Sojojin mamayar Isra’ila sun aiwatar da mummunan kisan kiyashi a garin Jabaliya, tare da janyo shahada da jikkatan wasu a Khan Yunis

A rana ta 56 da sake komawa yaki ta hanyar kai hare-haren wuce gona da iri kan Gaza, sojojin mamayar Isra’ila sun ci gaba da yin luguden wuta kan wasu wuraren zama, da matsugunan ‘yan gudun hijira da suke Gaza, a matsayin matakin farko na hare-harensu a yau Litinin.

Bayan nan Sojojin mamayar sun farma garin Jabaliya da ke arewacin zirin Gaza, inda suka kai wasu munanan hare-hare kan garin da jiragen saman yaki da suka aiwatar da mummunan kisan kiyashi a makarantar Fatima Bint Asad, da ya zama mafaka ga ‘yan gudun hijira.

Hare-haren bama-bamai biyu da aka kai kan makarantar ya yi sanadiyar shahadan fararen hula 16 tare da jikkata wasu, bayan da daya daga cikin jiragen ya kai hari a ajujuwa biyu har sau biyu a jere.

Haka a Jabaliya matashin bafalasdine mai suna Adham Al-Amital ya yi shahada sakamakon harin bam da jirgin sojin Isra’ila ya kai kan yankin “Abd Rabbo” da ke gabashin sansanin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum

Ɗaya daga cikin baƙin da suka tafi ɗaurin aure daga Zariya, Abbas Rufa’i, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga harin da wasu matasa suka kai musu a Ƙaramar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato.

A cewarsa, “Da muka tsaya a hanya domin yin tambaya, na fito daga motar domin neman hanya. Amma sai na ga yadda mutanen da ke wajen suka fara mana wani irin kallo.

Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma 1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

“Na ji ɗaya daga cikinsu yana cewa, ‘a kashe su gaba ɗaya, a ƙone motar.’”

Rufa’i ya ƙara da cewa, “Na cire rigata, na shiga cikin daji har na sai da na samu wani mai babur, na ce masa ya kai ni wajen ‘yan sanda. Amma da muka isa wajen wasu sojoji, sai na ce ya tsaya, na sanar da su abin da ya faru.”

Ya bayyana cewa sojojin sin bi shi zuwa wajen, inda suka ceto mutane 18 da suka jikkata, yayin da wasu sun rasu.

Za mu biya diyya – Gwamnatin Filato

Kwamishinar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato, Joyce Ramnap, ta ce gwamnati za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ta ce, “Za mu biya diyya. Amma muna jiran rahoton ‘yan sanda kafin mu ɗauki mataki.”

’Yan majalisa sun buƙaci a kama waɗanda suka aikata laifin

Majalisar Wakilai ta buƙaci Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Shugaban DSS da Hafsan Sojin Ƙasa su kama waɗanda suka aikata kisan.

Hon. Sadiq Ango Abdullahi ya ce, “Rashin kama masu laifi yana ƙara kawo rashin gaskiya da ƙarancin amana ga gwamnati.”

Kowa yana da ’yancin yin tafiya — Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce, “Doka ta bai wa kowa ’yancin zirga-zirga a Najeriya. Gwamnoni su tabbatar da hakan.”

Ya godewa al’ummar Kudan da suka zauna lafiya duk da irin halin da suka tsinci kansu a ciki.

Za a hukunta waɗanda suka aikata laifin – Gwamnatin Filato

Joyce Ramnap ta ce an kama mutum 22 da ake zargi da hannu a harin. “Za mu hukunta duk wanda aka samu da laifi,” in ji ta.

Wannan laifi abu ne da aka tsara — Ƙungiyar Musulmai

Ƙungiyar Musulmai ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta ce, “Ba kuskure aka yi ba. Wannan kisan an shirya shi ne. Idan ba a hukunta masu laifin ba, hakan na iya jawo ramuwar gayya.”

Waɗanda suka aikata wannan laifi dabbobi ne — Ƙungiyar CAN

Ƙungiyar Kiristoci ta Arewa ta ce, “Kisan da aka yi wa waɗanda ba su da laifi ba shi ne mafi muni cikin ɗabi’ar ɗan Adam. Wannan rashin imani ne kuma bai dace ba.”

Wannan kisan laifi ne da aka shirya — Ƙungiyar Dattawan Arewa

NEF ta ce, “Wannan ba kuskure ba ne, laifi ne da aka tsara. Yana nuna irin matsalolin da ke damun Arewa.”

Ƙungiyar ta buƙaci a hukunta duk masu hannu cikin lamarin.

Kisan ’yan ɗaurin auren da suka taso daga garin Zariya zuwa Filato, ya tayar da ƙura a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke Allah-wadai da kisan.

Yanzu haka dai an zuba wa jami’an tsaro da gwamnati ido don ganin irin matakin da za a ɗauka kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani
  • ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta