Shugaban kungiyar ya yi magana

Ibrahim Yusuf Babayo,Shugaban kungiyar  Miyetti Allah masu kiwon dabbobi na kasa ya bayyanawa jaridar karshen mako cewar dukkan hare- haren da ake kaiwa dabbobin da kuma kashesu an sanar da jami’an tsaro daban- daban,da suka hada da Kwamanda na rundunar soja ta,3 kuma kwamandan Operation Safe Haben (OPSH), Manjo- Janar Foluaho Oyinlola,Kwamishinan‘yansanda na Jihar, Emmanuel Adesina,da kuma darekta na bangaren jami’an farin kaya DSS.

Ya ce jami’an tsaro da suke a bangaren Karamar Hukuma an kai su can wuraren da aka kai hare- haren domin su ganewa idanunsu yadda lamarin yake.

Sa Wa Shanu 110 guba

Kamar yadda jagorancin kungiyar MACBAN a Jihar yace,an kashe Shanu a kalla 110 ta hanyar guba a hare- haren da aka kai daban- daban.

Babayo ya yi zargin cewa an yi amfani ne da gauta, mangwarori da sauran kayan abinci wadanda aka zuba masu guba,aka kuma  zuzzubasu wuraren da ake kiwo saboda dabbobin su ci.Ya kara da cewa masu kai harin suna sau da yawa suna zuba gubar ne wuraren da dabbobin suke zuwa domin shan ruwa.

Lokacin da aka kai hare- haren

Makiyaya a Jihar sun ce tsakanin watan Maris zuwa Afrilu 2025,an samu al’amarin da ya shafi saw a Shanu guba a wurin kiwonsu sau shida a Kananan Hukumomin Bassa da Mangu.Bugu da kari tsakanin Maris 3 zuwa 10, Shanu 9 an sa masu guba a kauyukan Kwerenkwe, Rukwechogu da  kuma Dan Tanko a cikin Karamar Hukumar Bassa.

Hakanan ma ranar 31 Maris, 2025,  sai kuma wasu Shanu 10 da aka sa wa guba a  gundumar Woshina, Panyam ,Karamar Hukumar Mangu.Sai kuma,2 Afrilu ,Shanu 20  su ma haka aka yi masu duk dai a garin Woshina.

Makiyayan haka suka ce ranar 14 Afrilu 14, hanu 4 su ma basu tsira ba daga hakan a cattle were  a a gundumar Anchetahu, Miango,a Karamar Hukumar Bassa ;bayan kwana biyu kuma,sai kuma ga wasu 36 su ma dai duk lamarin gubar ne kusa da kwanar Tafi Gana ranar 16 Afrilu 2025.

Jaridar Trust ta karshe mako  ta bada labarin cewar ranar 16,Afrilu a kwanar Tafi Gana can ma din an sa wa Shanu 36 guba, mataimakin Insifekta Janar sashen ayyuka,DIG B.D Kwazhi,wanda aka maida shi Jihar domin  ya kawo zaman lafiya tsaknain al’ummar Jihar,ya ziyarci wurin da lamarin ya faru cikin rakiyar Kwamiushinan ‘yansanda na Jihar,sashen Jihar Filato ranar 17 Afrilu domin su jajantawa wadanda aka sa wa Shanun nasu guba.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansanda ta Jihar DSP Alabo Alfred,a wata sanarwar da ya fitar bayan ziyarar 17 Afrilu da ya kai a wurin da lamarin ya faru, ya lura da cewar Shanun 33 an sa masu guba ne har sai da suka mutu,na wadansu mutane ne wadanda har yanzun ba a gane ko su wanene ba daga wurin,ya lokacin da ya kai ziyara wurin, mataimakin Insifekata Janar na ‘yansanda,DIG ya ja kunnen su makiyayan da,cewar kada sukai ramuwar gaiya.

