Borrell : Rabin bama-baman da aka jefa a Gaza sun fito ne daga Turai
Published: 11th, May 2025 GMT
Tsohon jami’in harkokin wajen kungiyar tarayyar turai Josep Borrell ya yi kakkausar suka ga kungiyar kan rashin daukar mataki game da kisan kiyashin da gwamnatin Isra’ila ke yi a zirin Gaza yana mai cewa “rabin bama-baman da aka jefa a zirin Gaza ne muke kawowa.”
Da yake jawabi bayan karbar lambar yabo ta Carlos V ta Turai da ke Spain, Josep Borrell ya ce nahiyar Turai na shaida kawar da wata kabila tun bayan karshen yakin duniya na biyu, domin gina wurin yawon bude ido bayan korar da Falasdinawa.
Ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin kisan kiyashi, ya kuma ce kungiyar EU, duk da cewa tana da hanyoyin nunna adawa da kuma kawo karshen ayyukan Isra’ila, amma ba ta sauke nauyin da ke kanta kan wannan batu ba.
Borrell ya ce: “kungiyar Tarayyar Turai ba ta yin abin da za ta iya.
Mista Borrell ya soki Isra’ila da keta dokokin yaki da kuma amfani da yunwa ga farar hular Gaza inda ya kara da cewa: ” bama-baman da aka jefa a Gaza sun ninka na bam din da aka jefa Hiroshima sau uku.”
“Kuma tsawon watanni, babu wani abu da ya shiga Gaza, babu ruwa, ba abinci, ba wutar lantarki, ba man fetur, ba kiwon lafiya.
Borrell ya ce: “Dukkanmu mun san abin da ke faruwa a can, kuma mun sami labarin manufofin da ministocin Netanyahu suka bayyana.
A ranar 18 ga watan Maris ne sojojin Isra’ila suka sake kai hare-hare a zirin Gaza, inda suka kashe dubban Falasdinawa tare da raunata wasu da dama, bayan karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni biyu da kungiyar Hamas da kuma yarjejeniyar musayar fursunonin Isra’ila da Falasdinawa.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza, ta ce akalla Falasdinawa 52,810 aka kashe, akasari mata da yara, yayin da wasu 119,473 suka jikkata tun bayan barkewar mummunan yakin da Isra’ila ta yi da yankin Falasdinu bayan harin ranar 7 ga Oktoba, 2023.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
Sheikh Na’in Kasem shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ya bayyana cewa kungiyar bata bukatar Izini don kare kasar Lebanon daga makiyanta. Yama fadar haka ne ga wanda suka cika kunnen duniya kan cewa dole ne kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim ya nakalto Sheikh Kasim yana fada a wani jawabin da ya gabatar a ranakun Ashoora na Imam Hussain (a) ta kafar Bidiyo. Ya kuma kara da cewa wadanda suke maganar kungiyar Hizbullah ta mika makamanta ga gwamnatinsa kasar, ya fiye masu sauki su fadawa yan mamaya su fice daga kasar Lebanon su kuma dakatar da hare-haren ta’addancin da suke kawo mata.
Ya kara jaddada cewa kungiyarsa zata ci gaba da rike makamanta sannan bata bukatar izini daga wani don kare-kasar Lebanon daga makiyanta.
Malaman ya kara da cewa, wani mai hankali ne zai amince ya mika makamansa a dai dai lokacinda mikiyan kasar Lebanon suna ci gaba da kawo hare-hare kan kasar a ko wace rana. Maimakon su yi allawadai da mai shisgigi sai suka sa idanso a kan makaman hizbulla.
Yace idan wasu a kasar Lebanon sun zami mika kai ga HKI da Amurka to wannan zaminsa ne, amma mu ba masu mika kai ga makiyammu ne ba. Shi’arimmu shi ne {bama daukar kaskanci}.
Ya ce kun yi kuskure da kuka dogara da karfin wasu don takurawa masu gwagwarmaya. Masu gwagwarmaya basa jin tsoron makiya. Ya ce manufarmu ita ce yantar da kasa daga hannun makiya itace manufarmu.
Ya kammala da cewa makiyarmu it ace HKI, dole ne ta fice daga kasar Lebanon, kuma gwagwarmaya ita ce hanya tilo ta korar yan mamaya daga kasarmu. Idan kuma wani yana ganin akwai wata hanya korar makiya daga kasarmu a shirye muke mu shiga tataunawa da shi, ya gamsar damu a kan shirin nasa.