin da take yi, asalin kwayar halittar ta kan kasu kashi-kashi; suna mutuwa idan aka fitar da su ko kuma suka lalace, sai wata kwayar ta maye gurbinsu. A irin wannan lokaci ne, Kansar ke samun gurin zama sai ta zuba tata kwayar halittar ta kori asalin kwayar halittar da ke jikin Dan’adam, wanda hakan ke jawo matsaloli a sassan jikin da Kansar ta kama.
Saboda haka, kwayar cutar Kansa; ta kan watsu a sauran sassan jiki, misali Kansar huhu ta kan tafi cikin kasusuwa ta girma, a yayin da kwayar ta yadu; ana kiranta da suna ‘meh-TAS-tuh-sis’, ita kuma Kansar huhu idan ta tafi cikin kasusuwa; ana kiran ta da suna ‘Lung Cancer’ a turance. A bangaren likitoci, kwayar cutar Kansar da ta shiga cikin kashi; daidai ta ke da ta huhu, sai dai idan ta yadu a cikin kashin.
Banbance-banbancen cutar Kansa:
Wata Kansar ta kan yadu ne cikin gaggawa, yayin da kuma wata ta ke yaduwa a hankali a hankali, sannan kowacce ana iya yin maganinta ta hanyoyi daban-daban, wata ta hanyar tiyata kadai za a iya samun waraka; wata kuma ta hanyar shan magani.
Idan mutum yana dauke da Kansa, likita ya kan yi kokari wajen gano irin Kansar da yake dauke da ita. Mutanen da ke da cutar Kansa, ana yi musu magani ne gwargwadon irin yanayin wadda suke dauke da ita.
Wane matsayi cutar Kansa ta taka?
Duk wanda ke dauke da wannan cuta ta Kansa, likita zai so sanin matakin da ta kai, daga inda ta fara ana kiran sa a turance ‘Cancer Stage’, sannan matsayin da Kansar ta ke shi ne zai taimaka wajen sanin maganin da za a dora mai dauke da lalurar a kai.
Kowace irin Kansa, akwai gwajin da ake yi domin gano matasayin da ta kai. A dokar gwajin matakinta na farko da kuma mataki na biyu, na nuna Kansar ba ta yi karfi sosai ba. Mataki na uku da na hudu kuma yana nuna ta yadu sosai. Mataki na hudu shi ne makura wajen yaduwar ta.
Alamomin 20 Na Kamuwa Da Cutar Kansa:
1- Shashsheka da karancin numfashi
2- Tari da ciwon kirji, alama ce ta Kansar huhu ko ta bargo ciwon kirjin kan kasance daga kirjin zuwa kafada, sannan ya sauko zuwa hannu
3- Zazzabi da saurin kamuwa da ciwo, hakan na faruwa ne dalilin asalin kwayar halittar jinin mutum ta tabu
4- Fama wajen hadiye abu, wannan na nuni da an kamu da wannan cuta
5- Futowar kurji me ruwa a wuya, hammata da kuma gwiwa
6- Yawan zubda jini
7- Kasala da yawan gajiya
8- Kumburin ciki
9- Rashin sha’awar abu da kuma daukewar dandano
10- Ciwon ciki da mara
11- Fitar jini daga dubura
12- Rama lokaci guda
13- Yawan ciwon ciki
14- Nono ya yi ja ya kumbura alama ce ta ‘breast cancer’
15- Canjawar kan nono
16- Nauyi da kuma ciwo na fitar hankali a lokacin al’ada, wannan ita ma alama ce ta ‘uterus cancer’, ana bukatar yin hoto (transbiginal)
17- Kumburin fuska
18- Canjawar farce, zai iya kasancewa ‘lung cancer’, idan kuma ya kode ya yi fari to ‘liber cancer’ ne
19- Ciwon baya a bangaren dama, yana nuni da ‘liber cancer’ ko ‘breast cancer’
20-Fesowar kuraje a jikin mutum
Amma sai an je asibiti an ga likita kafin a tabbatar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA