Kamfanin man fetur da gas na kasar Iran zai fara aikin nema da hakar man fetur a tekun Caspian da ke arewacin kasar, wanda mataki ne na ci gaba ga kamfanin musamman a halin da ake ciki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto jami’an kamfanin na cewa tuni sun kai kayakin aiki zuwa wuraren da suke zata akwai danyen man fetur a cikin tekun, sannan a shirye suke su fara aiki don hakar man daga yanzun.

Ba wannan ne karon farko wanda gwamnatin kasar Iran take hakar danyen man fetur a cikin tekun Caspian ba, saboda a shekara ta 1997 ne ta dakatar da hakar mai daga gabar tekun, sannan ta dakatar da hakar man a tsakiyar tekun a shekara ta 2014.

Labarin ya kara da cewa ministan man fetur na kasar ne Mohsen Paknejad ya kaddamar da aikin hakar man a gefen kasuwar baje koli na Gas, tashewa, da sinadaran danyen mai karo 29 da ke gudana a nan tehran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza

Malaman jami’o’i sama da 100 daga Isra’ila sun bayyana cewar jan kafar da ƙasar Jamus ke yi wajen ɗaukar matakin matsin lamba ga gwamnatin Isra’ila na iya bai wa ƙasar damar ci gaba da aikata manyan laifuffuka a Gaza.

Wata wasika da masanan suka rubuta wa ɗaya daga cikin manyan shugabannin jam’iyyar SPD da ke mulki a Jamus, ta ce rashin ɗaukar matakin na iya bada damar gudanar da wasu sabbin laifuffuka a Gaza, tare da watsi da irin tarihin da aka koya a shekarun baya.

A ranar 22 ga watan Yuli, biyu daga cikin jiga jigan kawancen jam’iyyun dake jagorancin Jamus, sun bukaci ƙasar da ta shiga cikin ƙasashen duniya da ke ƙawance domin gaggauta kawo ƙarshen yaƙin Gaza da kuma sanya takunkumi a kan Isra’ila da kuma kin sayar mata da makamai.

Gwamnatin Jamus da ke ƙarƙashin ƙawance jam’iyyun CDU da SCU da kuma SPD ta ƙarfafa sukar da take yiwa gwamnatin Isra’ila a kan yadda take azabtar da mazauna Gaza wajen hana kai musu kayan agaji, amma kuma ya zuwa yanzu bata bayyana ɗaukar wasu matakai masu tsauri ba.

Isra’ilar dai ta yi watsi da duk wani yunkuri na zargin da ake mata na amfani da yunwa wajen azabtar da mutane akalla miliyan biyu dake zama a Gaza, inda ta bayyana cewar ƙungiyar Hamas ce ke sace abincin da ake kai wa mutanen yankin.

Matakan kai hari a kan masu neman kayan agajin da Isra’ila ke yi a kan mazauna Gazar, sun yi sanadiyar hallaka akalla mutane sama da dubu guda.

Kungiyar Hamas ta ƙaddamar da harin da ya hallaka Yahudawa sama da 1,200 a watan Oktobar shekarar 2023, abinda ya sa Isra’ila ƙaddamar da yakin da ya hallaka mutane sama da 50,000 a bangaren Falasdinawa.

Tuni ƙasashen Birtaniya da Canada da kuma Faransa suka bayyana aniyarsu ta amincewa da ƙasar Falasdinu a taron Majalisar Ɗinkin Duniyar da zai gudana a watan Satumba, inda suke cewa ta wannan hanyar ce kawai za a samu zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.

Isra’ila da Amurka sun bayyana matuƙar ɓacin ransu da matakin, yayin da a yau Firaminista Benjamin Netanyahu ke cewa ba zai dakatar da yakin da yake yi ba har sai ya murkushe ƙungiyar Hamas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen
  • Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • An Biya Diyyar Naira Miliyan 277 Ga Wadanda Aikin Ginin Masallacin Gumel Ya Shafa
  • Mutanen Kasar Lebanon Suna Tsoron HKI Zata Shiga Kasar Daga Kasar Siriya
  • Amurka ta Fara Janye Wasu Sojojinta Daga Wurare 3 A Kasashen Iraki Da Siriya
  • An Fara Gudanar Da Juyayin Cikan Shekaru 80 Da Harin Amurka Da Makamin Nukiliya Kan Hiroshima Na Kasar Japan
  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza
  • Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a Sakkwato