Aminiya:
2025-08-12@17:53:27 GMT

An kama matashi da kawunan mutane a Legas

Published: 11th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ta cafke wani mutum mai suna Samson Oghenebreme a unguwar Odomola ɗauke da kawunan mutane.

Sanarwar da kakakin ’yan sandan Legas, Benjamin Hundeyin ya fitar, ta ce an kai kawunan da aka gano asibiti a Epe, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama

An kama matashin ne ɗan shekara 25 bayan da jami’an bijilanti da ke sintiri a yankin suka sanar da jami’an tsaro cewa ba su yadda da take-takensa ba.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa ’yan sandan sun yi zargin cewa matashin yana kai kawunan Jihar Edo wajen wani boka — wanda yake amfani da su don yin kuɗi.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Olohundare Jimoh ya yaba wa jami’an ’yan sanda da na bijilanti kan ɗaukar matakin da ya dace da sauri.

Ya kuma buƙaci duk mazauna jihar da su riƙa sa ido da kai rahoton abin da ba su yarda da shi ba zuwa ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Legas Kawunan mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayar da gargadi game da hawan keken masu kananan shekaru da rashin biyayya ga fitilun ababen hawa a cikin babban birnin Kano.

 

 

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

 

Gargadin na zuwa ne bayan an samu munanan hadurran kan tituna guda 16 a cikin watan Agustan 2025, wanda ya yi sanadin jikkata da asarar dukiyoyi.

 

 

Rundunar ta lura cewa hawan keken ƙananan yara yana haifar da babban haɗari ga mahaya da sauran masu amfani da hanyar.

 

 

An shawarci iyaye da masu kula da su da su guji barin ‘ya’yansu da ba su da shekaru su yi amfani da keken mai kafa uku, domin hakan zai jawo hukunci mai tsanani a karkashin dokar.

 

 

Rundunar ta kuma lura da yanayin rashin biyayya ga fitilun ababen hawa da kuma dokokin hanya daga wasu masu amfani da hanyar.

 

 

“Wannan dabi’a tana haifar da cunkoson ababen hawa da ba dole ba, da kuma hadurran da za a iya kaucewa, da jefa rayukan mutane cikin hadari da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa.”

 

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kebe jami’an tsaro domin tabbatar da bin ka’idojin zirga-zirga.

 

Rundunar ta bukaci duk ‘yan kasar da su bi dokokin hanya da kuma bayar da rahoton duk wani abu na hawan keken kanana, tukin ganganci, ko wasu keta haddi.

 

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro na rayuka da dukiyoyi a jihar.

 

Abdullahi jalaluddeen/Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Kwastam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
  • Hukumar Kwatsam ta kama makamai da ƙwayoyin N10bn a Legas
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas