Aminiya:
2025-06-29@08:26:23 GMT

JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa

Published: 14th, May 2025 GMT

Shugaban Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB), Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana cewar an samu kura-kurai a sakamakon jarrabawar UTME ta shekarar 2025 da aka saki kwanan nan.

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, Farfesa Oloyede, ya fashe da kuka yayin da yake bai wa ɗalibai haƙuri, inda ya nuna nadamarsa kan wahalar da suka sha.

Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe ’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara 

A cewar JAMB, matsalolin fasaha sun shafi sakamakon ɗalibai 379,997.

Waɗannan matsaloli sun fi shafar jihohin Kudu maso Gabas da kuma Jihar Legas.

A Legas, ɗalibai 206,610 daga cibiyoyi 65 ne suka fuskanci matsalar, yayin da ɗalibai 173,387 daga jihohi biyar na Kudu maso Gabas suka fuskanci irin wannan matsala a cibiyoyi 92.

Baya ga kura-kuran, mafi yawan ɗaliban da suka zana jarrabawar ba su samu makin da ake buƙata ba.

Daga cikin sama da ɗalibai miliyan 1.96 da suka rubuta jarrabawar, sama da miliyan 1.5 sun samu maki ƙasa da 200 daga cikin maki 400.

Ƙalilan daga cikin ɗaliban ne suka samu maki sama da 300.

Wannan sakamako ya tayar da hankali kan matsayin ilimi da yadda ake shiryawa ɗalibai jarrabawa.

JAMB ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan matsalolin fasaha da suka auku, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan da suka dace domin kauce wa faruwar hakan nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Ɗalibai Jarrabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ganduje, wanda ya kasance Gwamnan Jihar Kano daga 2015 zuwa 2023, ya zama shugaban APC a watan Agustan 2023 bayan murabus ɗin tsohon shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu daga yankin Arewa ta Tsakiya.

Tun daga wannan lokacin ne wasu daga cikin mambobin jam’iyyar suka fara sukar jagorancinsa, suna ganin naɗa shi ya karya tsarin raba muƙamai na cikin gida da jam’iyyar ke bi.

Dama tuni wasu manyan dattawan jam’iyyar da shugabannin yankuna daban-daban suka bayyana rashin jin daɗinsu, inda suka dk ga kira ga jam’iyyar da ta gyara wannan tsari.

Majiyoyi sun ce saukar Ganduje za ta samar da haɗin kai a cikin jam’iyyar, da kuma gyara matsalolin rabon muƙamai don sake farfaɗo da APC kafin babban zaɓen 2027.

A halin yanzu, babu wata sanarwa da Ganduje ko jam’iyyar APC ta fitar kan murabus ɗinsa.

Murabus ɗin na Ganduje na nuna wani babban sauyi a shugabancin jam’iyyar APC tun bayan hawan mulkin Shugaba Bola Tinubu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
  • Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
  • Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO
  • ‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2
  • WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe