Jami’ar Colombiya Ta Birnin New York A Amurka Ta Dakatar Da Karatun Daliban Jami’ar Fiye Da 65
Published: 10th, May 2025 GMT
Hukumomi a Jami’ar Colombia dake birnin NewYork na kasar Amurka sun bada sanarwan cewa, sun dakatar da karatun daliban jami’ar fiye da 65 saboda shiga cikin zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a kusa da babban dakin ajiyar littafai ko karatu a Jami’ar a ranar Laraban da ta gabata.
Tashar talabijin ta Press tv a nan Tehran ta nakalto kakakin Jami’ar a jiya Jumma’a na cewa a ranar Laraba yansandan NewYork sun kama talibai kimani 80 inda suke tsare da su, a halin yanzu suke kuma ci gaba da gudanar da bincike a kansu.
Labarin ya kara da cewa akwai wasu karin mutane 33 wadanda Jami’ar ta dakatar saboda hannun a cikin zanga-zangar goyon bayan Falasdinawar.
Labarin ya bayyana cewa hotunan bidiyo na tsaro a dakin karatu na Jami’ar sun nuna daliban suna shiga dakin sannan jami’an tsaro suna binsu suna kamawa, sannan wasu daga cikinsu na sanye da ‘Keffiyeh’ wani kelle wanada yake nuna alamar Falasdinawa.
Jami’o’ii da dama a Amurka suna gudanar da irin wannan zanga-zangar, don nuan rashin amincewarsu da kissan kiyashen da HKI take yi a gaza tun shekara ta 2023 ya zuwa yanzu, da kuma tallafa mata wanda gwamnatin kasar ta Amurka take yi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Fiye Da Falasdinawa 900,000 Ne Su Ka Yi Hijira A Cikin Gaza
HKI tana ci gaba da kai wa muhimman cibiyoyi da gidajen Falasdinawa a fadin Gaza.
Majiyar Falasdinawa ta ce daga safiyar yau Laraba adadin wadanda su ka yi shahadar sun kai 45 sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin ‘yan sahayoniyar su ka kai.
Har ila yau an sami wasu Karin shahidan biyar a wuraren karbar agaji dake arewacin Rafaha.
A wani labarin mai alaka da hakan shugaban hukumar lafiya ta duniya ( w.h.o) Tedross Adhanom ya ce; Kai hare-haren da ake yi a kusa da asibitin Rantisy, dake Gaza, ya yi sanadiyyar tsayuwar aikin Asibiti, domin rashin tsaro.
Har ila yau ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta kara da cewa; Jinkirin shigar da makamashi zuwa yankin yana barazanar tsayar da aikin injinan da suke bayar da wuta a asibitin idanu,wanda yake yi wa mutane da dama aiki.
Ofishin hukuma a Gaza ya sanar da cewa, mutanen da sun kai 900,000 sun fice daga gidajensu amma kuma suna ci gaba da riko da ci gaba da zamansu a cikin kasarsu.
Bugu da kari, ‘yan mamayar suna ci gaba da tilastawa mutanen na Gaza ficewa daga gidajensu, zuwa yankunan kudancin Gaza, ta hanyar kai musu hare-hare.
Haka nan kuma da akwai wasu Karin mutanen 334,000 da aka fitarsa fita daga gidajensu a cikin kwanaki uku, da hakan ya sa yawansu ya kai 60,000.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Imam Khamenei: Hadin kan al’ummar Iran a yakin kwanaki 12 ya sanya makiya kunya September 24, 2025 Larijani: Iran na kare tsaron kasa da azama September 24, 2025 Jagora: Iran Ba Za Ta Taba Yin Watsi Da Inganta Sinadarin Uranium Ba September 24, 2025 Larijani: Iran Tana Nazarin Shawarwarin Turai Da Na Rasha Domin Kare Muradunta September 24, 2025 Araqchi; Iran Da Norway Sun Tattaunawa Batun kyakkyawar Alakar Da Ke Tsakaninsu September 24, 2025 Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran September 24, 2025 Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa Daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya September 24, 2025 Imam Khamenei Zai Yi Jawabi Ga mutanen Iran A Cikin Makon Tsaro Da Ya Shigo September 23, 2025 Lebanon: A yau Ne Aka Yi Jana’izar Shahidan Bitij Bail Wadanda HKI Ta Kai Ga Shahada A Ranar Lahadi September 23, 2025 Pezeshkiyan Ya Ce Tattaunawa Da Kasashe Masu Nuna Karfi Kan Wasu Ba Zai Taba Yi Yuwa Ba September 23, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci