Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano
Published: 12th, May 2025 GMT
Jami’ar Maryam Abacha MAAUN ta rufe wasu gidaje biyu da ke zaman ɗakunan kwanan ɗalibanta mata a Jihar Kano.
Hukumar gudanarwar jami’ar ta rufe ɗakunan kwanan ɗaliban da ke unguwar Hotoro da titin UDB a Kano saboda zargin rashin ɗa’a.
Awakin da ke rayuwa sama da shekaru 200 a inda babu ruwa Za mu ci gaba da aikin haƙo ɗanyen mai a Arewa —NNPCLWannan jami’i da ke kula da ɗakunan kwanan, Hamza Garba, ya ce an ɗauki matakin ne a ƙoƙarin da jami’ar take yi na tabbatar da aminci da tsaro da kuma daƙile duk wata kafa ta aikata masha’a a tsakanin ɗalibai.
Jami’ar ta ce cikin dalilan da ta ɗauki wannan mataki akwai ayyuka na rashin ɗa’a, ƙarancin ruwa da wutar lantarki, tashin-tashina da kuma tsugunar da waɗanda ba su cancanta ba a gidajen.
Sanarwar ta buƙaci ɗaliban da ke zama a gidajen biyu da su tattara komatsai da zarar sun kammala jarrabawar zangon farko.
Kazalika, sanarwar ta yi kira ga iyayen ɗaliban da cewa kada su zargi jami’ar kan duk abin da ya faru da ’ya’yansu da suka bijirewa wannan umarni.
Aminiya ta ruwaito cewa tun a shekarar 2022 ce jami’ar ta Maryam Abacha ta samu lasisin soma gudanar da harkokin karatu amma har kawo yanzu ba ta tanadi ɗakunan kwanan ɗalibai a cikinta ba.
Sai dai jami’ar ta ƙulla yarjejeniya a hukumance da wasu masu gidaje da ke bayar da haya domin tsungunar da ɗalibanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗakunan Kwana Ɗalibai Jihar Kano ɗakunan kwanan
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa
Ɗan Majalisar Wakilai, Honorabul Yusuf Gadgi, ya yi iƙirarin cewa mayaƙan Boko Haram sun ƙwace makaman sojoji da kuɗaɗensu ya kai tiriliyoyin naira a hare-haren da kungiyar ta kai kan sansanonin soji a yankin Arewa maso Gabas.
Gadgi ya bayyana haka ne a yayin da yake tsokaci kan ƙudirin da Honorabul Ahmed Satomi daga Jihar Borno ya gabatar a zauren Majalisar, kan gobarar da ta tashi a ma’ajiyar makamai ta rundunar soji da ke Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri da kuma ƙaruwar hare-haren Boko Haram a jihohin Borno da Yobe a baya-bayan nan.
Ɗan malisar ya ce yawan yadda ’yan ta’adda ke lalata kayan yaƙin sojoji a yanzu, ba a taɓa ganin irinsa ba a baya. Ya ƙara da cewa rashin ɗaukar mataki cikin gaggawa zai haifar da mummunan sakamako musamman ga zaɓaɓɓun shugabanni.
Ya ce, “Na firgita da abin da Boko Haram ta yi a Barikin Giwa da sauran cibiyoyin sojoji. Akwai abin damuwa game da tsaro da amincin ’yan Najeriya da ma ita kanta ƙasar.”
Yusuf Gadgi ya ce Majalisa ta ware wa sojoji kuɗaɗe a cikin kasafi domin sayen motocin yaƙi sama da 40 da sauran kayan yaƙi, da kuɗinsu ya kai tiriliyoyin naira, domin tsaron ’yan Najeriya.
Ya ce. “To yaya za mu samu tabbacin tsaron al’umma a irin wannan yanayi, idan ’yan ta’dda sun kwace waɗannan kayan yaƙi?”
Ya ci gaba da cewa “Majalisa tana yin iya bakin ƙoƙarinta wajen yin magana da kan sha’anin tsaro, amma wajibi ne hukumomin gwamnati su ɗauki mataka. Ya zama tilas shugaban ƙasa ya binciki shuagabannin sojoji da sauran hukumomin tsaro game da wannan sakacin, sannan ya ɗauki mataki a kansu.
“Sannan ya zama dole mu gayyaci hukumomin gwamnati domin su rika bayani a game da gazawarsu wajen gudanar da ayyukansu,” in Honorabul Yusuf Gadgi.
Ya bayyana cewa yawan halin ko-in-kula daga gwamnati da hukumomin tsaro zai haifar da rashin yardar al’umma da su, wanda hakan babbar barazana ce ga shugabannin siyasa.
Ya ce ya zama wajibi a ɗauki mataki, idan ba haka ba, “’yan Najeriya za su ɗauki matakan kare kansu da kansu, kuma za su yake mu kamar yadda za su yakar Boko Haram.”