Majalisar Dattawa ta buƙaci a tura ƙarin sojoji zuwa Borno da Yobe
Published: 14th, May 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta buƙaci rundunar sojin Nijeriya ta tura ƙarin sojoji da manyan makaman yaƙi zuwa jihohin Borno da Yobe, bayan farfaɗowar hare-haren ‘yan ta’adda na Boko Haram a jihohin.
Ƙudurin ya biyo bayan ƙarin hare-haren ‘yan ta’addan ne a arewa maso gabashin ƙasar, ciki har da kashe kimanin sojoji goma a garin Marte da ke ƙaramar hukumar Monguno ranar Litinin, 12 ga watan Mayu, da kuma wani harin da suka kai Gajiram na Ƙaramar Hukumar Nganzai, da sanyin safiyar ranar Talata.
A wani ƙuduri da mai tsawatarwa majalisar, Sanata Tahir Munguno, ya gabatar a ranar Talata, ‘yan majalisar sun ce duk da cewa a baya kashi biyu cikin uku na ƙananan hukumomin Jihar Borno sun kasance ƙarƙashin ikon ‘yan Boko Haram — haɗin kai tsakanin sojoji da ‘yan sa-kai ya taimaka wajen ƙwato ƙananan hukumomin.
Amman zaman lafiyan da aka samu, ya sa hedikwatar yaƙi da ta’addancin ta koma Arewa maso yammacin ƙasar, inda sojin ƙasar ke yaƙi da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.
Yayin da yake nuna damuwa game da yadda ‘yan ta’addan ke sauya dabarun yaƙin su, Monguno ya bayyana yadda ƙungiyar ke amfani da na’urorin zamani ciki har da jirage marasa matuƙa da kuma ƙarin amfani da abubuwan fashewa da suka ƙera da kansu, lamarin da ya janyo mace-macen fararen hula da sojoji da kuma katse harkokin sufuri.
Majalisar Dattawan, ta yi kira ga shugabannin sojin ƙasar su tura isassun sojoji zuwa arewa maso gabashin ƙasar su kuma tabbatar da cewa an ba su na’urorin zamani domin su daƙile sabuwar barazanar.
Kazalika, majalisar ta nemi kwamitinta kan sojin ƙasa da na sama ya sa ido tare da tabbatar da cewa sojojin sun bi umarnin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Jihar Yobe Majalisar Dattawa Makaman Yaƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
Majiyoyi sun kuma ce “an kashe adadi mai yawa na ‘yan bindigar”.
Shugaban karamar hukumar, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya ce harin ya kara firgitar da manoman yankin.
Ya ce taimakon gaggawa daga barikin soji na Kontagora ya tilastawa ‘yan bindigar tserewa zuwa dazuka.
Ya kuma ce ‘yan bindigar sun yi awon gaba da shanu, sun farfasa shaguna tare da kwashe kayan abinci da kayayyaki masu daraja a shagunan mutanen yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp