JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa
Published: 14th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB), Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana cewar an samu kura-kurai a sakamakon jarrabawar UTME ta shekarar 2025 da aka saki kwanan nan.
A yayin wani taron manema labarai a Abuja, Farfesa Oloyede, ya fashe da kuka yayin da yake bai wa ɗalibai haƙuri, inda ya nuna nadamarsa kan wahalar da suka sha.
A cewar JAMB, matsalolin fasaha sun shafi sakamakon ɗalibai 379,997.
Waɗannan matsaloli sun fi shafar jihohin Kudu maso Gabas da kuma Jihar Legas.
A Legas, ɗalibai 206,610 daga cibiyoyi 65 ne suka fuskanci matsalar, yayin da ɗalibai 173,387 daga jihohi biyar na Kudu maso Gabas suka fuskanci irin wannan matsala a cibiyoyi 92.
Baya ga kura-kuran, mafi yawan ɗaliban da suka zana jarrabawar ba su samu makin da ake buƙata ba.
Daga cikin sama da ɗalibai miliyan 1.96 da suka rubuta jarrabawar, sama da miliyan 1.5 sun samu maki ƙasa da 200 daga cikin maki 400.
Ƙalilan daga cikin ɗaliban ne suka samu maki sama da 300.
Wannan sakamako ya tayar da hankali kan matsayin ilimi da yadda ake shiryawa ɗalibai jarrabawa.
JAMB ta bayyana cewa tana gudanar da bincike kan matsalolin fasaha da suka auku, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan da suka dace domin kauce wa faruwar hakan nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Afuwa Ɗalibai Jarrabawa
এছাড়াও পড়ুন:
Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
Sakamakon farko na zaben shugaban kasar Jamhuriyar Kamaru da ake ci gaba da kirgawa ya nuna jagoran adawa, Issa Tchiroma Bakary, ya samu gagarumin rinjaye a yankunan da a bayan Shugaba Paul Biya ya saba rinjaye.
Shugaba Paul Biya mai shekaru 92 yana fuskantar abokan hamayya 11 cikin har da tsofaffin mukarrabansa, da ma tsoffin ministocinsa da ke neman kujerarsa da ya shafe shekara 43 a kai kuma yake namen wa’adi na takswas.
Cikinsu har da tsohon Ministan Yawon Bude Ido, Bello Bouba Maigari, da tsohon ministan Ayyuka, Bakary, wanda ya yi murabus a watan Yuli domin shiga takara kuma ya sama mafi shahara bayan doka ta haramta wa madugun adawa Maurice Kamto shiga zaben..
Biya ya ki yin tsokaci game da nasarar a lokacin da ya jefa kuri’arsa a birnin Yaounde ranar Lahadi, amma sakamakon farko sun nuna jam’iyyar FSNC wadda Bakary ya tsaya takara ta samu galaba a yankin da a bayan jam’iyyar CPDM ta Shugaba Biya ke da rinjaye.
Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a BornoWani dan jarida da ke aikin sa ido kan zaben shaida wa wakilimu cewa jam’iyyar FSNC ta samu rinjaye a yawancin runfunan zaben da ke larduna bakwai na birnin Yaounde.
Kowacce daga cikin lardunan na da rumfunan zabe 40 zuwa 50, lamarin da ya mayar da Yaounde fage mai matukar muhimmanci a zaben kasar.
Bakary, wanda dan asalin yankin Garoua ne a yankni Arewa mai Nisa ya kuma doke Bello Maigari a yankin da su biyun suka fito.
Amma duk da haka Jam’iyyar CPDM tana bukatar samun gagarumar goyon bayan a yankin Ambazoniya – Arewa mai nisa da kuma yankin Kudu maso Yamma da kuma Arewa maso Yamma masu amfani da turancin Ingilishi.
Wani dan jarida ya bayyana cewa Bakary ya samu rinjaye a kuri’un da aka jefa a kasashen waje, in banda kasar Rasha.
“Karon farko ke nan tun shekarar 1992 da jam’iyyar adawa ta samu irin wannan rinjaye tun da wuri,” in ji shi.
Wadannan alkaluman wucin gadi ne a yayin da ake jihar Hukuamr Shari’a ta kasar za ta sanar da sakamakon zaben a hukumance cikin makonni biyu da ke tafe.
Ya ci gaba da cewa “Hukumar tana iya sauya sakamakon kuma Kotun Koli tana iya nada duk wanda ta ga ya dace da kujerar.”
Tsarin zaben Kamaru na zagaye daya ne, inda duk wanda ya fi samun kuri’u shi ne ke da nasara.