Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umurci shugabannin kananan hukumomin jihar 44 da su tabbatar da cewa Kansilolinsu sun shiga dukkan ayyukan da aka gudanar a kananan hukumominsu .

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da kansilolin kananan hukumomi 484 daga kananan hukumomi 44 na jihar.

 

Taron wanda ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, da nufin karfafa alaka tsakanin gwamnatin jihar da majalisun kananan hukumomi.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa tana da hankali kuma ba ta da almundahana, kuma ba za a amince da duk wani nau’i na almundahana ba.

 

Ya kuma bukaci kansilolin da su yi aiki tukuru don ganin sun rike amanar da aka ba su.

 

Gwamnan ya shawarce su da su yi aiki tare da shugabannin su don inganta ilimi, kiwon lafiya, noma, da kuma ci gaban bil’adama.

 

Gwamna Yusuf ya umurci kansilolin da su fito da ayyukan da za su amfanar da unguwanninsu, wadanda za a aiwatar da su ne domin amfanin kowa da kowa.

 

Kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu Muhammad Tajuddeen ya yabawa kokarin kansilolin kananan hukumomin wajen gudanar da harkokin kananan hukumominsu.

 

Ya bukace su da su ci gaba da marawa manufofin gwamnati baya tare da tabbatar da sun sanar da masu zabe wadannan manufofin.

 

Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Falgore, ya shawarci shugabannin kananan hukumomin da su yi aiki tare da shugabanninsu domin cimma manufofinsu.

 

Ya kuma yi kira ga gwamnan da ya duba albashi da alawus-alawus na kansilolin kananan hukumomin domin kara musu kwarin gwiwa.

 

Shugabar Kungiyar Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON) reshen Jihar Kano, Hajiya Saadatu Yusha’u, ta yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na taba rayuwar ‘yan Kano ba tare da la’akari da matsayinsa ba.

 

Shugaban kungiyar kansilan Arewa maso Yamma, Bashir Shehu Achika, ya yaba da kokarin gwamnati mai ci na samar da ababen more rayuwa ga talakawa.

 

Ya yi nuni da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna jajircewarsa na tallafawa kananan hukumomi ta hanyar ware kudade don gudanar da ayyuka don jin dadin jama’a.

 

Achika ya roki gwamnatin jihar da ta shirya wani taron karawa juna sani domin bunkasa kwarjinin kansilolin kananan hukumomi domin gudanar da ayyuka masu inganci.

 

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Kabir Yusuf

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce dole ne dukkan kasashen duniya su yi kokarin kawo karshen laifukan da Isra’ila ke aikatawa a zirin Gaza da kuma kawo karshen killacewa da take yi wa yankin.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin da yake karbar takardar shaidar sabbin jakadun kasashen Habasha, Estonia, Djibouti, Laos, Cambodia, Burundi, Latvia, Myanmar, da Nepal.

Ya ce gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da  kara zafafa laifukan da take aikatawa a kan al’ummar Palastinu marasa kariya da ake zalunta a zirin Gaza.

Shugaban na Iran ya jaddada cewa: Dole ne dukkan kasashen duniya musamman kasashen musulmi su kara himma da hadin gwiwa wajen dakile wadannan laifuka a Gaza, da kuma isar da  taimako mai yawa ga mutanen Gaza.

Ya yi gargadin cewa wani “mummunan bala’i” yana faruwa a Gaza, inda Isra’ila ke kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, tare da toshe hanyoyin samun abinci, ruwa, da magunguna da sunan kare kai.

“Babban abin bakin ciki shi ne ana aikata wadannan laifuka a kan idanun wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama, dimokuradiyya, da ‘yancin dan adam a duniya,” in ji Pezeshkian.

Yakin Isra’ila, wanda ya fara a watan Oktoban 2023, ya yi sanadin shahadar Falasdinawa akalla 61,430 tare da jikkata sama da 153,213.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Wani Hari Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Babu wani abu da aka yanke game da tattaunawa da Washington August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
  • Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza