NDLEA ta kama matar da ta ɓoye hodar iblis a al’aurarta
Published: 12th, May 2025 GMT
Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya, NDLEA ta sanar da cafke wata mata da ta ɓoye hodar iblis tana shirin tafiya ƙasar Iran.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi ya fitar, ya ce an kama matar ce a filin jirgin sama a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas.
Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670Babafemi ya ce matar ta ɓoye hodar iblis ɗin a cikin al’aurarta da cikinta da kuma a wata jaka.
A cewarsa, matar mai suna Ihensekhien Miracle Obehi, wadda ta saka hijabi domin ƙoƙarin tsallake binciken jami’an tsaro, an cafke ta ne a Lahadin da ta gabata lokacin da take yunƙurin shiga jirgin Qatar Airline zuwa Doha, kafin ta wuce Iran.
Ya ƙara da cewa yayin bincike, an gano matar ta saka ƙunshin hodar iblis har uku cikin al’aurarta, sannan ta saka wani a jakarta sai kuma ta haɗiye ƙwayoyi 67 a cikinta.
Sai dai mai magana da yawun hukumar ya ce an tilasta wa matar yin aman ƙwayoyin da kuma ƙunshin waɗanda ta haɗiye a cikinta da na ɓoye a al’aurarta.
Obehi ta yi iƙirarin cewa an buƙaci ta haɗiye ƙwayoyin hobar iblis 70, sai dai bayan haɗiye 67 ta kasa haɗiye sauran — inda ta yanke shawarar saka su a al’aurarta, a cewar Babafemi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: al aurarta hodar iblis hodar iblis
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
Babban malamin addinin Islama kuma jagoran mabiya Darikar Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya cika shekaru 101 a duniya, a lissafin kalandar Musulunci.
An haifi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ne a ranar 2 ga watan Muharram a shekara ta 1346 bayan hijira, inda a gobe Juma’a, 2 ga Muharram na shekarar 1447, yake cika shekaru 101 cif a ban kasa.
Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun IslamiyyaDuk da cewa iyalai da almajiran Maulana Shehu Dahiru Usman Bauchi ba su yi wani biki don taya shi murnar cika shekara 100 a duniya, amma masoya da almajiran Shehin Malamin sun bayyana farin cikinsu da yi masa addu’o’i musamman a dandali daban-daban na shafukan Intanet.
Sun yaba da irin hidimar da ya yi wa Musulunci da Bil Adama, inda suka jinjina rawar da ya taka a matsayinsa na shugaba mai kishi da kuma tsayuwar daka.
Daya daga cikin almajiransa, Malam Ahmad Tijjani Saeed ya ce, “Yayin da Maulana Sheikh yake cika shekaru 101 cikin koshin lafiya, ya bar abin koyi mai tarin yawa a rayuwa wajen bauta wa Allah da hidimta wa al’ummarsa da kuma bil’adama.”
Sauran almajiran irinsu Malam Ahmad Tijjani Kolo, Sanusi Ahmad, da Muhammad Sogiji, sun yaba wa jajircewar Sheikh Bauchi wajen yin magana kan zalunci da azzalumai da kuma matsalolin zamantakewa kamar cin hanci da rashawa, kungiyoyin asiri, da shaye-shayen miyagun kwayoyi.
Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda babban jigo a Darikar Tijjaniyya a Nijeriya da Afirka, shi ne Mataimakin Shugaban Kwamitin Fatawa na Majalisar Koli kan Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya.
Babban malamin na da ’ya’ya kimanin 100 da jikoki 406, da tattaba-kunne 100, wadanda su ma suka gaje shi a fannin haddar Al-Qur’ani.
Abin sha’awa, 78 daga cikin ’ya’yansa da jikoki sama da 199, da tattaba kunne 12 su ma sun haddacce Al-Kur’ani, hadi da ilimin boko da na addinin Musulunci.
Sheikh Bauchi ya yi aikin Hajji sau 56 da Umrah sau 207.
Hidimar Al-QuraniSheikh Bauchi ya fara Tafsirinsa ne a Jihar Bauchi a shekarar 1948, kuma ya shafe shekaru 77 wajen yin tafsirin Alkur’ani mai girma.
An fara yada Tafsirinsa a gidan rediyon Bauchi a shekarar 1976, kafin daga baya gidan rediyon Najeriya Kaduna ya fara yadawa a 1980.
A halin yanzu, gidajen rediyo da dama a arewacin Najeriya suna yada koyarwarsa, musamman a cikin watan Ramadan.
KaratunsaYa fara karatunsa na Musulunci ne a hannun mahaifinsa, Alhaji Usman, inda ya haddacce Alkur’ani mai girma tun kafin ya cika shekara 20 a duniya.
Ya ci gaba da karatunsa a karkashin manya malaman Musulunci na ciki da wajen Najeriya, inda Sheikh Ibrahim Inyass ya kasance babban malaminsa.
A halin yanzu Sheikh Bauchi yana zaune ne a Kofar Gombe da ke birnin Bauchi.