Majalisar Dattawa ta buƙaci a tura ƙarin sojoji zuwa Borno da Yobe
Published: 14th, May 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta buƙaci rundunar sojin Nijeriya ta tura ƙarin sojoji da manyan makaman yaƙi zuwa jihohin Borno da Yobe, bayan farfaɗowar hare-haren ‘yan ta’adda na Boko Haram a jihohin.
Ƙudurin ya biyo bayan ƙarin hare-haren ‘yan ta’addan ne a arewa maso gabashin ƙasar, ciki har da kashe kimanin sojoji goma a garin Marte da ke ƙaramar hukumar Monguno ranar Litinin, 12 ga watan Mayu, da kuma wani harin da suka kai Gajiram na Ƙaramar Hukumar Nganzai, da sanyin safiyar ranar Talata.
A wani ƙuduri da mai tsawatarwa majalisar, Sanata Tahir Munguno, ya gabatar a ranar Talata, ‘yan majalisar sun ce duk da cewa a baya kashi biyu cikin uku na ƙananan hukumomin Jihar Borno sun kasance ƙarƙashin ikon ‘yan Boko Haram — haɗin kai tsakanin sojoji da ‘yan sa-kai ya taimaka wajen ƙwato ƙananan hukumomin.
Amman zaman lafiyan da aka samu, ya sa hedikwatar yaƙi da ta’addancin ta koma Arewa maso yammacin ƙasar, inda sojin ƙasar ke yaƙi da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.
Yayin da yake nuna damuwa game da yadda ‘yan ta’addan ke sauya dabarun yaƙin su, Monguno ya bayyana yadda ƙungiyar ke amfani da na’urorin zamani ciki har da jirage marasa matuƙa da kuma ƙarin amfani da abubuwan fashewa da suka ƙera da kansu, lamarin da ya janyo mace-macen fararen hula da sojoji da kuma katse harkokin sufuri.
Majalisar Dattawan, ta yi kira ga shugabannin sojin ƙasar su tura isassun sojoji zuwa arewa maso gabashin ƙasar su kuma tabbatar da cewa an ba su na’urorin zamani domin su daƙile sabuwar barazanar.
Kazalika, majalisar ta nemi kwamitinta kan sojin ƙasa da na sama ya sa ido tare da tabbatar da cewa sojojin sun bi umarnin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Jihar Yobe Majalisar Dattawa Makaman Yaƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri na kashe jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ba zai rura wutar rikicin da ake yi yanzu ba, hasali zai ma kawo ƙarshen rikicin ne.
A wata hira ta tsawon minti 20 da tashar talabijin ta ABC ta Amurka ta yi da shi, Netanyahu ya kare matakin farmakin da ƙasarsa ta kai wa Iran, inda ya kwatanta jagoran addini Khamenei a matsayin wani sabon Hitler na wannan zamani.
Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan sisaya ta satar kuɗi — EFCC Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a BenuweA yayin hirar, duk wata tambaya da aka yi masa game da ko Shugaban Amurka Donald Trump ya sahale wa Isra’ila kan shirin kashe babban jagoran addinin, Netanyahu ya ki kawar da yuwuwar hakan.
Da aka matsa shi a kan ko za su hari jagoran, sai ya ce : “Muna yin abin da muke da bukatar yi.”
“Mun hari manyan masana nukiliyarsu, sannan har yanzu muna da sauran aikin da za mu yi a daya bangaren.”
Netanyahu ya nuna cewa sun kai wa Iran hari ne domin kare al’umma, domin kare duk wata barazanar nukiliya daga Iran.
Firaministan a hirarrakin da ya yi da kafofin yada labaran Amurka a kwanakin nan, ya bayyana rikicin Isra’ila da Iran a matsayin “yakin wayewa da dabbanci.”
Ya ce akwai bukatar Amurkawa su damu matuka game da kokarin da Tehran ke yi na mallakar makamin nukiliya da karfinta na makami mai linzami.
“Idan yau birnin Tel Aviv ne, gobe kuma New York ne,” kamar yadda Netanyahu ya shaida wa wakilin ABC, Jon Karl.
AFP