Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano
Published: 12th, May 2025 GMT
Jami’ar Maryam Abacha MAAUN ta rufe wasu gidaje biyu da ke zaman ɗakunan kwanan ɗalibanta mata a Jihar Kano.
Hukumar gudanarwar jami’ar ta rufe ɗakunan kwanan ɗaliban da ke unguwar Hotoro da titin UDB a Kano saboda zargin rashin ɗa’a.
Awakin da ke rayuwa sama da shekaru 200 a inda babu ruwa Za mu ci gaba da aikin haƙo ɗanyen mai a Arewa —NNPCLWannan jami’i da ke kula da ɗakunan kwanan, Hamza Garba, ya ce an ɗauki matakin ne a ƙoƙarin da jami’ar take yi na tabbatar da aminci da tsaro da kuma daƙile duk wata kafa ta aikata masha’a a tsakanin ɗalibai.
Jami’ar ta ce cikin dalilan da ta ɗauki wannan mataki akwai ayyuka na rashin ɗa’a, ƙarancin ruwa da wutar lantarki, tashin-tashina da kuma tsugunar da waɗanda ba su cancanta ba a gidajen.
Sanarwar ta buƙaci ɗaliban da ke zama a gidajen biyu da su tattara komatsai da zarar sun kammala jarrabawar zangon farko.
Kazalika, sanarwar ta yi kira ga iyayen ɗaliban da cewa kada su zargi jami’ar kan duk abin da ya faru da ’ya’yansu da suka bijirewa wannan umarni.
Aminiya ta ruwaito cewa tun a shekarar 2022 ce jami’ar ta Maryam Abacha ta samu lasisin soma gudanar da harkokin karatu amma har kawo yanzu ba ta tanadi ɗakunan kwanan ɗalibai a cikinta ba.
Sai dai jami’ar ta ƙulla yarjejeniya a hukumance da wasu masu gidaje da ke bayar da haya domin tsungunar da ɗalibanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗakunan Kwana Ɗalibai Jihar Kano ɗakunan kwanan
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta gano harsasai 210 da aka jefar a kan babbar hanyar Zariya zuwa Funtuwa, a unguwar Dogo Itace da ke Samaru, Zariya.
Lamarin ya faru ne lokacin da DPO na Samaru tare da tawagarsa suke sintiri a kan hanyar.
Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-BissauJama’ar yankin ne suka kira rundunar cewar fasinjojin wata mota ƙirar Volkswagen Golf mai launin baƙi sun jefar da wata jaka, sannan suka tsere.
Da jami’an rundunar suka isa, sun tarar da jakar da aka jefar.
Bayan gudanar da bincike, sun gano harsasai 210 na ɗangon 7.56mm.
DPO ɗin yankin ya sanar da sauran jami’an rundunar da ke kan hanyar Funtuwa domin dakatar da motar amma ba a ga motar ba.
Ana zargin direban da fasinjojin motar sun lura da jami’an tsaron da ke kan hanyar, wanda hakan ya sa suka zubar da jakar.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yi kira ga jama’a da ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai.
Ya jaddada ƙudirin rundunar na ci gaba da sintiri da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.
Ya kuma gargaɗi masu aikata laifi da su guji duk wani yunƙurin tayar da zaune-tsaye, inda ya ce duk wanda aka kama zai fuskanci hukunci mai tsanani.