Aminiya:
2025-10-13@20:04:44 GMT

An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano

Published: 12th, May 2025 GMT

Dubun wani ɗan daba da ƙwacen waya da satar babura a cikin shigar mata mata wajen aikata ayyukan laifinsa a unguwar Ɗorayi da ke Jihar Kano ta cika.

An kama matashin mai suna Abdullahi, wanda aka fi sani da “Audu Manye,” ne bayan tsawon shekaru ana zargin sa da tunzura faɗan ’yan daba, fashi da makami da ƙwace wayoyi da satar babura a yankin.

Audu Manye ya shafe shekaru ya tsere wa jami’an tsaro ta hanyar yin shigar mata da hijabi da siket da da niƙabi, inda yake shiga cikin mata ba tare da an gane shi ba a yayin da yake aikata laifukansa.

Amma a ranar Laraba, dubunsa ta cika, inda haɗin gwiwar ƙungiyar “Gamayyar Matasan Kano,” tare da Kwamitin Tsaro na Al’ummar Ɗorayi, suka yi nasarar rutsa shi tare da kama shi.

Mahara sanye da kayan ’yan sanda sun kashe malami sun sace mata 3 a makaranta a Zamfara Boko Haram ta ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa

Al’ummar Ɗorayi, waɗanda suka sha fama da yawan faɗan ’yan daba, wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka, raunuka, da lalata dukiyoyi, sun nuna farin cikinsu game da kama ɗan fashin da ya addabe su.

Shugaban ƙungiyar matasan, Muhammad Tijjani Dorayi, ya bayyana wa wani shirin rediyo mai suna “Baba Suda,” cewa “Mun gano cewa wannan ɗan fashin yakan shiga unguwa ne a matsayin mace, sanye da hijabi, ba a gane shi. Da rana, yana harkokinsa kamar kowace mace, inda yake amfani da damar wajen aikata laifukansa ba tare da an gane shi ba.

“Tsawon lokaci, hukumomi sun yi ta neman sa, amma yana tserewa. Amma alhamdulillah ƙwazon matasanmu ya biya, a ƙarshe an kama shi kuma an miƙa shi ga ’yan sanda.”

Shugaban Kwamitin Tsaro na Al’ummar Dorayi, Malam Abdullahi Idris, ya bayyana cewa matashin ya daɗe a cikin jerin waɗanda suke nema ruwa a jallo.

Ya ce wanda ake zargin “yana ɗaya daga cikin fitattun ’yan fashin da suka addabi al’ummarmu. Salonsa na yin shigar mata, wanda ya sa da wuya a iya bibiyar shi, amma a ƙarshe da taimakon matasanmu, mun kama shi.”

Wani mazaunin yankin ya bayyana farin cikinsa da kama Audu Manye da cewa , “Mun daɗe muna rayuwa cikin tsoro saboda mutane irin su Audu Manye. Yakan yi shigar mace, ya shiga gidajen mutane, ya yi sata.

“Wani lokaci ma, yakan tunzura faɗa tsakanin ’yan daba, wanda yakan kai ga mutuwar mutane. Yawancinmu mun gane shi, amma ba mu iya tabbatarwa ba saboda shigarsa. Kama shi zai kawo mana sauƙi,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗorayi Shigar mata shigar mata

এছাড়াও পড়ুন:

Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.

Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Rahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.

Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.

Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.

Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.

Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano