‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’
Published: 13th, May 2025 GMT
Bankin Duniya ya sanar da cewa duk da ƙalubalen hauhawar farashin da Nijeriya take fuskanta, tattalin arzikin ƙasar ya ƙaru a shekarar da ta gabata.
Babban bankin ya ce tattalin arzikin Nijeriyar ya samu haɓaka a kusan shekaru goma a 2024, inda a watanni uku na karshen 2024 aka samu haɓaka sosai.
HOTUNA: Trump na ziyara a Saudiyya Majalisa ta yi watsi da kudurin dokar mulkin karba-karbaHakan na ƙunshe cikin wani rahoto da babban jami’in tattalin arzaki na Bankin Duniya a Nijeriya, Alex Sienaert, ya fitar ranar Litinin a Abuja.
Sienaert ya bayyana cewa tattalin arzikin ya ƙaru da kashi 4.6 a watanni uku na ƙarshen 2024, inda ya kuma yi nuni da cewa zai ci gaba da haɓaka a farkon 2025.
Sai dai ya yi gargaɗin cewa hauhawar farashi na ci gaba da zama ƙalubale amma ana sa ran tattalin arzikin Nijeriyar zai haɓaka a wannan shekarar da kashi 3.6.
Nijeriya na ci gaba da fama da hauhawar farashi, inda Sieneart ya yi gargaɗin cewa dole ne a ɗauki matakan tsuke bakin aljihu da tasarrufin kuɗaɗe bisa doka da oda.
Sienaert ya ce harajin gwamnati ya ƙaru da kashi 4.5 sama da na shekarar da ta gabata, wanda “muhimmiyar nasara” ce, da janye tallafi ga kuɗaɗen ƙasashen waje, da kyautata tsarin karɓar haraji da yawan saka kuɗaɗe a asusun gwamnati suka kawo.
Kuɗaɗen shiga masu yawa da aka samu sun taimaka wajen cike giɓin Kasafin Kuɗi da aka yi hasashen ya kai kusan kashi uku a 2024, daga kashi 5.4 da aka samu a 2023.
Manyan matakan da shugaban ƙasar Bola Tinubu ke ɗauka, ciki har da kawo ƙarshen tallafin mai, da janye tallafi kan wutar lantarki da karya darajar naira har sau biyu, sun ƙara matsa lamba ga farashin kayayyaki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bankin Duniya Bunƙasa Tattalin Arziƙi Hauhawar Farashi Nijeriya tattalin arzikin
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
Nijeriya da ƙasar Isra’ila sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro a fannoni masu muhimmanci kamar yaƙi da ta’addanci, musayar bayanan sirri, samar da kuɗin tsaro da kuma horaswa ta musamman.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar haɗin gwiwa wadda Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, da Mataimakiyar Ministan Harkokin Waje ta Isra’ila, Sharren Haskel-Harpaz suka fitar bayan wani taro na musamman da suka gudanar ranar Litinin a Abuja.
Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa junaSanarwar, wadda mai magana da yawun Ofishin Ƙaramar Ministar Harkokin Wajen, Dokta Magnus Eze ya fitar, ta ce taron ya nuna alaƙa mai ɗorewa da muhimmanci tsakanin ƙasashen biyu.
A yayin taron, wakilan ƙasashen biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi tsaro a duniya, musamman yaƙi da ta’addanci, da kuma inganta hulɗar siyasa da tattalin arziki.
Ministocin biyu sun yi ƙara jan hankali kan barazanar ta’addanci a duniya, inda suka ce dole ne ƙasashe su haɗa kai wajen yaƙi da shi, musamman wajen samun bayanai kan hanyoyin samar da kuɗaɗen da ke ɗaukar nauyin ta’addanci.
Haka kuma, ƙasashen biyu sun amince su ƙara haɗin kai a fannonin da suka shafi ƙasa da ƙasa tare da mara wa juna baya a muhimman batutuwa masu kawo ci gaba.
Baya ga tsaro, taron ya mayar da hankali kan amfani da fasaha da ƙirkire-ƙirkire wajen kula da iyakoki, inganta ƙwarewar makamar aiki, musayar al’adu, yawon buɗe ido, noma, da ayyukan jakadanci da shige-da-fice.
Kazalika, ƙasashen sun amince da shirye-shiryen musayar ma’aikata da ziyarar ƙara ilimi, tare da kafa tsari na musamman domin ci gaba da tattaunawa da haɗin gwiwa a nan gaba.
A wani ɓangare na taron, an yi muhawara kan fasahar zamani wadda Ambasada Janet Olisa daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta jagoranta tare da Ambasada Sharon Bar-Li daga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Isra’ila.