Hakanan ma ranar 18 Afrilu, 2025, Gwamnatin Filato ta hannun Kwamishinan yada labaranta, Joice Ramnap,ya kafa kwamiti domin ya binciki lamarin. Kwamishinan ya ce Gwamna Caleb Mutfwang  ya ba ma’aikatar ci gaban dabbobi da lamauran lafiyarsu da Kifi, su yi cikakken bincike dangane da zargin da ake yi.

Ranar 22 Afrilu, duk dai Jaridar ta bada rahoton an sa ma Shanu 36 guba kusa da ofishin Hukumar Zabe mai zaman kanta a Karamar Hukumar Mangu lokacin da suke kiwo a wurin, inda ya kara da cewa Jami’in ‘yansanda na wurin (DPO), shiyya ta 8 Kwamandan  Operation Safe Haben, da kuma wanda ke kulawa da ofishin Hukumar farinkaya sun je wurin domin su ganewa idanunsu abubuwan da suka faru.

A wancan harin ta’addancin da aka kai wani mutum mai suna Alhaji Nyako Muhammad,wanda shi makiyayi ne,ya yi bayanin yadda ransa ya baci inda yace lamarin ya  jefa iyalansa cikin matsalar koma-baya,inda kuma yake bayanain cewa,“wadanda suka aikata laifin sun sa wa mangwaro guba inda aka zube su kasa.Sai dai kuma wani abin bakin- ciki dabbobinmu sunci magwarorin,da aka sa wa guba. Dukkannin jami’an hukumomin tsaro na Karamar Hukumar tare da Shugaban Karamar Hukumar sun sann halin da ake ciki da kuma abubuwan da suka faru.

Ya ce sa wa Shanu na guba gaba daya abin ya shafi hanyoyin da iyali na suke samun yadda za su tafiyar da rayuwarsu“.Shanun sun kai Naira milyan 33 yawancinsu na marayu ne a karkashin kulawa ta. Sune muka sa ran a kansu wajen tafiyar da harkokinmu.Fiye da mutane 20 sun dogara ne kan Shanun ,yanzu kuma sai ga shi duk an kashe su.Mun ja hankalin matasa cewar kada su yi ramuwar gaiya. Muna yin kira ga gwamnati ta shiga cikin lamarin namu kamar yadda ya ce’’.

Ismail Idris,wanda shi ma makiyayi ne da ya rasa Shanunsa 36  ta hanyar gubar da aka sa masu kusa da kwanar Tafi Gana  cewa yayi kudin Shanun sun kai Naira milyan 23.

Ya ce“Ban san abinda zan yi ba.Asarar da na yi tayi yawa.An lalata mani hanyar tafiyar da rayuwata.Ina da yara ; babu wani abinda na sani in ban da kiwon Shanu kamar yadda ya jaddada,”.

Harbe Shanu 45

Al’ummar da yawansu  makiyaya ne sun bayyanawa Jaridar Trust ta karshen mako  cewa an kasha Shanu  45  ne a garuruwan Tangjol da Tashek  cikin Karamar Hukumar Riyom, yayin da sauarn an kasha su ne a , kauyen Shen,Karamar Hukumar Jos ta Kudu.

Shi kuwa Abdullahi Garba,  Shugaban Jiha na kungiyar ci gaban Gan Allah Fulani (GAFDAN), ya bayyana cewa ranar 19  Afrilu,2025,an harbi Shanu f4 su kuma masu kiwonsu an ji masu rauni,a  Tangjol, cikin Karamar Hukumar Riyom.Har ila yau ya kara da cewa ranar 27  Afrilu  2025 an kara kashe Shanu 37 .

Makiyayan sun ce ranar 21 Afrilu, 2025, ‘yan ta’adda sun kashe Shanu 3 da kuma makiyayi daya,Hamza Suleiman a kauyen Shen, cikin Karamar Hukumar Jos ta Kudu.

Bashiru Haruna, wanda shi ma makiyayi ne ya yi asarar Shanu 37 lokacin da aka yi harbe- harbe,a garin Riyom, ya ce kudin Shanun sun kai fiye da Naira milyan 30 sanadiyar shi hari na harbe- harben da aka kai.

