Falasdinawa mazauna yankunan Khan-Yunus dake kudancin zirin Gaza suna fama da matsananciyar yunuwa, a lokaci daya suna fuskantar hare-hare masu tsanani daga sojojin HKI.

Mata mazauna yankin sun fi fuskantar matsaloli saboda kananan yaran da suke tare da su, alhali kuma an rushe gidajensu.

A tsawon yakin kisan kiyashin da HKI take yi, matan da su ka yi shahada sun kai 12,000 da 400.

Bugu da kari wasu matan da sun kai 14 sun bace ba a gano su ba, sai kuma wasu matan masu ciki da sun kai 60,000 da suke fuskantar hatsari mai tsanani saboda rashin kula da su, da kuma rusa asibitoti da sojojin HKI su ka yi.

A cikin wani tanti a Khan-Yunus da akwai wata mace mai suna Ummu Muhamad da take rayuwa da ‘ya’yanta 7, bayan da maigidanta ya yi shahada sanadiyyar harin sojojin HKI.

Matar ta bayyana cewa, baya ga mijinta da akwai wani daga cikin ‘ya’yanta da ya yi shahada, kuma su da suke a raye suna da bukatuwa da magungunan da samunsu yake yin wahala saboda halin yaki da ake ciki.

Ta kuma bayyana cewa; Muna fama a yunuwa mai tsanani,babu wanda zai taimake mu, kuma fulawar da ake da ita, ta yin burodi ta kare.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Shirin gwamnatin mamayar Isra’ila shi ne shirin share al’umma Falasdinu daga kan doron kasa

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Shirye-shiryen da gwamnatin ‘yan sahayoniyya take yi na mamaye yankin Zirin Gaza da kuma tilastawa al’ummar yankin gudun hijira wani karin shaida ne na musamman da wannan gwamnatin take da niyyar aikata kisan kiyashi a Falastinu da ta mamaye.

Ismail Baqa’i ya bayyana shirin gwamnatin ‘yan sahayoniyya na mamaye garin Gaza da sojoji da kuma tilastawa mazauna yankin kauracewa gidajensu a matsayin wani shiri na kammala kisan gillar da  take yi wa al’ummar Falastinu, yana mai jaddada tofin Allah tsine da Allah wadai da wannan mummunan cin zarafi.

Baqa’i ya jaddada cewa: Barazanar mamaye daukacin Zirin Gaza daga lalatattun wadanda suka mamayeFalasdinu tsawon lokaci, kuma kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ke bibiyar ayyukansu da kotun kasa da kasa ke bincike a matsayin laifin kisan kiyashi, wani lamari ne da ya kara bayyana a fili kan takamaiman manufar ‘yan sahayoniyya na tsarkake Gaza bisa manufa ta aikata kisan kiyashi kan Falasdinawa a kan tubalin nuna kyamar kabilanci, lamarin da ya zama wajibi kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta yi la’akari da shi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen August 9, 2025 Guterres: Dole Ne Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Gaggauta Janye Shirinta Kan Gaza August 9, 2025 Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza August 9, 2025 Iran Da Iraki Sun Jaddada Goyon Bayan Kungiyoyin ‘Yan Gwagwarmaya August 9, 2025 Kwamitin Sulhu na MDD na Shirin gudanar da zaman gaggawa kan batun Gaza August 9, 2025 Iran da Masar sun jaddada wajabcin daukar matakan kawo karshen kisan kiyashi a Gaza August 9, 2025 Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza August 9, 2025 Hizbullah: Amurka na hakoron taimaka wa ajandar Isra’ila ne a kan Lebanon August 9, 2025 Ramaphosa da Putin sun tattauna rikicin Ukraine da batutuwan da suka shafi kasashensu August 8, 2025 Australia ta gargadi Isra’ila game da yunkurin mamaye Gaza August 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124
  • Falasdinawa 11 Ne Suka Rasa Rayukansu Saboda Yunwa A Gaza
  • Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa
  • Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga