Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Published: 11th, May 2025 GMT
Ya kara da cewa bukatar kasa da kasa game da karfin ma’adinai na Kaduna yana karuwa, tare da masu saka hannun jari da yawa wadanda suke bincike kan yadda za su yi amfani da wadannan albarkatun da ba a taba amfani da su ba.
“Baya ga wannan, muna da ma’adanan karfe. Kamfanin ‘African Mines’ ya riga ya zo Kaduna don hakar wannan albarkatun, wanda ya nuna a fili cewa Kaduna tana da ma’adanan karfe da za a iya gudanar da kasuwancinsu,” in ji shi.
Bello ya jaddada cewa tsarin kamfanin yana nuna jajircewa don kokarin killace iyakokin ma’adinai da kuma habaka su.
Ya ce tun lokacin da aka kafa kamfanin, hukumar gudanarwaar kamfanin ta ba da fifiko ga ayyukan da ke sanya alhakin muhalli da zamantakewar al’umma a gaba a ayyukanta.
Haka kuma manajan daraktan ya kuma yaba wa Gwamna Uba Sani saboda goyon bayan da yake bayarwa ga bangaren hakar ma’adanai, yana mai cewa a karkashin jagorancin gwamnan, kamfanin ba wai kawai a shirye yake ba har ma yana da cikakkiyar kayan aiki don samar da sakamako mai kyau.
“Ana sa ran wannan kokari zai samar da ci gaba a hakar ma’adanai tare da bude hanyoyin arziki a bangaren ma’adanai, samar da dubban ayyuka, da kuma habaka ci gaban tattalin arziki ba kawai a Kaduna ba har ma a duk fadin Nijeriya,” in ji shi.
Ya kuma tabbatar wa masu saka hannun jari na cikin gida da na waje samar da yanayi mai aminci wanda ke karfafa kirkire-kirkire da ci gaba na dogon lokaci.
Bello ya kuma sanar da cewa kamfanin bunkasa ma’adanai na Kaduna a shirye yake ya yi maraba da masu saka hannun jari da ke da sha’awar yin amfani da albarkatun kasa na jihar.
Ya bayyana tashar sarrafa lithium ta Kangimi, wacce ke aiki a karfin tan 5,000 a kowace rana, a matsayin babban ci gaba a tafiyar hakar ma’adinai ta jihar.
“Bisa jajircewar kamfanin wajen samar da aminci da ci gaba mai dorewa, Kaduna za ta kasance a matsayin babban wurin saka hannun jari,” in ji shi.
Ya nuna godiya ga Gwamna Uba Sani, yana mai cewa, “Godiya ga kokarin da Gwamna Uba Sani ya yi, muna shaida canji mai ban mamaki a bangaren hakar ma’adanai wanda ke bude hanya don kyakkyawar makoma mai kyau.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: saka hannun jari
এছাড়াও পড়ুন:
Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
Hukumar tsaro ta DSS ta zargi dan jarida kuma mai shiga tsakani da ’yan ta’addar da suka sace fasinjojin jrigin kasan Kaduna-Abuja a shekarar 2022, Tukur Mamu, da karbar Naira miliyan 50 daga kudin fansar fasinjojin.
Ana zargin Tukur Mamu da karbar kudin ne daga jagoran ’yan bindigar da ake kira da “Shugaba”.
Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000 Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan KebbiMamu na fuskantar tuhumar laifukan ta’addanci, ciki har da karɓar kuɗin fansa daga iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a harin jirgin Kaduna na ranar 28 ga Maris, 2022, hulɗa da kuɗaɗen ’yan ta’adda, hana aikin kwamitin babban hafsan tsaron kasa da aka kafa domin tattaunawa da masu garkuwa da mutanen, musayar saƙonnin murya da mai magana da yawun Boko Haram, da sauransu.
A ci gaba da shari’ar a ranar Talata, shaida na hukumae ta DSS na shida ya shaida wa kotu cewa ƙungiyar ta’addan ta nemi Mamu ya koya musu yadda ake buɗe shafin yanar gizo domin gudanar da ayyukansu.
Tun da farko, DSS ta bayyana cewa Mamu ya ba da shawara ga ƙungiyar ’yan ta’addan da su tattauna kai tsaye da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su, ba tare da shiga kwamitin babban hafsan tsaron da gwamnatin tarayya ta kafa ba.
Shaidar ya yi wannan bayani ne yayin fassara saƙonnin murya na Mamu a lokacin da ake yi masa tambayoyi a ƙasar Masar kafin a dawo da shi Najeriya.
A halin yanzu, Mamu ya shigar da Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN) kara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa kiran shi da dan ta’adda.
Ya ce ya shigar da ƙarar ce kan kiran nasa da dan ta’adda da ministan ya yi, alhali ana tsaka da shari’ar tuhumar laifukan ta’addanci kuma har yanzu ba a kai ga yanke hukunci ba.
Alƙali ya dage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Fabrairun 2026, domin amincewa da jawaban ƙarshe na ɓangarorin da abin ya shafa bisa tanadin Sashe na 49 na Dokar da kuma Sashe na 36 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.