Aminiya:
2025-08-12@13:24:41 GMT

HOTUNA: Trump na ziyara a Saudiyya

Published: 13th, May 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump ya isa ƙasar Saudiyya a ziyararsa ta farko a yankin Gabas ta Tsakiya, inda tuni ya sauka a Riyadh a jirgin Air Force One.

Shugaban na Amurka ya yi zaman farko da Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman, kafin su shiga wani zaman sirri.

Bom ya kashe jami’an ilimi 2 a Borno Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano

Trump zai gana ne da Mohammed bin Salman a filin jirgin sama na Sarki Khalid da ke Riyadh a kusa da hotunan wasu daga ckin mambobin iyalan sarauta na Saudiyya

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ma zai kasance a cikin taron.

Bayan Saudiyya, Trump dai na shirin kai ziyara ƙasashen Qatar da kuma Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa daga ranar Talata zuwa Alhamis na wannan makon.

Shugaban Amurkan na wannan ziyara ta kwanaki huɗu a ƙasashen Gabas ta Tsakiya domin yauƙaƙa dangantaka da kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar cinikin makamai na biliyoyi har ma da tattaunawa kan batun yakin Gaza da shirin nukiliyar Iran.

Mista Trump na tare da attajirin Amurka kuma shugaban kamfanin ƙera motocin Tesla, Elon Musk da kuma wasu manyan muƙarraban gwamnati.

Wannan ce ziyararsa ta biyu tun bayan hawu kan karagar mulkin Amurka baya ga halartar jana’izar tsohon shugaban Darikar Katolika na Duniya Fafaroma Francis a birnin Rome na ƙasar Italiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gabas ta Tsakiya Qatar Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Yayin ziyararsa a kasar Indiya kwanan nan, shugaban kasar Philippines ya bayyana cewa, idan Sin da Amurka suka yi taho-mu-gama kan batun yankin Taiwan, Philippines ba za ta iya killace kanta daga ciki ba. Irin wannan furucin nasa yana da ban mamaki, wanda ya saba da alkawarin da Philippines ta yi na tsayawa ga manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana, zai kara illata dangantakarta da kasar Sin, da zaman lafiya da tsaro a wannan shiyya.

Rura wutar rikici kan yankin Taiwan, yunkuri ne da Philippines ta yi na dogaro kan Amurka tare da ba ta hadin-kai, don hana ci gaban kasar Sin. Amma batun da ya shafi yankin Taiwan, batu ne na cikin gidan kasar Sin, kuma yadda za’a daidaita batun, harka ce ta al’ummar kasar zalla. Furucin shugaban Philippines ya saba da dokokin kasa da kasa da tsarin mulki na kungiyar ASEAN, tare da kawo babbar illa ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin shiyyar gami da muradun jama’ar Philippines. Mai yiwuwa dogaro kan Amurka zai iya kwantar da hankalin gwamnatin Marcos ta Philippines, amma hakikanin gaskiya shi ne, za ta girbi abun da ta shuka. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Giyar mulki Na Jan Trump – Ƴan Democrats
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
  • MDD za ta yi zaman gaggawa kan yunƙurin ƙwace Gaza
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno