Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Gudanar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Jabaliya Da Khan Yunus
Published: 12th, May 2025 GMT
Sojojin mamayar Isra’ila sun aiwatar da mummunan kisan kiyashi a garin Jabaliya, tare da janyo shahada da jikkatan wasu a Khan Yunis
A rana ta 56 da sake komawa yaki ta hanyar kai hare-haren wuce gona da iri kan Gaza, sojojin mamayar Isra’ila sun ci gaba da yin luguden wuta kan wasu wuraren zama, da matsugunan ‘yan gudun hijira da suke Gaza, a matsayin matakin farko na hare-harensu a yau Litinin.
Bayan nan Sojojin mamayar sun farma garin Jabaliya da ke arewacin zirin Gaza, inda suka kai wasu munanan hare-hare kan garin da jiragen saman yaki da suka aiwatar da mummunan kisan kiyashi a makarantar Fatima Bint Asad, da ya zama mafaka ga ‘yan gudun hijira.
Hare-haren bama-bamai biyu da aka kai kan makarantar ya yi sanadiyar shahadan fararen hula 16 tare da jikkata wasu, bayan da daya daga cikin jiragen ya kai hari a ajujuwa biyu har sau biyu a jere.
Haka a Jabaliya matashin bafalasdine mai suna Adham Al-Amital ya yi shahada sakamakon harin bam da jirgin sojin Isra’ila ya kai kan yankin “Abd Rabbo” da ke gabashin sansanin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tawagar da ke karkashin jagorancin, Barry Andrews ta kuma ziyarci hedkwatar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), inda shugabanta, Mahmood Yakubu, ya yi gargadin cewa jinkirin da ‘yan majalisa ke yi wajen gyaran dokar zabe ta 2022 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen gudanar da zabe a 2027.
Wakilan, wadanda suke Nijeriya tun kusan makonni uku domin nazarin matakin aiwatar da shawarwarin da ke cikin rahotonsu na bayan zaben 2023, sun kuma yi tattauna da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
Abbas, a cikin wata sanarwar da sakataren yada labaransa, Leke Bayeiwu, ya shaida wa tawagar EU cewa rahotanninta kan zabukan shekarar 2023 ana la’akari da su a cikin sauye-sauyen gyara dokar zabe da na dimokuradiyya da Majalisar dokoki ke gudanarwa.
Abbas ya ce, “Ina so in bayyana cewa shugabancin kasar nan karkashin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yana kokarin tabbatar da cewa mun inganta tsarin zabenmu, musamman game da abubuwan da masu saka ido na kasashen waje suka lura da su a lokacin zaben 2023.
“Mu a majalisar kasa ma mun kasance cikin aiki tukuru wajen tattara mafi yawan batutuwa da suka taso daga zaben 2023, domin mu ga yadda za mu iya magance su ta hanyar bin dokoki, domin zabenmu na gaba ya kasance mai inganci da amsuwa a idon duniya.”
Ya shaida wa tawagar cewa taron shugabannin majalisar dattawa da na majalisar wakilai da aka yi kwanan nan ya yanke shawarar warware batutuwan gyaran tsarin zabe cikin hanzari.
Ya bayyana cewa ra’ayin da yawa daga ‘yan majalisar kasa shi ne, gudanar da zabe a rana guda ba wai kawai zai kara inganci da gaskiya a gudanar da zaben kadai ba, har ma zai rage yawan kashe kudade na kusan kashi 40 cikin dari.
Ya ce, “Kamar gudanar da zabe a rana daya, wanda zai bayar da damar gudanar da zaben shugaban kasa da mambobin majalisar tarayya da gwamnonin jihohi da kuma ‘yan majalisar dokoki na jihohi duka a rana guda.
“A tunaninmu, zai taimaka wajen rage kashe kudaden gudanar da zabenmu har kashi 40 cikin ddari idan muka iya gudanar da zabukan cikin rana guda. Hakan zai kuma inganta gaskiya da karfafa aiki yadda ya kamata, musamman wajen fitowar masu kada kuri’a.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA