HausaTv:
2025-05-22@06:06:00 GMT

Ambaliyar Ruwan Sama Ya Ci Mutane Fiye Da 48,0000 A Somaliya

Published: 14th, May 2025 GMT

Rahoton MDD ya sanar da cewa, fiye da mutane 48,000 ne, ambaliyar ruwan saman da aka yi a Somaliya ya yi wa illa, yayin da wasu da adadinsu ya kai 17 su ka rasa rayukansu.

Hukumar MDD mai kula da ayyukan jin kai da cewa ( OCHA) ce ta sanar da hakan,tana mai kara da cewa da akwai yiyuwar a kara samun saukar mamakon ruwa sama a tsakiyar kasar, nan da wasu kwanaki masu zuwa.

Wannan ambaliyar dai wacce ta shammaci mutanen kasar, a lokacin da kungiyar agajin kasar ta sanar da cewa, tana da karancin kayan da ake da bukatuwa da su domin kai daukin gaggawa idan hakan ta faru.

Kasar Somaliya ta fuskanci ambaliyar ruwa mai tsanani a 2023 wanda ya yi sanadiyyar  mutuwar mutane fiye da 100, da kuma tilastawa mutane fiye da miliyan 1 yin hijira.

Sauyin yanayi yana daga cikin muhimman dalilan faruwar ambaliyar ruwa irin wannan.

Yankin zirin Afirka da gabashinta, suna cikin wuraren da sauyin yanayi yake haddasa kamfar ruwa a baya da kuma fari,da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar dabbobi masu yawa. Hakan nan kuma ya tilastawa mutanen yankin barin matsugunansu zuwa sansanonin ‘yan hijira domin samun abinda za su ci.

 

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ambaliyar ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge

Jami’an Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Nasarawa (SCID) sun kama wani mai garkuwa da mutane a Kasuwar Shinge da ke Lafia, bisa rahotonnin sirri da suka samu.

An samu nasarar cafke wanda ake zargin bayan shafe dogon lokaci  rundunar na nemasa ruwa a jallo saboda laifuka da dama da suka hada da garkuwa da mutane da kuma satar shanu.

A yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, sannan ya jagoranci jami’an tsaro zuwa maboyarsa da ke kauyen Ruwan Baka a karamar hukumar Doma, inda aka samu bindiga kirar AK-49 mai lamba 453144 tare da alburusai.

Wannan nasarar ta biyo bayan kama wata Fatima Salisu a ‘yan kwanakin baya, wadda aka tare tana jigilar makamai daga Doma zuwa Jihar Katsina domin kaiwa miyagu.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa, CP Shattima Jauro Mohammed, ya jaddada kudirin rundunar na ci gaba da yaki da aikata laifuka tare da tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar Nasarawa.

Ya bukaci jama’a da su kasance masu lura, tare da bayar da rahoton duk wani motsi ko aikin da ba su yarda da shi ba, domin ‘yan sanda za su ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiyar  al’umma.

Aliyu Muraki

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa Babu Wata Kyakkyawar Fata A Tattaunawar Iran Da Amurka
  • Falasdinawa 94 sun yi shahada a Hare-haren Isra’ila a rana guda
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
  • Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi