Aminiya:
2025-09-17@23:19:35 GMT

KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano

Published: 30th, January 2025 GMT

Hukumar Kula da Hanyoyi da Sufuri ta Jihar Kano (KAROTA), ta ware Naira miliyan 250 domin gyaran wasu motocin aiki guda biyar.

Haka kuma, hukumar ta kashe Naira miliyan 250 domin sayen sabbin motoci domin amfanin da su.

Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden

Kwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi na Jihar, Musa Sulaiman Shanono ne, ya bayyana hakan yayin da yake bayani kan kasafin kuɗin shekarar 2025 da aka amince da shi.

Ya bayyana cewa ingantaccen tsarin sufuri yana da matuƙar muhimmanci ga bunƙasa tattalin arziƙi da ci gaban al’umma.

Ya kuma ce gwamnatin jihar na ƙoƙarin inganta kayan sufuri domin sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a da kayayyaki a faɗin jihar.

“Tsarin sufuri yana da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa da bunƙasar tattalin arziƙi. Don haka, gwamnatin jiha tana ɗaukar matakan da suka dace don inganta kayayyakin sufuri domin sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki a ciki da wajen jihar,” in ji shi.

Shanono ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta ware Naira biliyan 13.32 don aiwatar da wasu muhimman ayyuka a ɓangaren sufuri, ciki har da sayen sabbin motocin ofis da kuma gyaran motocin aiki na hukumar KAROTA.

Ya tabbatar da cewa Naira miliyan 250 za a yi amfani da su wajen sayen motocin ofis, yayin da sauran Naira miliyan 250 ɗin za a kashe su wajen gyaran wasu motocin aiki guda biyar.

Kwamishinan ya yi ƙarin haske kan yadda motocin da za a gyara za su laƙume kuɗaɗe daidai da kuɗaɗen sabbin motocin da za a siya.

“Waɗannan motocin aiki ne, kuma manyan motoci ne. Ba za a iya haɗa su da motocin ofis da shugaba ke amfani da su ba, domin suna da bambanci,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gyaran Motoci Kwamishina Naira miliyan 250

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.

Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.

El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.

A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.

Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.

Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.

Yadda aka yi muƙabala tsakanin Shehi Tajul Izzi da Maidubun Isa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha