JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa
Published: 14th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB), Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana cewar an samu kura-kurai a sakamakon jarrabawar UTME ta shekarar 2025 da aka saki kwanan nan.
A yayin wani taron manema labarai a Abuja, Farfesa Oloyede, ya fashe da kuka yayin da yake bai wa ɗalibai haƙuri, inda ya nuna nadamarsa kan wahalar da suka sha.
A cewar JAMB, matsalolin fasaha sun shafi sakamakon ɗalibai 379,997.
Waɗannan matsaloli sun fi shafar jihohin Kudu maso Gabas da kuma Jihar Legas.
A Legas, ɗalibai 206,610 daga cibiyoyi 65 ne suka fuskanci matsalar, yayin da ɗalibai 173,387 daga jihohi biyar na Kudu maso Gabas suka fuskanci irin wannan matsala a cibiyoyi 92.
Baya ga kura-kuran, mafi yawan ɗaliban da suka zana jarrabawar ba su samu makin da ake buƙata ba.
Daga cikin sama da ɗalibai miliyan 1.96 da suka rubuta jarrabawar, sama da miliyan 1.5 sun samu maki ƙasa da 200 daga cikin maki 400.
Ƙalilan daga cikin ɗaliban ne suka samu maki sama da 300.
Wannan sakamako ya tayar da hankali kan matsayin ilimi da yadda ake shiryawa ɗalibai jarrabawa.
JAMB ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan matsalolin fasaha da suka auku, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan da suka dace domin kauce wa faruwar hakan nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Afuwa Ɗalibai Jarrabawa
এছাড়াও পড়ুন:
ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
Biyo bayan wani rahoto da ma’aikatar lafiya ta tarayya ta fitar na cewa sama da likitoci 16,000 ne suka bar Najeriya a cikin shekaru bakwai da suka gabata domin neman aiki a wasu kasashe, gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri na cike gurbin da likitocin suka haifar.
Da yake zantawa da manema labarai a Katsina, Shugaban Hukumar Kula da Ilimi ta Kasa (TETFund), Alhaji Aminu Bello Masari, ya ce hukumar ta kaddamar da wani shiri na musamman domin horar da karin likitoci, ma’aikatan jinya, masu harhada magunguna da kwararrun dakin gwaje-gwaje a manyan makarantun kasar nan.
Ya ce tuni hukumar ta TETFUND ta zuba sama da Naira biliyan 100 a manyan makarantu goma sha takwas domin kara karfinsu na horar da dalibai a fannin ilimin likitanci, ta hanyar samar da dakunan karatu, dakunan gwaje-gwaje da sauran abubuwan da suka shafi ababen more rayuwa da ilimi.
Masari ya ce, wannan matakin shiri ne don ba da damar tsarin kiwon lafiya ya farfado daga ficewar ma’aikatan lafiya tare da kara karfin ma’aikata a fannin.
Ya bayyana cewa an zabo manyan makarantu guda uku a kowace shiyyar siyasar kasar nan saboda kowace cibiya ta samu Naira biliyan 4 don gudanar da ayyuka da kuma sayan kayan aikin da ake bukata domin kara karfin daukar dalibai da horar da dalibai a fannin ilimin likitanci.
Masari ya bayyana cewa sun dauki matakin ne saboda muradin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na ganin an magance karancin ma’aikata a fannin kiwon lafiya da ke yin illa ga ayyukan hidima a fannin.
“A shekarun baya-bayan nan, likitoci da ma’aikatan jinya da yawa da masana harhada magunguna da kwararrun likitoci da sauran kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sun bar kasar nan don neman aiki mai gwabi a kasashen waje.
Isma’il Adamu/Katsina