“Dukkan Shanun shikenan sun tafi  na rasa su.Kowane daya daga cikin manyan ba zai rasa kai kasa da Naira milyan1 ba.Gaba daya, asarar ta kai ta fiye da Naira 30,amma sai ‘yan ta’addar suka kasha su,basu barni da komai ba.

“Wannan lamarin ya jefa iyalaina cikin halin rudani. Kiwon Shanu shi nake yi domin tafiyar da rayuwata. ‘Ya’yana basu kammala makaranta ba, maganar ma su samu ayyukan yi daga gwamnati bata ma taso ba, domin su kula da iyali.Gidan mu yanzu babu komai hanyar da muke amfani wajen tafiyar da rayuwarmu yanzu babu ita an raba mu da ita kamar yadda ya yi karin bayani”.

 

Sace Shanu 206

Al’ummar wuraren da ake yin kiwo wato makiyaye sun yi zargin sace masu Shanu lokacin da aka kai hare- haren.

Shugaban kungiyar masu kiwon Shanu MACBAN na Jihar Filato ya ce ranar 2 ga Maris 2025,an sace fiye da Shanu 30 a Marish cikin Karamar Hukumar Bokkos.

Hakanan ma makiyayan su zargi cwa ranar 13 ga Afrilu 2025, an sace Shanu 30 yayin da shi makiyayin babu wanda ya san inda yake a garin Murish karkashin Karamar Hukumar Mangu.

Bugu da kari kumaan bayyanawa Jaridar karshen mako  duk dai a rana daya, an samu labrin sace Shanu 14 wadanda suke mallakin wani mutum ne da ake kira Salihu Amadu,a kusa da Kopgain, a gundumar  Langai da ke karkashin Mangu.

Hakanan ma ranar 22  Afrilu 2025,an sace Shanu, 132 kusa da garin Jwokshang,a Karamar Hukumar Mangu da wata kungiyar mahara ‘yanta’adda suka yi .

Shagari Manu,wanda shi ma lamarin sace Shanun ya shafe shi a Mangu,yace Shanu 170 da kudinsu ya fi Naira milyan 100 wadanda  mallakin shi ne da shi da dan’uwansa an sace su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: cikin Karamar Hukumar Karamar Hukumar Mangu a Karamar Hukumar wanda shi ma Naira milyan sa wa Shanu

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

Kwamishinan lafiya na Jihar Adamawa, Dokta Felix Tangwami ya bayyana cewa, cutar kwalara a Ƙaramar hukumar Mubi ta yi sanadin mutuwar mutane 10, inda ya buƙaci mazauna yankin da su kula da tsaftar jikinsu.

Da yake yi wa Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) bayani a Yola ranar Laraba, Tangwami ya ce marasa lafiyan sun mutu ne a gida maimakon a cibiyoyin lafiya.

Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita

Ya ƙara da cewa, gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumar lafiya ta duniya (WHO) sun ɗauki matakin gaggawa don daƙile ɓarkewar cutar.

“Tun daga farko, mun ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin, kasancewar mu a can, kuma ba za a iya musanta hakan ba,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, waɗanda suka ziyarci cibiyoyin kiwon lafiya sun samu kulawa, inda aka kwantar da majinyata 25 a ranar Talata 4 ga watan Nuwamba, yayin da wasu da dama kuma an sallame su tare da wayar da su kan harkokin tsafta.

Ya bayyana cewa, an tura jami’an kula da cututtuka na jihar, da Daraktan kula da cututtuka a Hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko, da masu aikin sa-kai zuwa Mubi domin gudanar da ayyuka da kuma wayar da kan jama’a.

Sun kuma gano waɗanda abin ya shafa a cikin unguwanni don tabbatar da sun samu kulawar lafiya.

Tangwami ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya da su goyi bayan ƙoƙarin gwamnati ta hanyar ƙarfafa gwiwar mazauna yankin da su gaggauta neman magani a cibiyoyin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  •  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Babban Matsalar Jin Kai A Falasdinu, Inda Falasdinawa Miliyan 1.5 Suke Cikin Halin Musiba Da Bala’i
  • Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano