Dole Ne Kansiloli Su Shiga Cikin Dukkan Ayyukan Kananan Hukumomin Su – Gwamna Yusuf
Published: 14th, May 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umurci shugabannin kananan hukumomin jihar 44 da su tabbatar da cewa Kansilolinsu sun shiga dukkan ayyukan da aka gudanar a kananan hukumominsu .
Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da kansilolin kananan hukumomi 484 daga kananan hukumomi 44 na jihar.
Taron wanda ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, da nufin karfafa alaka tsakanin gwamnatin jihar da majalisun kananan hukumomi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa tana da hankali kuma ba ta da almundahana, kuma ba za a amince da duk wani nau’i na almundahana ba.
Ya kuma bukaci kansilolin da su yi aiki tukuru don ganin sun rike amanar da aka ba su.
Gwamnan ya shawarce su da su yi aiki tare da shugabannin su don inganta ilimi, kiwon lafiya, noma, da kuma ci gaban bil’adama.
Gwamna Yusuf ya umurci kansilolin da su fito da ayyukan da za su amfanar da unguwanninsu, wadanda za a aiwatar da su ne domin amfanin kowa da kowa.
Kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu Muhammad Tajuddeen ya yabawa kokarin kansilolin kananan hukumomin wajen gudanar da harkokin kananan hukumominsu.
Ya bukace su da su ci gaba da marawa manufofin gwamnati baya tare da tabbatar da sun sanar da masu zabe wadannan manufofin.
Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Falgore, ya shawarci shugabannin kananan hukumomin da su yi aiki tare da shugabanninsu domin cimma manufofinsu.
Ya kuma yi kira ga gwamnan da ya duba albashi da alawus-alawus na kansilolin kananan hukumomin domin kara musu kwarin gwiwa.
Shugabar Kungiyar Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON) reshen Jihar Kano, Hajiya Saadatu Yusha’u, ta yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na taba rayuwar ‘yan Kano ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
Shugaban kungiyar kansilan Arewa maso Yamma, Bashir Shehu Achika, ya yaba da kokarin gwamnati mai ci na samar da ababen more rayuwa ga talakawa.
Ya yi nuni da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna jajircewarsa na tallafawa kananan hukumomi ta hanyar ware kudade don gudanar da ayyuka don jin dadin jama’a.
Achika ya roki gwamnatin jihar da ta shirya wani taron karawa juna sani domin bunkasa kwarjinin kansilolin kananan hukumomi domin gudanar da ayyuka masu inganci.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamna Abba Kabir Yusuf
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
Aƙalla jihohi 11 na Najeriya sun kashe sama da Naira biliyan 6.2 wajen tallafa wa Alhazansu domin sauƙaƙa musu wajen zama a ƙasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Wannan tallafi ya haɗa da kuɗi, jakunkunan tafiya, da kuma sayen raguna na hadaya domin sallar Layya.
Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APCGwamnatin Jihar Sakkwato ce ta fi kowa bayar da tallafi mafi yawa, inda Gwamna Ahmed Aliyu, ya bai wa kowane daga cikin alhazai 3,200 na jihar Riyal 1,000 (kimanin Naira 450,000).
A Kano kuwa, kowane alhaji daga cikin alhazai 3,345 sun samu kyautar Riyal 50.
Gwamnatin Jihar Legas ta bai wa kowane daga cikin alhazai 1,315 Riyal 180 (kimanin N74,870), yayin da Jihohin Jigawa da Kebbi suka bayar da mafi ƙarancin adadi.
Wani jami’in Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana cewa: “Kowane Alhaji ya samu Riyal 180 a matsayin kyauta don sauƙaƙa rayuwarsu a lokacin aikin hajji.”
Jihar Borno ba ta bayar da kuɗi ba, amma ta biya kuɗin ragunan layya (hadaya) na Alhazan jihar guda 2,174.
Haka kuma, hukumomin Kano sun sanar da cewa kowane Alhaji zai samu babbar jakar tafiya domin dawowarsa gida cikin sauƙi.
Sai dai masana da malamai sun soki irin wannan kashe-kashen kuɗi da gwamnati ke yi, inda suka bayyana hakan a matsayin almubazzaranci da rashin fifita abin da ya fi muhimmanci.
Farfesa Yahaya Tanko, masani a harkokin siyasa, ya ce: “Wannan ba fifiko ba ne. Ya kamata gwamnoni su mayar da hankali kan matsalolin tsaro da talauci, ba tare da kashe kuɗi kan aikin hajji ba.”
Ya ƙara da cewa: “Al’umma na fama da sace-sace, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu, amma gwamnoni na kashe miliyoyi kan aikin Hajji. Wannan ba daidai ba ne.”
Hakazalika, babban malamin addini, Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce: “Kuɗaɗen da aka kashe a kan Hajji za a iya amfani da su wajen taimaka wa ‘ya’yan Alhazai su yi karatu. Wannan zai amfanar da iyalai da kuma al’umma gaba ɗaya.”
Mutane da dama a kafafen sada zumunta sun bayyana irin wannan kashe kuɗi a matsayin rashin adalci ga talakawa.
Wasu sun ce aikin Hajji ibada ce da ya kamata mutum ko al’umma su ɗauki nauyinta da kansu, ba gwamnati ba.
Yanzu haka ana ta kira ga gwamnoni da su dawo da hankali kan tsaro, kiwon lafiya, da ilimi domin hakan ne zai amfani mafi yawan jama’a, ba wasu ƙalilan da suka samu damar zuwa aikin Hajji kawai ba.