Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Published: 11th, May 2025 GMT
Ya kara da cewa bukatar kasa da kasa game da karfin ma’adinai na Kaduna yana karuwa, tare da masu saka hannun jari da yawa wadanda suke bincike kan yadda za su yi amfani da wadannan albarkatun da ba a taba amfani da su ba.
“Baya ga wannan, muna da ma’adanan karfe. Kamfanin ‘African Mines’ ya riga ya zo Kaduna don hakar wannan albarkatun, wanda ya nuna a fili cewa Kaduna tana da ma’adanan karfe da za a iya gudanar da kasuwancinsu,” in ji shi.
Bello ya jaddada cewa tsarin kamfanin yana nuna jajircewa don kokarin killace iyakokin ma’adinai da kuma habaka su.
Ya ce tun lokacin da aka kafa kamfanin, hukumar gudanarwaar kamfanin ta ba da fifiko ga ayyukan da ke sanya alhakin muhalli da zamantakewar al’umma a gaba a ayyukanta.
Haka kuma manajan daraktan ya kuma yaba wa Gwamna Uba Sani saboda goyon bayan da yake bayarwa ga bangaren hakar ma’adanai, yana mai cewa a karkashin jagorancin gwamnan, kamfanin ba wai kawai a shirye yake ba har ma yana da cikakkiyar kayan aiki don samar da sakamako mai kyau.
“Ana sa ran wannan kokari zai samar da ci gaba a hakar ma’adanai tare da bude hanyoyin arziki a bangaren ma’adanai, samar da dubban ayyuka, da kuma habaka ci gaban tattalin arziki ba kawai a Kaduna ba har ma a duk fadin Nijeriya,” in ji shi.
Ya kuma tabbatar wa masu saka hannun jari na cikin gida da na waje samar da yanayi mai aminci wanda ke karfafa kirkire-kirkire da ci gaba na dogon lokaci.
Bello ya kuma sanar da cewa kamfanin bunkasa ma’adanai na Kaduna a shirye yake ya yi maraba da masu saka hannun jari da ke da sha’awar yin amfani da albarkatun kasa na jihar.
Ya bayyana tashar sarrafa lithium ta Kangimi, wacce ke aiki a karfin tan 5,000 a kowace rana, a matsayin babban ci gaba a tafiyar hakar ma’adinai ta jihar.
“Bisa jajircewar kamfanin wajen samar da aminci da ci gaba mai dorewa, Kaduna za ta kasance a matsayin babban wurin saka hannun jari,” in ji shi.
Ya nuna godiya ga Gwamna Uba Sani, yana mai cewa, “Godiya ga kokarin da Gwamna Uba Sani ya yi, muna shaida canji mai ban mamaki a bangaren hakar ma’adanai wanda ke bude hanya don kyakkyawar makoma mai kyau.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: saka hannun jari
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, sun kashe ’yan fashi biyu, sannan sun kama wasu biyu a unguwar Makera da ke Kakuri.
Wannan ya biyo bayan musayar wuta da jami’an tsaro suka da ’yan fashin.
Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarentaRundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:10 na dare, bayan da suka samu kiran gaggawa daga mazauna unguwar Gashash a Barnawa.
Rahotanni sun ce ’yan fashi guda takwas sun shiga wani gida ɗauke da bindigu da makamai, sun sace wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki.
Bayan kiran gaggawar, DPO na Barnawa, Kakuri da Sabon Tasha tare da sojoji daga Rundunar 312 Artillery Regiment suka bi ’yan fashin har titin Makera.
Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya ce, “Da ’yan fashin suka ga jami’an tsaro, sai suka fara harbi.
“Wannan ya jawo musayar wuta, inda aka kashe biyu daga cikinsu sannan aka kama biyu da ransu.”
Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar gida, harsasai da wasu makamai.
Sannan sun dawo da kayan da aka sace ciki har da wayoyi bakwai, agoguna uku, kwamfutoci biyu da sauransu.
A lokacin musayar wutar, ɗan sanda ɗaya ya samu rauni amma an miƙa shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya jinjina wa jami’ansa kan yadda suka yi aiki cikin gaggawa tare da haɗin kai da sojoji da DSS.
Ya ce rundunar ta ƙudiri aniyar kare jihar daga miyagu.
Ya kuma roƙi al’umma da su riƙa sanya idanu tare da kai rahoton duk wani abun zargi.
Rundunar ta ce tana ci gaba da neman sauran ‘yan fashin da suka tsere.