A yau Laraba ne dai shugaban majalisar shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf ya birnin Jakarta na kasar Indonesia, da zummar halartar taron wakilan majalisun kasashen da suke mambobi a kungiyar kasashen musulmi.

Taron na wannan karon a kasar Indonesia shi ne karo na 19 da kungiyar ta kasashen musulmi take yi a matakin wakilan majalisun, kasashe mambobi.

An bude taron ne dai daga jiya Talata 13 ga watan Mayu, zai kuma ci gaba har zuwa ranar 15 gare shi.

Tun a jiya ne dai wakilan Iran su 4 daga majalisar shawarar musulunci ta kasar su ka isa birnin na Jakarta domin halartar taron.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta

Iran ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma a hukumance kan zaluncin ‘yan sahayoniyya da Amurka

Mataimakin babban jami’in kula da harkokin kasa da kasa na ma’aikatar shari’a kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta Iran ya yi la’akari da matakin wuce gona da iri na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan cibiyoyin makamashin nukiliya, da kafofin yada labarai, da cibiyoyin kiwon lafiya na Iran, da kuma wuraren zama, gidajen yari da birane da kauyuka, a matsayin misali karara na keta dokokin kasa da kasa da hakkokin bil’adama.

A cikin wata wasika da ya aike wa kwamishinan kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk Nasser Seraj mataimakin shugaban hukumar shari’a kan harkokin kasa da kasa kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta kasar Iran ya bayyana cewa da gan-gan yahudawan sahayoniyya sun kai hari kan ginin gidan rediyo da talabijin na Iran da makamai masu linzami.

Ya yi nuni da cewa, wannan harin ya ruguza wasu cibiyoyin yada labaran kasar, tare da kawo cikas wajen yada labarai, sannan kuma abin takaici ma ya kai ga shahada da raunata ma’aikatan kafafen yada labarai wadanda su kadai ke da alhakin sanar da jama’a abubuwan da ke faruwa.

A daya bangaren Saraj ya ci gaba da cewa: Hare-haren da ‘yam sahayoniyya suka kai a kwanakin baya kan cibiyoyin kiwon lafiya, ginin kungiyar agaji ta Red Crescent, da motocin daukar marasa lafiya, da kuma yankunan da ke kusa da asibitoci, sun haddasa lalacewar ababen more rayuwa, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula, tare da sanya tsoro da firgici a tsakanin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
  • Limamin Tehran:  Duniya Ce Ta Yi Yaki Da Iran
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  •  Titunan Birnin Tehran Sun Cika Makil Da Masu Jana’izar Shahidan Ta’addancin HKI
  • Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome