Idris ya ce: “Wannan ba kawai ƙaddamar da littafi ba ne, amma bikin rayuwa da jarumtaka, daidaito, da jajircewa ga tsarin dimokiraɗiyya suka bayyana.

 

“Ko da yake Alhaji Sule Lamiɗo babban jigo ne a jam’iyyar adawa kuma sau da dama mai suka ga gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), har yanzu yana daga cikin manyan ginshiƙai na cigaban siyasar Nijeriya.

 

Ministan ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ya yarda da siyasar da ke bai wa kowa dama, inda ake maraba da ra’ayoyi mabanbanta, kuma suna da muhimmanci ga tattaunawa kan makomar ƙasa.

 

“Kowane ɗan ƙasa, ba tare da la’akari da dangantakar sa da jam’iyya ba, yana da gurbin zama a teburin tattaunawa kan makomar ƙasa.”

 

Idris ya jinjina wa ƙoƙarin da Lamiɗo ya yi na fiye da shekaru goma wajen rubuta littafin, yana mai cewa ya taka rawar gani wajen adana tarihi, kuma ya buƙaci sauran tsofaffin ‘yan siyasa da su bi irin wannan hanya.

 

Ya kuma ce taken littafin, wato ‘Being True to Myself,’ ya dace da halayen Lamiɗo.

 

Ya ce: “Ya dace da halin Sule Lamiɗo da kuma sunan da yake da shi na ɗan siyasa mai aƙida da nuna ra’ayi kai-tsaye.

 

“Zan shawarci ɗalibai, malamai, ‘yan jarida, da sauran ‘yan siyasa da su karanta littafin don za su ga littafin yana da amfani a gare su na tsawon shekaru.”

 

Idris ya ƙara da cewa shi ma Shugaba Tinubu, kamar Lamiɗo, ya jajirce kan gaskiya, adalci, zaman lafiya da cigaban ƙasa.

 

Ya ce: “Ɗimbin ilimi da ƙwarewar marubucin, tabbas, wata baiwa ce da ya kamata duniya ta amfana da ita, kuma abin farin ciki ne ganin ya ɗauki mataki ya wallafa littafi.”

 

Yayin da Nijeriya take shirin cika shekaru 26 da dimokiraɗiyya, ministan ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa – duk da yake masu tsauri ne – sun fara haifar da sakamako mai kyau a fannin tattalin arziki.

 

Ya ce: “Shin muna cewa mun kai inda ya kamata mu kai, kuma babu sauran aikin da ya rage? A’a, ko kaɗan. Abin da muke cewa mai sauƙi ne: cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna ƙarfin hali da hangen nesa na musamman wajen ɗora Nijeriya a kan hanyar cigaba da bunƙasa na gaskiya.

 

“Kuma, bayan wata farawa mai ɗan wahala saboda tsauraran sauye-sauyen da ba za a guje masu ba, yanzu muna shiga wani sabon zamani na samun sakamakon alheri da aka yi niyya.”

 

Game da matsalar tsaro, ministan ya tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa yana aiki tuƙuru wajen kare rayuka da ƙasa daga barazanar ‘yan ta’adda.

 

“Don haka muna son jaddada buƙatar a yaba da sadaukarwar da sojojin Nijeriya suke yi a wannan fanni,” inji shi.

 

Ya kuma bayyana cewa sababbin dokokin haraji da Shugaban Ƙasa ya gabatar suna nufin haɓaka kuɗaɗen shiga ga gwamnatoci a matakai daban-daban ba tare da ƙara wa talakawa nauyi ba.

 

“Shugaban Ƙasa yana maraba da suka mai ma’ana a kowane lokaci, cikin ruhin ’yancin faɗar albarkacin baki da dimokiraɗiyya, amma ba zai taɓa bari a karkatar da shi daga aikata abin da ya dace da Nijeriya ba.”

 

Manyan baƙi daga bangarori daban-daban na siyasa sun halarci taron don girmama tsohon gwamnan da kuma yin nazari kan gudunmawar da ya bayar wajen gina dimokiraɗiyya a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

Shugaban ya ci gaba da cewa, a karkashin shugabancinsa, Hukumar za ta yi namijin kokari wajen bayar da goyon bayanta, wajen fitar da kayan da ba su shafi dangogin Mai ba, zuwa kasar waje, musamman ta hanyar cin giyar albakatun yanayin na Abuja da kuma na bangaren aikin noma, da birnin ke da shi. Ya kara da cewa, ta hanyar wadannan alkatun kasar da birnin ke da su, Hukumar za ta kara bayar da gudunmwarta, wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar nan da kuma kara fitar da kayan da ba su shafi Man ba, zuwa ketare.

 

A cewarsa, domin Hukumar ta tabbatar da na kara mayar da hankalin wajen ganin ana bin ka’ida da kuma tabbatar da ingancin gudanar da ayyukanta, ta kirkiro da tsare-tsare na fasahar zamani na bai daya da ake kira a turance, PCS da kuma NSW.

A cewarsa, wadannan fasahar ta zamani, za su taimaka wajen hada masu ruwa da tsaki a fannin da ke fitar da kaya zuwa ketare tare da kuma rage jinkiri wajen fitar da kayan waje da kuma samar da kyakyawan yanayi ga masu fitar da kayan ketare.Shugaban ya sanar da cewa, Hukumar na alfaharin danganta manta da ayyukan da Cibiyar ta kolin kasuwanci ta Abuja ke ci gaba da gudanarwa musamman a bangaren kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

Dantsoho ya kuma gayyaci masu ruwa da tsaki a fannin kar su bari a barsu a baya, wajen cin gajiyar saukin da Hukumar ta samar na fitar da kaya daga cikin kasar nan, zuwa ketare.

Kazalika, Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar ta kuma samar da tsarin fasahar zamani na fitar da kaya a cikin sauki a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar wato EPT.

Ya kara da cewa, wannan fasahar ta taimaka matuka wajen fitar da kaya waje ba tare da wani tarnaki ba.

Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta kuma fadada fasahar ta EPT, domin samar da saukin fitar da kaya ga kananan da matsakaitan masana’antun kasar suka sarrafa, domin fitar da su ketare.

Hakazalika, Shugaban ya bayyana cewa, domin ayyukan Hukumar su tafi kafada da kafada da kudurin Gwamnatin Tarayya NPA ta saita gudanar da ayyukanta ta hanyar yin amfani da fasahar ta zamani ta PCS.

A cewarsa, wannan zai tabbatar da samar da wani ginshike ga fasahar NSW, inda za a rinka fitar da kayan waje, ba tare da wata matsala ba.

Dantsoho ya yi nuni da cewa, fasahar ta NSW aba ce, da ake yin amfani da da ita, a daukacin fadin duniya, wajen samar da saukin fitar da kaya waje.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Hukumar na daukar Malamai wajen ganin cewa, ayyukanta, sun kai da lungu da sako, da ke da wuyar isa a kasar.

Ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yau, kofar Hukumar a bude take domin yin hadaka da su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025 Tattalin Arziki Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho