An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano
Published: 12th, May 2025 GMT
Dubun wani ɗan daba da ƙwacen waya da satar babura a cikin shigar mata mata wajen aikata ayyukan laifinsa a unguwar Ɗorayi da ke Jihar Kano ta cika.
An kama matashin mai suna Abdullahi, wanda aka fi sani da “Audu Manye,” ne bayan tsawon shekaru ana zargin sa da tunzura faɗan ’yan daba, fashi da makami da ƙwace wayoyi da satar babura a yankin.
Audu Manye ya shafe shekaru ya tsere wa jami’an tsaro ta hanyar yin shigar mata da hijabi da siket da da niƙabi, inda yake shiga cikin mata ba tare da an gane shi ba a yayin da yake aikata laifukansa.
Amma a ranar Laraba, dubunsa ta cika, inda haɗin gwiwar ƙungiyar “Gamayyar Matasan Kano,” tare da Kwamitin Tsaro na Al’ummar Ɗorayi, suka yi nasarar rutsa shi tare da kama shi.
Mahara sanye da kayan ’yan sanda sun kashe malami sun sace mata 3 a makaranta a Zamfara Boko Haram ta ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —MajalisaAl’ummar Ɗorayi, waɗanda suka sha fama da yawan faɗan ’yan daba, wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka, raunuka, da lalata dukiyoyi, sun nuna farin cikinsu game da kama ɗan fashin da ya addabe su.
Shugaban ƙungiyar matasan, Muhammad Tijjani Dorayi, ya bayyana wa wani shirin rediyo mai suna “Baba Suda,” cewa “Mun gano cewa wannan ɗan fashin yakan shiga unguwa ne a matsayin mace, sanye da hijabi, ba a gane shi. Da rana, yana harkokinsa kamar kowace mace, inda yake amfani da damar wajen aikata laifukansa ba tare da an gane shi ba.
“Tsawon lokaci, hukumomi sun yi ta neman sa, amma yana tserewa. Amma alhamdulillah ƙwazon matasanmu ya biya, a ƙarshe an kama shi kuma an miƙa shi ga ’yan sanda.”
Shugaban Kwamitin Tsaro na Al’ummar Dorayi, Malam Abdullahi Idris, ya bayyana cewa matashin ya daɗe a cikin jerin waɗanda suke nema ruwa a jallo.
Ya ce wanda ake zargin “yana ɗaya daga cikin fitattun ’yan fashin da suka addabi al’ummarmu. Salonsa na yin shigar mata, wanda ya sa da wuya a iya bibiyar shi, amma a ƙarshe da taimakon matasanmu, mun kama shi.”
Wani mazaunin yankin ya bayyana farin cikinsa da kama Audu Manye da cewa , “Mun daɗe muna rayuwa cikin tsoro saboda mutane irin su Audu Manye. Yakan yi shigar mace, ya shiga gidajen mutane, ya yi sata.
“Wani lokaci ma, yakan tunzura faɗa tsakanin ’yan daba, wanda yakan kai ga mutuwar mutane. Yawancinmu mun gane shi, amma ba mu iya tabbatarwa ba saboda shigarsa. Kama shi zai kawo mana sauƙi,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗorayi Shigar mata shigar mata
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
Daga Bello Wakili
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a duk fadin kasar, sakamakon karuwar kalubalen tsaro da ake fuskanta.
Shugaban ya ce za a dauki sabbin jami’an tsaro nan ba da jimawa ba, wadanda suka hada da na sojiin, ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro — domin karfafa matakan tsaron kasa.
A karkashin sabon umarnin, an bai wa Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ikon daukar karin jami’aaidubu ashirin, wanda hakan zai kawo yawan sabbin jami’an da za a dauka bana zuwa dubu hamsin.
Shugaban kasar ya kuma amince a yi amfani da sansanonin horas da matasa masu yi wa kasa NYSC a matsayin wuraren horaswa na wucin gadi, sakamakon gyare-gyaren da ake yi a makarantun horar da ‘yan sanda a fadin kasar.
Haka zalika Jami’an da aka cire daga ayyukan tsaron manyan mutane za su samu horo na gaggawa kafin a tura su zuwa yankunan da ke da hadari.
Shugaban ya kuma bai wa Hukumar tsaro ta DSS umarnin gaggauta tura dakaru masu horo na musamman zuwa dazuka domin yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga. A don haka, hukumar ta DSS za ta dauki karin ma’aikata don karfafa wannan aiki.
Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya su bada hadin kai ga matakan tsaron da ake dauka.
Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ceto daliban Jihar Kebbi 24 da aka yi garkuwa da su, da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Niger da sauran wadanda ke tsare.
Shugaban ya umurci Rundunar Soji ta kara zafafa ayyuka a dukkan yankunan da ake rikici, tare da jaddada muhimmancin ladabi, gaskiya da kin amincewa da cin hanci ko sakaci.
Ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe a hare-haren da suka faru a Kebbi, Borno, Zamfara, Niger, Yobe da Kwara, tare da karrama jaruman sojojin da suka rasa rayukansu, ciki har da Birgediya-Janar Musa Uba.
Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da goyon bayansa ga jami’an saro na jihohi, tare da kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da ke son kafa ‘yan sandan jiha damar yin hakan.
Ya shawarci gwamnatocin jihohi su sake duba tsarin kafa makarantun kwana a wuraren da ke da nisa ba tare da wadatattun matakan tsaro ba, sannan ya yi kira ga cibiyoyin addini su kara inganta tsaron wuraren ibada.
Dangane da rikice-rikicen manoma da makiyaya, Shugaban ya bukaci kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo na zamani (ranching) tare da yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya ta hannun sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwo.