Shugaban kasar Amurka ya sanar da cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Indiya da Pakistan

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa: Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta nan take, wanda Amurka ta shiga tsakani wajen kulla ta.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana farin cikinsa da wannan ci gaba, da aka samu, inda ya yaba da amfani da hankali da basirar da kasashen biyu suka nuna wajen daukar wannan mataki.

Ya kuma jaddada cewa, dogon tattaunawar da aka yi tsakanin bangarorin biyu ya haifar da wannan yarjejeniya, wanda ke nuna muradin bangarorin biyu na samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Wannan sanarwar ta zo ne a wani lokaci mai muhimmanci, yayin da alakar Indiya da Pakistan ke samun tangarda da kuma bullar takun-saka a tsakaninsu a ‘yan shekarun nan, musamman kan batun Kashmir.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF), ta kai hare-hare ta sama a yankin Rann, wani gari da ke Jihar Borno, wanda ake zargin ya zama mafakar ’yan ta’adda.

Wannan aiki na cikin shirin Operation Haɗin Kai, kuma ya yi sanadin hallaka ’yan ta’adda da dama.

’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun fara guduws bayan yunƙurinsu na kai hari sansanin sojoji ya ci tura.

Da suka hangi jiragen yaƙi na sojojin sama, sai suka fara tserewa daga maɓoyarsu, amma an kashe da yawa daga cikinsu ta hanyar ɓarin wuta.

Wani mazaunin Rann ya ce da farko sun yi zaton cewa ’yan ta’addan ne za su kai musu hari saboda ƙarar da suka ji kamar ta bindiga.

Daga baya ne suka fahimci cewa sojoji ne ke gudanar da aiki.

Mai magana da yawun Rundunar Sojin Sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya tabbatar da harin a cikin wata sanarwa.

Ya ce sun samu bayanan sirri da suka tabbatar da inda ’yan ta’addan suke, kuma bayan sojojin ƙasa sun gano su suna guduwa, sai aka aike jiragen yaƙi da suka kai musu farmaki.

Harin ya daƙile barazanar ’yan ta’addan, kuma ya dawo da zaman lafiya a yankin.

Ejodame, ya ƙara da cewa wannan aiki ya nuna irin sadaukarwar da Rundunar Sojin Sama ke yi wajen kare dakarunta da kuma daƙile duk wata barazanar ’yan ta’adda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • Majalisar Jigawa Ta Yi Karatu Na Biyu Kan Dokar Fansho Ga Tsofaffin Shugabanni
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi
  • Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka
  • Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina