Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan
Published: 11th, May 2025 GMT
Uwargidan tsohon Shugaban Najeriya Dame Patience Jonathan, ta bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu za ta marawa baya a Zaɓen 2027.
Patience ta nanata cewa ba ta da burin komawa fadar shugaban ƙasa, amma ta ce a shirye take ta taimakawa uwargidan shugaban ƙasa na yanzu, Sanata Oluremi Tinubu wajen yaƙin zaɓen 2027.
Aminiya ta ruwaito Patience na bayyana haka ne a lokacin da take kiran sunan manyan baƙi ciki har da ’yar shugaban ƙasar, Folashade Tinubu-Ojo a wajen taron da aka karrama ta a matsayin jagora ta gari, wanda kamfanin Accolade Dynamics Limited ya shirya ranar Asabar a Abuja.
Ta ce, “ita ya kamata in fara kira amma sai na bari zuwa ƙarshe wato ’yar shugaban ƙasarmu wanda muka aminta da shi wato Shugaba Bola Tinubu.
“Iyajola ina miki godiya bisa yadda kike ƙarfafa gwiwar mata. Muna tare da ke a wannan aikin kuma za mu mara miki baya.
“Ina da yawan magana, idan ba na son abu ana ganewa, amma idan ina tare da abu, zan iya mutuwa a kansa.
“Kowa da lokacinsa a mulki, kuma idan lokacin mutum ne, ina goya masa baya ne.”
Ta ƙara da cewa a lokacin da suke mulki, Uwargidan shugaban ƙasa Oluremi Tinubu ta goya mata baya.
“Ina da hankali, don haka dole ne in mayar da biki. Na faɗa mata cewa zan taya ta yaƙin zaɓe, ba zan juya mata baya ba. Ni ba na sha’awar komawa fadar shugaban.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi Hizbullah ta mika makamanta a cikin wannan lokacin da yaki bai kare ba, kuma HKI tana cigaba da keta tsagaita wutar yaki.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya bayyana masu tunani irin wannan da rashin Sanya hankali a cikinsa.
A jawabinsa na dararen Muharram a jiya Asabar, babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Nauyi ne da ya rataya a wuya gwamantin kasar ta takawa HKI birki akan keta tsagaita da take yi wanda take kai wa fararen hula hare-hare.”
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Babu yadda za a yi Hizbullah ta ci gaba da Sanya idanu ba tare da iyaka ba, domin mu Mabiya Imam Hussain ( a.s) kuma a kodayaushe muna bayar da taken da yake cewa; Ba Za Mu Yarda Da Kaskanci Ba.”
Har ila yau, Sheikh Na’im ya kuma ce; Duk wadanda suke cewa ana bai wa HKI uzurin ta kawo hari, su daina, domin ba ta da bukatuwa da wani uzuri da za ta fake da shi, abinda yake farwua a Falasdinu da Syria shi ne babban dalili akan hakan.:
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Isra’ila tana neman mai Rauni ne ta afka masa, wannan kuwa shi ne abinda ba zai faru da mu ba, domin mun sami tarbiyya ne ta rashin amincewa da kaskanci.
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Muna da karfin bugawa da Isra’ila, idan har ya zamana shi kadai ne zabinmu, kuma za mu yi nasara domin mun dogara ne da Allah.