Aminiya:
2025-11-27@21:57:38 GMT

Majalisar Dattawa ta buƙaci a tura ƙarin sojoji zuwa Borno da Yobe

Published: 14th, May 2025 GMT

Majalisar Dattawa ta buƙaci rundunar sojin Nijeriya ta tura ƙarin sojoji da manyan makaman yaƙi zuwa jihohin Borno da Yobe, bayan farfaɗowar hare-haren ‘yan ta’adda na Boko Haram a jihohin.

Ƙudurin ya biyo bayan ƙarin hare-haren ‘yan ta’addan ne a arewa maso gabashin ƙasar, ciki har da kashe kimanin sojoji goma a garin Marte da ke ƙaramar hukumar Monguno ranar Litinin, 12 ga watan Mayu, da kuma wani harin da suka kai Gajiram na Ƙaramar Hukumar Nganzai, da sanyin safiyar ranar Talata.

Zaɓen 1993: IBB ya wallafa ba daidai ba a littafinsa — Sule Lamiɗo Trump ya janye takunkumin da Amurka ta ƙaƙaba wa Syria

A wani ƙuduri da mai tsawatarwa majalisar, Sanata Tahir Munguno, ya gabatar a ranar Talata, ‘yan majalisar sun ce duk da cewa a baya kashi biyu cikin uku na ƙananan hukumomin Jihar Borno sun kasance ƙarƙashin ikon ‘yan Boko Haram — haɗin kai tsakanin sojoji da ‘yan sa-kai ya taimaka wajen ƙwato ƙananan hukumomin.

Amman zaman lafiyan da aka samu, ya sa hedikwatar yaƙi da ta’addancin ta koma Arewa maso yammacin ƙasar, inda sojin ƙasar ke yaƙi da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

Yayin da yake nuna damuwa game da yadda ‘yan ta’addan ke sauya dabarun yaƙin su, Monguno ya bayyana yadda ƙungiyar ke amfani da na’urorin zamani ciki har da jirage marasa matuƙa da kuma ƙarin amfani da abubuwan fashewa da suka ƙera da kansu, lamarin da ya janyo mace-macen fararen hula da sojoji da kuma katse harkokin sufuri.

Majalisar Dattawan, ta yi kira ga shugabannin sojin ƙasar su tura isassun sojoji zuwa arewa maso gabashin ƙasar su kuma tabbatar da cewa an ba su na’urorin zamani domin su daƙile sabuwar barazanar.

Kazalika, majalisar ta nemi kwamitinta kan sojin ƙasa da na sama ya sa ido tare da tabbatar da cewa sojojin sun bi umarnin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Jihar Yobe Majalisar Dattawa Makaman Yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa

’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa