NDLEA ta kama matar da ta ɓoye hodar iblis a al’aurarta
Published: 12th, May 2025 GMT
Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya, NDLEA ta sanar da cafke wata mata da ta ɓoye hodar iblis tana shirin tafiya ƙasar Iran.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi ya fitar, ya ce an kama matar ce a filin jirgin sama a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas.
Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670Babafemi ya ce matar ta ɓoye hodar iblis ɗin a cikin al’aurarta da cikinta da kuma a wata jaka.
A cewarsa, matar mai suna Ihensekhien Miracle Obehi, wadda ta saka hijabi domin ƙoƙarin tsallake binciken jami’an tsaro, an cafke ta ne a Lahadin da ta gabata lokacin da take yunƙurin shiga jirgin Qatar Airline zuwa Doha, kafin ta wuce Iran.
Ya ƙara da cewa yayin bincike, an gano matar ta saka ƙunshin hodar iblis har uku cikin al’aurarta, sannan ta saka wani a jakarta sai kuma ta haɗiye ƙwayoyi 67 a cikinta.
Sai dai mai magana da yawun hukumar ya ce an tilasta wa matar yin aman ƙwayoyin da kuma ƙunshin waɗanda ta haɗiye a cikinta da na ɓoye a al’aurarta.
Obehi ta yi iƙirarin cewa an buƙaci ta haɗiye ƙwayoyin hobar iblis 70, sai dai bayan haɗiye 67 ta kasa haɗiye sauran — inda ta yanke shawarar saka su a al’aurarta, a cewar Babafemi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: al aurarta hodar iblis hodar iblis
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
A safiyar Litinin ɗin nan ƙungiyar Hamas ta saki rukunin farko na ’yan ƙasar Isra’ila bakwai da ta yi garkuwa da su a Zirin Gaza.
A ɗaya ɓangaren kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako.
Tuni jami’an kungiyar agaji ta Red Cross suka shiga gidan yarin Wada a safiyar domin ɗaukar wani fursuna Bafalasdine da za fitar, wanda ke fama da rashin lafiya.
Hamas ta mika su ne ga kungiyar Red Cross a Gaza a yayin da ake da ran sako wasu ƙarin mutum 13 na gaba a Litinin ɗin nanm a cewar hukumomin Isra’ila.
Wannan na faruwa ne a yayin da Shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya taka muhimmiyar rawa a sulhun, yake ziyara a ƙasar Isra’ilan a safiyar Litinin.
Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — AtikuWannan na zuwa ne bayan yarjejeniyar zaman lafiyar da ɓangarorin biyu suka sanya hannu a kai a baya-bayan nan.
A bangare guda kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako, a matsayin ɓangarenta na musayar fursunonin yaƙin.
Ma’aikatar Harkokin Gida ta Isara’ila ta fitar da jerin sunayen mutanen da aka saki da shekarunsu:
Eitan Abraham Mor, 25 Gali Berman, 28 Ziv Berman, 28 Omri Miran, 48 Alon Ohel, 24 Guy Gilboa-Dalal, 24 Matan Angrest, 22Na gaba ake da ran muka su ga iyalansu a wani sansanin soji a Kudancin Isra’ila.
A ɗaya bangaren kuma kungiyar kula da Fursunoni ta Palastinu ta fitar da jerin sunayen mutane 1,718 da Isra’ila za ta sako.