Shugaban Amurka Ya Ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Indiya
Published: 10th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka ya sanar da cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Indiya da Pakistan
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa: Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta nan take, wanda Amurka ta shiga tsakani wajen kulla ta.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana farin cikinsa da wannan ci gaba, da aka samu, inda ya yaba da amfani da hankali da basirar da kasashen biyu suka nuna wajen daukar wannan mataki.
Wannan sanarwar ta zo ne a wani lokaci mai muhimmanci, yayin da alakar Indiya da Pakistan ke samun tangarda da kuma bullar takun-saka a tsakaninsu a ‘yan shekarun nan, musamman kan batun Kashmir.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
Ana zargin wani ɗan shekaru 18 da kashe wani maraya ɗan shekara 10 a yankin Ƙaramar Hukumar Zariya ta Jihar Kaduna.
’Yan sanda sun kama matashin ne kan zargin sa da yi wa ɗan yaron, wanda ɗan baffansa ne, ɗaurin goro tare da azabtar da shi saboda yaron ya ƙi amincewa ya yi lalata da shi.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a unguwar Iyan Juma da ke Karamar Hukumar Zariya.
Mahaifiyar marigayin mai suna Asama’u Mohammed ta shaida wa Aminiya cewa, “Na dawo wajen aikatau kamar yadda na saba yi don na samo abin da zan ba su su ci tare da ’yan uwansa, sai ga yayansa ya shigo a guje ya ce ga Idris can a kwance cikin jini kuma fuskarsa a kumbure, wai sun yi faɗa da wani duk an ji mishi ciwo, nan da nan na yafa hijabi ni da ɗan uwar gidana muka tafi inda yake.”
Mahaifiyar Babban Editan jaridar Daily Trust ta rasu Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —MasaniAminiya ta garzaya Babban Ofishin ’yan sanda da ke Ƙofar Fada cikin birnin Zariya domin ji daga bakin babban jima’i, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin kuma ya shaida wa wakilinmu, cewa sun tattara bayanai yadda lamarin ya kasance kuma sun tura zuwa babban ofishinsu da ke Kaduna
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kaduna DSP Mansur Hassan ya tabbatar wa wakilin namu da faruwar lamarin, da kama wanda da ake zargi.
Ya ƙara da cewa bayan sun kammala bincike za su tora zuwa kuto.