Aminiya:
2025-06-18@01:46:38 GMT

JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa

Published: 14th, May 2025 GMT

Shugaban Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB), Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana cewar an samu kura-kurai a sakamakon jarrabawar UTME ta shekarar 2025 da aka saki kwanan nan.

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, Farfesa Oloyede, ya fashe da kuka yayin da yake bai wa ɗalibai haƙuri, inda ya nuna nadamarsa kan wahalar da suka sha.

Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara 

A cewar JAMB, matsalolin fasaha sun shafi sakamakon ɗalibai 379,997.

Waɗannan matsaloli sun fi shafar jihohin Kudu maso Gabas da kuma Jihar Legas.

A Legas, ɗalibai 206,610 daga cibiyoyi 65 ne suka fuskanci matsalar, yayin da ɗalibai 173,387 daga jihohi biyar na Kudu maso Gabas suka fuskanci irin wannan matsala a cibiyoyi 92.

Baya ga kura-kuran, mafi yawan ɗaliban da suka zana jarrabawar ba su samu makin da ake buƙata ba.

Daga cikin sama da ɗalibai miliyan 1.96 da suka rubuta jarrabawar, sama da miliyan 1.5 sun samu maki ƙasa da 200 daga cikin maki 400.

Ƙalilan daga cikin ɗaliban ne suka samu maki sama da 300.

Wannan sakamako ya tayar da hankali kan matsayin ilimi da yadda ake shiryawa ɗalibai jarrabawa.

JAMB ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan matsalolin fasaha da suka auku, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan da suka dace domin kauce wa faruwar hakan nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Ɗalibai Jarrabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu

Martanin Iran game da ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila na ci gaba a rana ta biyu

Ana ci gaba da mayar da martani mai girma na Iran game da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki.

‘Yan mintoci da suka gabata a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya Na 3”, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta harba daruruwan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan haramtacciyar kasar Isra’ila.

An harba wadannan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki da kuma jiragen sama masu saukar ungulu daga Tehran da sauran garuruwan kasar Iran a matsayin wani mataki na murkushe laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a kan yankunan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya na 3”.

Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun watsa rahoton tashin gobara da hayaki a birnin Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye.

An ga wuta da hayaki na tashi bayan da makamai masu linzami na Iran sun afkawa matatar mai ta Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye. Sannan a cewar bayanan farko, an kashe fiye da mutane 10 a Haifa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB
  • Palermo ta ɗauki Filippo Inzaghi
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu